Sashe 113
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Eyyeeee ashe da gaske kikeyi gimbiya, nasamu gashi har mun kama hanya."
"To Allah ya saukeka lafiya ya karemun kai daga sharrin qarfe, mutum da kuma aljani."
"Amin gimbiya," yafad'a cike dajin dad'in addu'arta.
••• ••• •••
A can borno kuwa hajia nafeesa najen qesheqeshin cewa dady zaije nemawa little auren batool hankalinta ya tashi, tasan tabbas ba abunda zai hana dady zuwa sai in baya raye kuma duk yanda zaiyi ya wanke little daga kashin kajin data shafa masa awajen mahaifin batool sai yayi, don haka takasa zaune ta kasa tsaye har saida dady ya shigo, da yake yau zai dawo part d'in nata, ALLAH ALLAH tadingayi yayi sauri yagama cin abincin don ta maganta masa abunda ta qudurta aranta.
Yana kammalawa tace.
"Am Alhaji nikuwa Ina son yin magana dakai idan ka amince."
"Ina jinki hajiya nafeesa, injin dai ko lafiya?"
Yafad'a tare da d'aukar jarida yakoma can saman kujerun dake tsakiyar falon ya zauna, biyo bayansa tayi ta zauna kusa dashi had'e dayin shiru na 'yan mintota be sannan yace.
"Shin kasan ko yaron nan shima son batool yakeyi naji ana zancen zakaje nemawa wanda bayada asali ita."
Kar ya fahimci inda zancenta yanufa amma sai yabasar yana qoqarin bud'o wani shafin jaridar yace.
"Wane yaro kike zancen kuma wace batool d'in." 'dan muskutawa tayi daga zaunen da take sannan tace.
"Shakur mana da batool 'ya gidan kawuna alhaji umar fari dake zaune kano, yanzu hakan yana can kwance baya jin dad'i saboda yaji kana shirin zuwa nemoma wani bare ita gashi shi daya jima yana sonta, wlh alhaji zai iya rasa rayuwarsa akanta, shiyasa nace bari nafad'a maka don ya kamata kaduba wannan al'amarin.
Cigaba yayi da bud'a jaridarsa batare daya tankata ba har natsawon mintota da tagaji tace.
"Haba Alhaji!, Dakai fa nake magana kayi mani shiru.."
"Mts..shin mema kike cewa?"
Duk da ranta ya b'aci haka tasake daurewa ta maimaita masa tanaji kamar ta qwalla ihu saboda abunda yayi mata, ajiye jaridar yayi sannan ya aza qafarsa d'aya akan d'aya yana kallon yanda tacika tayi fam, yasan kad'an take jira yanzu tafitinesa ta hanasa bacci mai dad'i don haka sai yace.
"Shikenan naji, Kuma in sha ALLAH kafin muje zanyi tunani akai, idan naga yafi dacewa da ita shikenan sai ayo maganar dashi, duk da shima yaron da kikacewa bayada asali kakarsa na acikin gidannan kuma a matsayin matata baza'a ce abawa daji gida bai qoshi ba, don haka in sha ALLAH za'ayi abunda ya dace, Ina shi shakur d'in?."
Washe baki tayi saboda taji dad'in yanda haqarta zata cimma ruwa anata tunanin sannan tace.
"Yana can sashensa kwance tun safe ba inda yaje."
"Ok Bari nadubosa."
"Ai daka bari har nan da zuwa safiya, don inaga yasamu yayi bacci yanzu kada atashesa."
Tafad'a gabanta na fad'uwa don bata masan inda yaron nata take ba tana qoqarin dakatar dashi, cigaba yayi da tafiyarsa yana fad'in.
"Eh bara dai nadubosa, ai kamata yayi tun wuri ki sanar dani, yanzu idan har ciwon yayi masa tsanani ya cutar dashi ban sani ba, sai kice a'a." Yasa kai ya ficewarsa.
Da sauri taje ta d'au wayarta takira shakur lokacin yana zaune yana game da wayarsa hankali kwance.
"Kai shashasha, me kakeyi yanzu?"
"Zaune nake Ina game awayana lafiya mom?"
"Maza, maza, kanemi waje ka kwanta kuma katabbatar ka lullub'a, nafad'awa dadynku cewa bakada lafiya saboda kaji zaije nemawa wannan shegen auren batool, shine zaizo dubaka, maza ka kwanta kafin ya qaraso."
"Mom nifa Ina da.."
"dallah rufamun baki sakaran banza, kayi abunda nace kawai."
Jefar da wayar yayi agefe tare da komawa yakwanta saman gadonsa ya lullub'e yana qunquni, kasancewar qofar d'akin abud'e take kuma ga fitila akunne yasa har dady yaqaraso bai sani ba,
Shikuwa dady qunqunin da yakeyi ya tabbatar masa da cewa idanuwansa biyu, shigowa yayi ciki ya tako har gaban gadon nasa ya zauna wajen gefen kansa cikin muryar dake tabbatarwa da Shakur bawasa atattare da mahaifin nasa yaji yace.
"Kai Shakur tashi!"
Aikuwa kamar jira yakeyi yayi zumbur yamiqe yayi zaune tsakiyar gadon idanuwansa wuqiwuqi babu alamun ko ciwon kai yayi balle zazzab'i,
Saida dady yaqare masa kallo sannan yayi murmushi had'e da cewa.
"Meyake damunka ne?"
"Ba.ba.babu komai dady zazzab'ine kawai" yafad'a cikin rawar murya yana b'ab'b'ata rai, d'aure fuska dady yayi sosai had'e da cewa
"Ok. To meye alaqarka da batool qanwar mahaifiyarka, naji ance kamar kana sonta, meye gaskiya?"
