Sashe 53
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kin cuceni hawwa kinci amanar zaman da mukayi dake, haqiqa ba qaramin kuskure natabka ba wajen zab'awa d'ana ke amatsayin uwa, gashi yanzu duk wani farincikin mu dani har shi kin rusa mana shi, naso nacigaba da haqurin zama dake ko don albarkacin d'anmu har lokacin da mutuwa zata rabamu, amma bazan iyaba, ko kad'an bazan iyaci gaba da zama da mushirikar mace da bata tsoron ALLAH ba kamarki, macen da batada imani da tausayi, son kanta yasa ta cilla mutane da yawa cikin wani hali, ALLAH yasani nayi iya qoqarin zaman da zan iya dake amma yanzu kitafi na sakeki, na sakeki hawwa saki biyu, keji duk abunda kika yimun nayafe maki duniya da lahira albarkacin yaronmu, Amma Ina so kisani bazan tab'a d'aga maki k'afa akan sauran haqqoqan bayinsa da kika zalunta ba, wlh ni da kaina zan tsaya na bimusu shi koda duka abunda ALLAH ya mallakamun aduniya zai qare musamman haqqin wannan qanqanuwar yarinyar da kika d'auka, yarinyar da zuciyarta bata san komai ba sai tarin qauna da soyayya agaremu, tayi mana halacci mai d'inbin yawa kama daga soyayyar da take yiwa d'anmu har zuwa kulawar data bani agidannan nasamu lafiya da haqurin cin kashin da kika tayi mata amma kikasa qafa kika shure duk wud'annan abubuwan keda marasa imanin da kuka had'a baki kuka cutar mana da ita, in sha ALLAH, ALLAH bazai barki ba har sai ya hukuntaki tun aduniya kafin kije lahira." Yana gama maganar yajuya yafice daga gidan ko gani bayayi saboda tsananin b'acin rai, tafiya mai nisa yayi baffa Usman na biye dashi kafin yasamu waje ya zauna, kuka ya shiga rerawa tamkar qaramin yaro cike da nadamar sanin Yaya hawwa da yayi aduniya, gaba d'aya ji yakeyi yatsani duk wani abu daya dangance ta balle ita kanta, Saida yayi kukansa mai isarsa sannan yamiqe suka nufi asibiti, akan hanyarsu suka gamu da baffa Ali sai faman sabbatu yakeyi wai Nuraddeen ya maisheshi d'an iska ya gudu daga asibiti yabarshi, gashi yasa agaban mutane likita yayi mashi wala qanci, har ya d'an gotasu zai wuce baffa Usman yajuyo don da alama duk kansu basuga juna ba sai yanzu.
"Ali Ina kanufa kuma haka?, Ko har Nuraddeen d'in yatashi an baku sallama ne.?"
"Af Yaya kun dawo? Injin an dace anga yarinyar?, "
"Kai ka amsamun tambayar da nayi maka, yarinya kam idan da rabon agata ko anqi ko anso ai ganinta za'ayi da yardar ALLAH." Baffa Usman yabashi amsa yana kafesa da idanuwa,
"Aw Nuraddeen kake magana?, ai kabarni da shashashan yaro, wai daga infita inyo sallah yaronnan ya gudu daga asibiti, sai dawowa nayi natarar da likaita na tambayarsa yarufeni da fad'a agaban mutane baka ganiba abunnan zak kunya."
Shiru baffa Usman yayi cike da mamaki yana kallonsa kafin yaji muryar baffa yace
"Ba komai Aliyu, Nuraddeen ai d'an kane duk abunda kayi masa ko kabari ya samesa kanka kayiwa, shidai zumunci yananan rataye aqasan al'arshi duk wanda ya gyara yaga da kyau wanda kuma ya munana yaga akasin haka, ni dai addu'a ta d'aya shine ubangijin dake tare da waccan yarinyar shima yakare mani shi aduk inda ya tafi, kuma Allah ya qaddara had'uwarsa da ita cikin amincinsa da yardarsa."
Yana gama fad'ar haka yanufi hanyar gidan daya d'aukarwa su Nuraddeen haya yana fad'in. "Usman zo mutafi."
