Sashe 109
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ina ruwan auntyn yara, ai banga laifinta ba nikam, tama d'an jure data iya saurararku, don da nice wlh bori zan azawa, dady ai ko abbaty bazan yarda yaje waje karatuba wlh balle ita da take ganin sanadiyar hakan mahaifin little yabarsu gaba d'aya."
"Da gaskiyarki kema my dota, ALLAH dai yaraya manasu kuma yanuna mana shima mahaifin nasa yadawo, wannan abun da yafaru yana d'aya daga cikin rashin amfanin fita wajen karatu, kawai bama ganewa ne, Amma babu abunda zakaje can qasarsu ka karanto da bazaka iya karantarsa anan qasarka ba, ko tsabar son kai irin nasu nasa suriqe mutum acan saboda basa son cigaban tamu qasar." dady yafad'a cike da takaicin abun.
Ita dai umma tunda taji an d'auko zancen mahaifin little batace komai ba saima komawarta gefe da tayi ta zauna tana kallon samarin dake har had'a kujerun da akayi walima dasu wasu kuma na warware rumfar da aka kakkafa, gaba d'aya bata son jin zancen Dr ko kad'an saboda duk daren ALLAH sai tayi kukan halin da 'yar tata keciki, wanda badon haka ba da yanzu itama ta tara nata zuri'a a gabanta kamar yanda su Fatima da Dr keda su, don yanzu 'ya'yansu bakwai aduniya, bayan haihuwar abbaty, shahid da shahida, walida, sultan da kuma jidda fatima ta sake haihuwar zainab wanda yanzu tanada shekaru goma aduniya saboda haihuwarsu da takeyi kusa kusa daga ita kuma bata sake haihuwa ba.
Ganin haka yasa little yaje inda take ya zauna tare dasa hannuwansa ya tallafe fuskarta yana kallonta, d'an harararsa tayi takai masa ranqwashi akai had'e da cewa.
"Lafiya?" Saida ya d'an sosa wajen yayiwa fuskarsa kamar zaiyi kuka sannan yace.
"Da zafi umma."
"Ai Kai kajawa kanka, meyakawo nan!"
"Haquri nazo nabaki, Naga kamar kinajin haushin mahaifina ne har yanzu?"
Jin tayi jikinta yayi sanyi saboda yanayin yanda yayi maganar sai taji yamatuqar bata tausayi, hannunta ta d'ora akan nasa tana d'an mummurzawa a hankali alamun ban haquri sannan tace.
"Kayi haquri amma Ina matuqar jin haushin mahaifinka saboda yanda yasa mahaifiyarka ta b'ata duka qurciyarta akansa, dole naji ba dad'i ko kad'anne domin bana son ace yanda take 'yah tilo awajena itama yazamana taqare rayuwarta kai kad'ai awajenta, duk da wannan hurumine na ALLAH amma ina fatar ace ita tatara zuri'a fiye dani."
Sosai little yafahimci pain d'in da takeji a matsayinta na uwa, don haka sai yayita fad'a mata kalamai masu matuqar sanyi da kuma dad'i da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga tasaki takoma daidai yanda take d'azu sannan yabarta da yake su dady najiranta suka wuce gida.
Bayan anyi sallar la'asar little ya iske mahaifiyarsa cikin shirinsa na manyan kaya yayi matuqar kyau har yagaji, murmushi tayi data kallesa tare dayin hamdala tana Mai godewa ALLAH acikin zuciyarta da yayi mata ni'imar samunsa a matsayin d'ah, murmushi ya sakar mata ganin rin kallon da takeyi masa itama tana murmushi yace.
"Gwaggona barka da marece, anwuni lafiya?"
"Yawwa little, lafiya klw, wannan irin gayu kuma sai Ina?"
Saida ya sosa kansa sannan yayi qasa dashi had'e da cewa.
"Kano zanje in Sha ALLAH."
"Tohh!..injin dai lafiya?, Ina yau d'in nan da safe kadawo?, to kuma me zakaje yowa a can yanzu?"
Shiru yayi batare daya bata amsa ba yanaci gaba da sosa kansa har lokacin kan nasa na aqasa tayi murmushi don tafahimci inda zancen yanufa!.
"Au shiyasa tun dawuri kaje ka kai qarata gunsu dady akayi mani shigo shigo ba zurfi?"