Bayansa baffa Usman yabi shi kuma baffa Ali yawuce gida yana maijin d'acin maganganun da baffa yafad'a masa, "wato duk abunda nayi masa baiga qoqarina ba, amaimakon yaga laifin d'ansa laifina yake gani, ai shikenan gobema ranace" haka baffa Ali yaba hanya yana fad'a cike dajin haushin d'an uwan nasa har ya isa gida,
Yana isa kururuwar yaya hawwa yafara jiyowa tun daga zaure har ya iso cikin gidan, gaba d'aya ta zauce sai masifa takeyi tamkar wata tsohuwar mahaukaciya, kallo d'aya yayi mata ya kauda kai Inna ruqayya na gefe yace da ita, "yau mutuniyarki ko lafiya?, Ko duk cikin tsarin data tanada ne yau don kar agano ita ta halakarwa da mutane 'ya?"
"Ohommata! Saki daine data sha yake neman zautar da ita bayan asirinta ya tonu."
"Tab kice yau taga fushin maza, ai dama Yaya haurine dashi amma idan ransa yab'aci ba'a mai kyau, ni kaina d'agamun qafa yakeyi saboda wasiccin da baaba tabashi shiyasa kikaga Ina cin karena ba babbaka, badon haka nan ba wlh inya riqani sai buzuna, kawai tagodewa ALLAH da yasa sakin d'aine yayi mata bai had'a mata da duka ba."
"Ita dai tasani can taqare mata."
Kujera Baffa Ali ya jawo 'yar ta zaman tsakar gida ya zauna yan sauraren asharariyar da Yaya hawwa ke d'urowa daga shiyarsu yace.
"Ikon ALLAH! Shin waike rakkiya meya jawo wannan sakin da maganganun da naji tana yab'owa masu kama da gugar zana, ko dai Yaya yagano ita tayi tsiyar?"
Nan Inna ruqayya takwashe qarya da gaskiya tafad'a masa akan abunda yafaru, wata irin zabura baffa Ali yayi yna kallonta sannan yace, "Amma wannan muneera anyi d'ebabbiyar yarinya, yanzu duk wannan fitinar ita tajawo mana ita? to tsakanina da ALLAH tajawo mana abunda yafi qarfinmu, wannan matar mara imani da kike gani ba qyalemu zatayi ba, shi kuma yaya da kikaji yayi shiru baice maki komai ba akwai had'ari, don wlh shirunsa da kike gani ba alkhairi bane."
Nan take tsoro da fargabar abunda zai biyo bayansu ya mamaye masu zukata, aran baffa Ali kuwa tunanin yanda zasu tsere na kwanaki ya shigayi don ya tabbata baffa zai juyo garesu, babban takicinsa d'aya yaran dake gabansu, idan sun gudu to a hannun wa zasu barsu?.
••• ••• •••
A b'an garensu Dr nura kuwa saida yakai Fatima d'akin da aka kwantar da jaririn Rashida tukuna yaje yabiya bill d'in kud'in da wata nurse tabashi lokcin da suka dawo nan inda Rashida take sannan yayiwa Fatima sallama bayan ya tabbatar mata da ko nawa ake buqata idan wata matsala ta taso ta bud'e safe d'in da yake ajiye kud'i ta d'iba, wata nurse takira tace don ALLAH takula mata da patient d'in dake gado no15 zataje tadawo sannan taje tashiga motar da Dr keciki yana jiranta, Tasha yanufa yasamu motar da zata kaishi kano ita kuma tajuyo da motar zuwa asibiti,
Bayan kwana biyu Rashida tafara jin sauqi sosai bayan ta shanye tulunan oxygen har guda biyar haka yaronta shima saida yashanye oxygen uku sannan yadawo normal don gaba d'aya likitoci da nurses d'in dake d'akin har sun fitar masa darai sai gashi cikin ikon ALLAH da yardarshi yatashi, yana samun lafiya sosai shima don har an fara kawo matashi yau ta bashi nono, sosai take samun kulawa wajen Fatima da ita har babynta kullum tana tare dasu, musamman tasamu wata tsohuwa a asibiti irin masu shara da mopping d'innan tana biyanta kullum idan zataje gida tayo wanka tare da had'o abinci sai tasa ita kuma ta kula mata da ita, gaba d'aya Fatima ta sadaukar da lokacinta a asibitin don ganin tabasu cikakkiyar kulawa,
Zaune take agefen gado tana kallon yanda nurse d'in dake gyarawa Rashida yanda zataba jaririnta nono, cike da sha'awa take kallonsu tana murmushi kafin can taji 'yar qarar Rashida saboda zafin da taji lokacin da yaron yafara Kama nonon yanasha, da sauri tamiqe tazo kusa gareta tana shafa kanta.
"Sorry kiyi hak'uri ko! Haka kowace uwa keji lokacinda yaronta yafara kama nonon, amma idan kika jure ahankali zai dena zafin gaba d'aya."