Dariya yayi tare da d'ago kansa yace, "haba dai mamana!, ALLAH yatsareni da son duk wani abu da zaisa har inkai qararki ko awurin waye kuwa, shi dady kawai alqawari yayimun shiyasa yayi hakan, ni kuma bisa umurninki nayi mata alqawarin bazan sake waiwayarta ba har sai ranar dana cika maki burinki, shiyasa yau dana tabbatar da hakan nake qoqarin itama naje nacika mata alqawarinta."
"To kayi haquri ranka yadad'e har zuwa gobe tukuna kaga yanzu marece yayi, yaushe har ka isa kuma har kace kaje zakaje wajenta, ai kamata yayi ace yau kafin kazo kafara zuwa saboda kada jewad'in yayi yawa."
Zaunawa yayi ya tanqwashe qafafuwansa agabanta kamar mai shirin d'aukar karatu sannan yace.
"Duk duniya Babu wanda yakamata yafara sanin nasarar dana samu inba keba hakan yasa nafara zuwa agareki domin neman sa albarkarki da kuma addu'o'inki kafin naje wajenta, idan hankalinki yafi kwanciya dana bari sai gobe zanyi hakan don faranta maki koda kuwa zuciyata bata so."
"Eh bawai nafi son hakan bane, kakirata kaji idan tayarda kabari sai goben shikenan don kada ta d'aukeka cikin masu karya alqawari."
Murmushi yayi had'e da cewa.
"Dame zan kirata gwaggo bayan tunda muka rabu da ita bamu koma waya ba balle muhad'u da ita, asalima har nasoma mantawa da muryarta saboda nadad'e banji ba, wataqil itama ta canza lambar waya tunda jiya ba yau ba."
Riqe kunnensa tayi had'e da cewa.
"Da kuwa kazamo gajiyayye a fannin soyayya domin komai dad'ewar masoya basu had'uba idan da halacci bazasu manta muryar juna ba matuqar akwai amana a tsakani."
"Kiyi haquri mamana da abunda zance, kenan hakan na nufin har yanzu kema baki manta da muryar abbana ba?."
Jikinta a sanyaye tasaki kunnensa da take riqe dashi fuskarta na mai sauyawa daga yanayin farinciki da take izuwa damuwa, da sauri yayi nail down had'e da cewa.
"Kiyafemun idan fad'ar hakan ya b'ata maki rai, akoda yaushe Ina mai qoqarin nesanta kaina da duk wata kalma data shafi mahaifina saboda nafaranta maki kamar yanda kike buqata amma hakan ba yana nufin na manta dashi bane a matsayinsa na uba awurina, kiyi haquri bana gaji bane da bin umurninki kawai yau natsinci kaina da fad'ar hakanne sanadiyar abunda kika fad'a, don ALLAH kada kiyi fushi dani akan haka"
Ganin yanda yadamu yasa tad'an saki fuskarta tare da d'aga hannu kamar zata maresa sannan ta ajiye tana fad'in.
"Bakayi laifi ba amatsayinka nad'a don ka ambaci mahaifinka, nakan ji ba dad'i kawaine aduk lokacin da aka tuna mani dashi, amma taya kake tunanin zan manta da muryarsa bayan a kullum inajin muryarka?, Hakan zai kasancene kawai idan rouhina yarabu da gangar jikina, tashi katafi, ALLAH yasa kaci galaba a soyayyarka kuma yabaka ikon shiga gaban duk wani Abu da zai shiga tsakaninka da ita, ya hanaka zubar da qwalla acikin soyayyarka kamar yanda nayi."
"Amin ya rabbi gwaggo, Amma nafasa tafiyar sai gobe in Sha ALLAH, bazan iya tafiya nabarki da b'acin ran da nine silar sakaki acikinsa ba koda da qwarar zarra ne."
Wani farinciki taji ya dirar mata azuciya saboda jin kalamansa, tabbas tasan yana iya qoqarinsa wajen faranta mata, don haka itama dole taso duk abunda zai faranta masa, ko kad'an bata tab'a sa tsammanin biyayyarsa tayi girman da zai datse duk wata alaqa da abunda yake matuqar so ba musamman waya da baza'a iya yiwa kowane mutum shamaki akanta ba, murmushin daya fassara masa irin farincikin dake zuciyarta ta sakar masa had'e da cewa.
"Tashi kaje marece nayi Abu sumayya, ALLAH ya tsare hanya, kuma kagaishemun da ita sosai kaji ko.?"