Ita dai Rashida kasa amsa mata tayi sai faman b'ata rai takeyi tana cije baki saboda zafin da takeji, dariya nurse d'in tayi had'e da yimata sannu sannan tabar wajen, Saida yasha ya qoshi tana kallonsa kamarsa gaba d'aya babu inda yaron yabarota kamarshi sak da ita farin fatarta kad'aine be biyo don duk da take da duhu ga alama bazaiyi hasken taba, wasu zafafan hawayene suka zubo mata tanajin wata irin qauna yaron da soyayyarsa na mamaye mata zuciya, a hankali tashiga rera kukan tausayin kanta dana d'anta, ko kad'an bata tab'a tsammanin cewa tsanar da uwar mijinta keyi mata ba tayi zurfin da zata iya salwantar mata da rayuwa ba har tarabata da farincikinta, gashi yanzu tahanasu jin dad'in rayuwarsu, tahana d'anta yaji d'imi da soyayyar mahaifinsa, tajefata cikin wata rayuwar da batasan ko meye makomarta ba, ta nisantata da iyayenta ta cutar da ita, tun kukan nafita ba sauti har yafara bayyana, Fatima dake zaune tana kallonta ta karb'i yaron don har ya soma bacci had'e da cewa.
"Ali Ina kanufa kuma haka?, Ko har Nuraddeen d'in yatashi an baku sallama ne.?"
"Af Yaya kun dawo? Injin an dace anga yarinyar?, "
"Kai ka amsamun tambayar da nayi maka, yarinya kam idan da rabon agata ko anqi ko anso ai ganinta za'ayi da yardar ALLAH." Baffa Usman yabashi amsa yana kafesa da idanuwa,
"Aw Nuraddeen kake magana?, ai kabarni da shashashan yaro, wai daga infita inyo sallah yaronnan ya gudu daga asibiti, sai dawowa nayi natarar da likaita na tambayarsa yarufeni da fad'a agaban mutane baka ganiba abunnan zak kunya."
Shiru baffa Usman yayi cike da mamaki yana kallonsa kafin yaji muryar baffa yace
"Ba komai Aliyu, Nuraddeen ai d'an kane duk abunda kayi masa ko kabari ya samesa kanka kayiwa, shidai zumunci yananan rataye aqasan al'arshi duk wanda ya gyara yaga da kyau wanda kuma ya munana yaga akasin haka, ni dai addu'a ta d'aya shine ubangijin dake tare da waccan yarinyar shima yakare mani shi aduk inda ya tafi, kuma Allah ya qaddara had'uwarsa da ita cikin amincinsa da yardarsa."
Yana gama fad'ar haka yanufi hanyar gidan daya d'aukarwa su Nuraddeen haya yana fad'in. "Usman zo mutafi."
Bayansa baffa Usman yabi shi kuma baffa Ali yawuce gida yana maijin d'acin maganganun da baffa yafad'a masa, "wato duk abunda nayi masa baiga qoqarina ba, amaimakon yaga laifin d'ansa laifina yake gani, ai shikenan gobema ranace" haka baffa Ali yaba hanya yana fad'a cike dajin haushin d'an uwan nasa har ya isa gida,
Yana isa kururuwar yaya hawwa yafara jiyowa tun daga zaure har ya iso cikin gidan, gaba d'aya ta zauce sai masifa takeyi tamkar wata tsohuwar mahaukaciya, kallo d'aya yayi mata ya kauda kai Inna ruqayya na gefe yace da ita, "yau mutuniyarki ko lafiya?, Ko duk cikin tsarin data tanada ne yau don kar agano ita ta halakarwa da mutane 'ya?"
"Ohommata! Saki daine data sha yake neman zautar da ita bayan asirinta ya tonu."
"Tab kice yau taga fushin maza, ai dama Yaya haurine dashi amma idan ransa yab'aci ba'a mai kyau, ni kaina d'agamun qafa yakeyi saboda wasiccin da baaba tabashi shiyasa kikaga Ina cin karena ba babbaka, badon haka nan ba wlh inya riqani sai buzuna, kawai tagodewa ALLAH da yasa sakin d'aine yayi mata bai had'a mata da duka ba."
"Ita dai tasani can taqare mata."
Kujera Baffa Ali ya jawo 'yar ta zaman tsakar gida ya zauna yan sauraren asharariyar da Yaya hawwa ke d'urowa daga shiyarsu yace.