Cikin qwarin guiwa yamiqe yanajin farinciki shima aransa tare da yimata sallama sannan yabar d'akin, part d'in Fatima yanufa itama yayi mata sallama had'e da kama hanya yana mai fatar samun masoyansa cikin qoshin lafiya.
Bashi ya isa kano ba sai zuwa qarfe takwas da rabi na dare, kai tsaye ya nufi anguwar su batool batare daya biya ko Ina ba don ko baba balarabe da baffa bai sanar dasu zancen zuwansa ba saida ya iso sunata mamakin abunda ya dawo dashi bayan sunsan yau yakoma,
A anguwar sharad'a phase 1 little yasa Mai mashin d'in daya d'aukosa ya ajiyesa kamar yanda batool ta tab'a fad'a masa.
Bayan ya sallami mai mashin d'in yanufi qofar wani gida daya hango mai gadin gidan awaje shida wani mutum saman kujeru, hannu yamiqa masu duk suka gaisa sannan yashiga tambayarsu don ALLAH a ina ne gidan Alhaji umar fari,
Tasowa d'aya daga cikinsu yayi ya d'an matso kusa dashi tare da nuna masa wani gida can gaba kad'an da yatsa yana fad'in.
"Kaga wacan gidan mai gate kalar ruwan qwai?, to ka matsa gaba canne gidansa?"
"Alhaji umar fari nake tambayarka fa?"
"Eh! Kaje mana canne gidan, halan kai baqone agarin?"
"A'a! kawai dai bansan gidan bane."
Little yabashi amsa had'e da miqa masa hannu yayi masa godiya sosai sannan yawuce.
Bakin gate ya tsaya lokacin daya isa qidan yana qarewa girmansa da had'uwarsa kallo, gabansa ne ya soma fad'uwa da sauri ya dafe qirjinsa tare da isa jikin gate d'in ya d'an qwanqwasa mai gadin ya leqo had'e da cewa.
"Waye?"
"Amm..nine?"
"Kaine wa?"
"Baqon batool ne."
Bud'e masa yayi tare da cewa ya shigo, bayan yashiga ciki maigidan yadinga qare masa kallo tun daga sama har qasa sannan yace.
"Jira, Bari afad'o mata."
A daidai bakin qofar shiga falon part d'insu batool ya tsaya tare dayin sallama,
"Da gaskiyarki kema my dota, ALLAH dai yaraya manasu kuma yanuna mana shima mahaifin nasa yadawo, wannan abun da yafaru yana d'aya daga cikin rashin amfanin fita wajen karatu, kawai bama ganewa ne, Amma babu abunda zakaje can qasarsu ka karanto da bazaka iya karantarsa anan qasarka ba, ko tsabar son kai irin nasu nasa suriqe mutum acan saboda basa son cigaban tamu qasar." dady yafad'a cike da takaicin abun.
Ita dai umma tunda taji an d'auko zancen mahaifin little batace komai ba saima komawarta gefe da tayi ta zauna tana kallon samarin dake har had'a kujerun da akayi walima dasu wasu kuma na warware rumfar da aka kakkafa, gaba d'aya bata son jin zancen Dr ko kad'an saboda duk daren ALLAH sai tayi kukan halin da 'yar tata keciki, wanda badon haka ba da yanzu itama ta tara nata zuri'a a gabanta kamar yanda su Fatima da Dr keda su, don yanzu 'ya'yansu bakwai aduniya, bayan haihuwar abbaty, shahid da shahida, walida, sultan da kuma jidda fatima ta sake haihuwar zainab wanda yanzu tanada shekaru goma aduniya saboda haihuwarsu da takeyi kusa kusa daga ita kuma bata sake haihuwa ba.
Ganin haka yasa little yaje inda take ya zauna tare dasa hannuwansa ya tallafe fuskarta yana kallonta, d'an harararsa tayi takai masa ranqwashi akai had'e da cewa.
"Lafiya?" Saida ya d'an sosa wajen yayiwa fuskarsa kamar zaiyi kuka sannan yace.
"Da zafi umma."
"Ai Kai kajawa kanka, meyakawo nan!"
"Haquri nazo nabaki, Naga kamar kinajin haushin mahaifina ne har yanzu?"
Jin tayi jikinta yayi sanyi saboda yanayin yanda yayi maganar sai taji yamatuqar bata tausayi, hannunta ta d'ora akan nasa tana d'an mummurzawa a hankali alamun ban haquri sannan tace.