"Ikon ALLAH! Shin waike rakkiya meya jawo wannan sakin da maganganun da naji tana yab'owa masu kama da gugar zana, ko dai Yaya yagano ita tayi tsiyar?"
Nan Inna ruqayya takwashe qarya da gaskiya tafad'a masa akan abunda yafaru, wata irin zabura baffa Ali yayi yna kallonta sannan yace, "Amma wannan muneera anyi d'ebabbiyar yarinya, yanzu duk wannan fitinar ita tajawo mana ita? to tsakanina da ALLAH tajawo mana abunda yafi qarfinmu, wannan matar mara imani da kike gani ba qyalemu zatayi ba, shi kuma yaya da kikaji yayi shiru baice maki komai ba akwai had'ari, don wlh shirunsa da kike gani ba alkhairi bane."
Nan take tsoro da fargabar abunda zai biyo bayansu ya mamaye masu zukata, aran baffa Ali kuwa tunanin yanda zasu tsere na kwanaki ya shigayi don ya tabbata baffa zai juyo garesu, babban takicinsa d'aya yaran dake gabansu, idan sun gudu to a hannun wa zasu barsu?.
••• ••• •••
A b'an garensu Dr nura kuwa saida yakai Fatima d'akin da aka kwantar da jaririn Rashida tukuna yaje yabiya bill d'in kud'in da wata nurse tabashi lokcin da suka dawo nan inda Rashida take sannan yayiwa Fatima sallama bayan ya tabbatar mata da ko nawa ake buqata idan wata matsala ta taso ta bud'e safe d'in da yake ajiye kud'i ta d'iba, wata nurse takira tace don ALLAH takula mata da patient d'in dake gado no15 zataje tadawo sannan taje tashiga motar da Dr keciki yana jiranta, Tasha yanufa yasamu motar da zata kaishi kano ita kuma tajuyo da motar zuwa asibiti,
Bayan kwana biyu Rashida tafara jin sauqi sosai bayan ta shanye tulunan oxygen har guda biyar haka yaronta shima saida yashanye oxygen uku sannan yadawo normal don gaba d'aya likitoci da nurses d'in dake d'akin har sun fitar masa darai sai gashi cikin ikon ALLAH da yardarshi yatashi, yana samun lafiya sosai shima don har an fara kawo matashi yau ta bashi nono, sosai take samun kulawa wajen Fatima da ita har babynta kullum tana tare dasu, musamman tasamu wata tsohuwa a asibiti irin masu shara da mopping d'innan tana biyanta kullum idan zataje gida tayo wanka tare da had'o abinci sai tasa ita kuma ta kula mata da ita, gaba d'aya Fatima ta sadaukar da lokacinta a asibitin don ganin tabasu cikakkiyar kulawa,
Zaune take agefen gado tana kallon yanda nurse d'in dake gyarawa Rashida yanda zataba jaririnta nono, cike da sha'awa take kallonsu tana murmushi kafin can taji 'yar qarar Rashida saboda zafin da taji lokacin da yaron yafara Kama nonon yanasha, da sauri tamiqe tazo kusa gareta tana shafa kanta.
"Sorry kiyi hak'uri ko! Haka kowace uwa keji lokacinda yaronta yafara kama nonon, amma idan kika jure ahankali zai dena zafin gaba d'aya."
Ita dai Rashida kasa amsa mata tayi sai faman b'ata rai takeyi tana cije baki saboda zafin da takeji, dariya nurse d'in tayi had'e da yimata sannu sannan tabar wajen, Saida yasha ya qoshi tana kallonsa kamarsa gaba d'aya babu inda yaron yabarota kamarshi sak da ita farin fatarta kad'aine be biyo don duk da take da duhu ga alama bazaiyi hasken taba, wasu zafafan hawayene suka zubo mata tanajin wata irin qauna yaron da soyayyarsa na mamaye mata zuciya, a hankali tashiga rera kukan tausayin kanta dana d'anta, ko kad'an bata tab'a tsammanin cewa tsanar da uwar mijinta keyi mata ba tayi zurfin da zata iya salwantar mata da rayuwa ba har tarabata da farincikinta, gashi yanzu tahanasu jin dad'in rayuwarsu, tahana d'anta yaji d'imi da soyayyar mahaifinsa, tajefata cikin wata rayuwar da batasan ko meye makomarta ba, ta nisantata da iyayenta ta cutar da ita, tun kukan nafita ba sauti har yafara bayyana, Fatima dake zaune tana kallonta ta karb'i yaron don har ya soma bacci had'e da cewa.