"Kayi haquri amma Ina matuqar jin haushin mahaifinka saboda yanda yasa mahaifiyarka ta b'ata duka qurciyarta akansa, dole naji ba dad'i ko kad'anne domin bana son ace yanda take 'yah tilo awajena itama yazamana taqare rayuwarta kai kad'ai awajenta, duk da wannan hurumine na ALLAH amma ina fatar ace ita tatara zuri'a fiye dani."
Sosai little yafahimci pain d'in da takeji a matsayinta na uwa, don haka sai yayita fad'a mata kalamai masu matuqar sanyi da kuma dad'i da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga tasaki takoma daidai yanda take d'azu sannan yabarta da yake su dady najiranta suka wuce gida.
Bayan anyi sallar la'asar little ya iske mahaifiyarsa cikin shirinsa na manyan kaya yayi matuqar kyau har yagaji, murmushi tayi data kallesa tare dayin hamdala tana Mai godewa ALLAH acikin zuciyarta da yayi mata ni'imar samunsa a matsayin d'ah, murmushi ya sakar mata ganin rin kallon da takeyi masa itama tana murmushi yace.
"Gwaggona barka da marece, anwuni lafiya?"
"Yawwa little, lafiya klw, wannan irin gayu kuma sai Ina?"
Saida ya sosa kansa sannan yayi qasa dashi had'e da cewa.
"Kano zanje in Sha ALLAH."
"Tohh!..injin dai lafiya?, Ina yau d'in nan da safe kadawo?, to kuma me zakaje yowa a can yanzu?"
Shiru yayi batare daya bata amsa ba yanaci gaba da sosa kansa har lokacin kan nasa na aqasa tayi murmushi don tafahimci inda zancen yanufa!.
"Au shiyasa tun dawuri kaje ka kai qarata gunsu dady akayi mani shigo shigo ba zurfi?"
Dariya yayi tare da d'ago kansa yace, "haba dai mamana!, ALLAH yatsareni da son duk wani abu da zaisa har inkai qararki ko awurin waye kuwa, shi dady kawai alqawari yayimun shiyasa yayi hakan, ni kuma bisa umurninki nayi mata alqawarin bazan sake waiwayarta ba har sai ranar dana cika maki burinki, shiyasa yau dana tabbatar da hakan nake qoqarin itama naje nacika mata alqawarinta."
"To kayi haquri ranka yadad'e har zuwa gobe tukuna kaga yanzu marece yayi, yaushe har ka isa kuma har kace kaje zakaje wajenta, ai kamata yayi ace yau kafin kazo kafara zuwa saboda kada jewad'in yayi yawa."
Zaunawa yayi ya tanqwashe qafafuwansa agabanta kamar mai shirin d'aukar karatu sannan yace.
"Duk duniya Babu wanda yakamata yafara sanin nasarar dana samu inba keba hakan yasa nafara zuwa agareki domin neman sa albarkarki da kuma addu'o'inki kafin naje wajenta, idan hankalinki yafi kwanciya dana bari sai gobe zanyi hakan don faranta maki koda kuwa zuciyata bata so."
"Eh bawai nafi son hakan bane, kakirata kaji idan tayarda kabari sai goben shikenan don kada ta d'aukeka cikin masu karya alqawari."
Murmushi yayi had'e da cewa.
"Dame zan kirata gwaggo bayan tunda muka rabu da ita bamu koma waya ba balle muhad'u da ita, asalima har nasoma mantawa da muryarta saboda nadad'e banji ba, wataqil itama ta canza lambar waya tunda jiya ba yau ba."
Riqe kunnensa tayi had'e da cewa.
"Da kuwa kazamo gajiyayye a fannin soyayya domin komai dad'ewar masoya basu had'uba idan da halacci bazasu manta muryar juna ba matuqar akwai amana a tsakani."
"Kiyi haquri mamana da abunda zance, kenan hakan na nufin har yanzu kema baki manta da muryar abbana ba?."
Jikinta a sanyaye tasaki kunnensa da take riqe dashi fuskarta na mai sauyawa daga yanayin farinciki da take izuwa damuwa, da sauri yayi nail down had'e da cewa.
"Kiyafemun idan fad'ar hakan ya b'ata maki rai, akoda yaushe Ina mai qoqarin nesanta kaina da duk wata kalma data shafi mahaifina saboda nafaranta maki kamar yanda kike buqata amma hakan ba yana nufin na manta dashi bane a matsayinsa na uba awurina, kiyi haquri bana gaji bane da bin umurninki kawai yau natsinci kaina da fad'ar hakanne sanadiyar abunda kika fad'a, don ALLAH kada kiyi fushi dani akan haka"
Ganin yanda yadamu yasa tad'an saki fuskarta tare da d'aga hannu kamar zata maresa sannan ta ajiye tana fad'in.
"Bakayi laifi ba amatsayinka nad'a don ka ambaci mahaifinka, nakan ji ba dad'i kawaine aduk lokacin da aka tuna mani dashi, amma taya kake tunanin zan manta da muryarsa bayan a kullum inajin muryarka?, Hakan zai kasancene kawai idan rouhina yarabu da gangar jikina, tashi katafi, ALLAH yasa kaci galaba a soyayyarka kuma yabaka ikon shiga gaban duk wani Abu da zai shiga tsakaninka da ita, ya hanaka zubar da qwalla acikin soyayyarka kamar yanda nayi."
"Amin ya rabbi gwaggo, Amma nafasa tafiyar sai gobe in Sha ALLAH, bazan iya tafiya nabarki da b'acin ran da nine silar sakaki acikinsa ba koda da qwarar zarra ne."
Wani farinciki taji ya dirar mata azuciya saboda jin kalamansa, tabbas tasan yana iya qoqarinsa wajen faranta mata, don haka itama dole taso duk abunda zai faranta masa, ko kad'an bata tab'a sa tsammanin biyayyarsa tayi girman da zai datse duk wata alaqa da abunda yake matuqar so ba musamman waya da baza'a iya yiwa kowane mutum shamaki akanta ba, murmushin daya fassara masa irin farincikin dake zuciyarta ta sakar masa had'e da cewa.
"Tashi kaje marece nayi Abu sumayya, ALLAH ya tsare hanya, kuma kagaishemun da ita sosai kaji ko.?"
Cikin qwarin guiwa yamiqe yanajin farinciki shima aransa tare da yimata sallama sannan yabar d'akin, part d'in Fatima yanufa itama yayi mata sallama had'e da kama hanya yana mai fatar samun masoyansa cikin qoshin lafiya.
Bashi ya isa kano ba sai zuwa qarfe takwas da rabi na dare, kai tsaye ya nufi anguwar su batool batare daya biya ko Ina ba don ko baba balarabe da baffa bai sanar dasu zancen zuwansa ba saida ya iso sunata mamakin abunda ya dawo dashi bayan sunsan yau yakoma,
A anguwar sharad'a phase 1 little yasa Mai mashin d'in daya d'aukosa ya ajiyesa kamar yanda batool ta tab'a fad'a masa.
Bayan ya sallami mai mashin d'in yanufi qofar wani gida daya hango mai gadin gidan awaje shida wani mutum saman kujeru, hannu yamiqa masu duk suka gaisa sannan yashiga tambayarsu don ALLAH a ina ne gidan Alhaji umar fari,
Tasowa d'aya daga cikinsu yayi ya d'an matso kusa dashi tare da nuna masa wani gida can gaba kad'an da yatsa yana fad'in.
"Kaga wacan gidan mai gate kalar ruwan qwai?, to ka matsa gaba canne gidansa?"
"Alhaji umar fari nake tambayarka fa?"
"Eh! Kaje mana canne gidan, halan kai baqone agarin?"
"A'a! kawai dai bansan gidan bane."
Little yabashi amsa had'e da miqa masa hannu yayi masa godiya sosai sannan yawuce.
Bakin gate ya tsaya lokacin daya isa qidan yana qarewa girmansa da had'uwarsa kallo, gabansa ne ya soma fad'uwa da sauri ya dafe qirjinsa tare da isa jikin gate d'in ya d'an qwanqwasa mai gadin ya leqo had'e da cewa.
"Waye?"
"Amm..nine?"
"Kaine wa?"
"Baqon batool ne."
Bud'e masa yayi tare da cewa ya shigo, bayan yashiga ciki maigidan yadinga qare masa kallo tun daga sama har qasa sannan yace.
"Jira, Bari afad'o mata."
A daidai bakin qofar shiga falon part d'insu batool ya tsaya tare dayin sallama,