Har zaiyi magana dady ya nunasa da yatsa yana zaro masa idanuwa. "Ka tabbatar kafad'amun gaskiya, idan nace gaskiya Ina nufin magana qwaya d'aya tilo wacce batada tabiyu, samuwar ta biyunta kan iyasa na d'auki mummunan mataki akanka, Ina saurarenka!"
Wani qugi Shakur cikinsa yayi don yasan halin abban nasa, idan yace abu to tabbas zaiyisa, wani irin zufane ya keto masa ya shiga sharewa tare da kallon mahaifinnasa yace.
"Dady maganar gaskiya ni bana son batool, asalima bamu fiye jituwa da ita ba, mom ce ke matsamun akan innemi aurenta saboda dani tafi dacewa ba little ba, nayi qoqarin nuna mata banison yarinyar saboda cin mutuncin da take jawowa tana yimani amma taqi ta fahimta, Dana matsa matsa mata da zancen sai tace idan har nakoma musa mata akan maganar zan fuskanci fushinta, shiyasa kawai nahaqura Ina qoqarin cusawa zuciyata yarinyar."
Murmushi dady yayi had'e da bubbuga bayansa sannan yace.
"Gud, kanada wacce kake so yanzu?"
"Eh dady, amma mom bata son na aureta."
"Wacece ita?, kuma meyasa bata sonta?."
"Qanwar matar ya faruq ce dady, sunanta hafsat amma ana kiranta iman, mom Bata sonta ne wai saboda ammie tunda yayarta surukar tace." Tsaki dady yayi saboda gaba d'aya alamurran hajia nafeesa ba komai acikin Inba tarin hauka da shirme ba, bata tab'a tanadar qwaqqwarar hujja cmai ma'ana sai shirme,
"Katabbata yarinyar na sonka kamar yanda kake sonta?" Dady yafad'a yana kallonsa.
"Eh dady."
"Shikenan! Koma ka kwantawarka, Kuma katabbatar kayo arwala ka kashe fitilar d'akin kafin ka koma kaji nafad'a maka."
"To dady nagode saida safe."
"ALLAH yatashemu lafiya, ubangiji yayi maku albarka."
"Amin dady" Shakur yafad'a tare da yaye bargon daya lullub'a dashi ya sauko daga saman gadon tare da wucewa toilet yana maijin wani sanyi aransa, dama duk abunda yake yiwa batool mom d'insa ke sashi, shi kuma sai yana amfani da wannan damar don ya tunzura batool taqara tsanarsa aranta yanda koda ance za'a had'a aurensa da ita bazata yarda ba.
Koda dady yakoma bai cema hajia nafeesa komai ba yayi shirinsa na kwanciya ya kwanta yana mai addua'ar ALLAH yatashesa lafiya.
Da sassafe yakira faruq qanen dr, yace yaturo masa lambar mahaifin surayya matarsa, bayan yaturo masa sukayi magana mai tsawo sannan yakashe yakira dr, shima nan sun d'an jima kafin yakashe yafad'a toilet yayo wanka.
Misalin qarfe 9:30 na safe dady yagama shirin tafiyarsa kano yashiga sukayi sallama dasu umma da ammie sannan yadawo itama hajia nafeesa sukayi sallama batare daya nuna mata komai ba, so take ta taddo masa da zancen amma ayanayin da tagansa ciki sai tad'auka haqartace ta cimma ruwa.
Koda yafito tana biye dashi ta rakoshi Dr da faruq na tsaye bakin mota suna jiran fitowarsa don tare zasu fita tawani galla masu harara aranta tana mai jin kamar takamo su tashaqe tsabar tsanar da tayi masu.
Kai tsaye gidan iyayen matar faruq suka nufa su uku lokacin mahifinta shima yakirawo 'yan uwansa su uku sun iso suka nemawa shakur auren hafsat (iman), iyayen nata sun tarbesu hannu biyu kuma sun amince da maganar don seda suka tambayeta tace eh tana sonsa sannan suka bashi ita, yarage sadaki da sa rana yarage, saida sukayi masu godiya sosai sannan suka baro gidan suna yabawa nagartar sarakanan na faruq.
A bakin titi suka ajiye faruq su kuma suka kama hanyar kano.
Suna Isa misalin qarfe uku na rana suka nufi gidan baba balarabe kai tsaye suka samu anhad'a masu 'yar qwarya qwaryar liyafa don dama yasan da maganar.
Bayan sunci sun sha sun qoshi baba balarabe ya d'auko masu zancen mahaifan little ta b'angaren mahaifinsa inda ya nuna masu bai kamata aje nema masa aureba bada suba saboda haqinsu ne, asalima sun fisu qarfi dashi, nan dai yazauna ya labarta masu duk abunda yafaru da yanda yahad'asa da dangin mahaifina nasa tacikin sirri, sun matuqar gamsuwa tare da fahimtarsa, kuma sunyaba masa bisa qoqarin da yayi inda suka d'aukar masa alqawarin cewa suma zasu riqe wannan sirrin batare da sun bari umma da Rashida sunji ba har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta, anan yake sanar dasu cewa ai yariga daya fad'amasu baffa zancen yanzu haka shi little yana can tare zasu dawo dasu.
Ana kiraye kirayen sallar la'asar su baffa suka iso gidan baba balarabe, sunji dad'in yanda ya nuna muhimmancinsu acikin sha'anin tare da yimasa godiya sannan baba balarabe ya gabatar masu dasu Dr.
Yauma baffa seda yayi kuka yanata sakawa Dr albarka bisa taimakon da yayiwa Rashida da kuma gudan jininsa little alokacin da suke matuqar buqatar sa, hakama suka taru shida baffa Usman suka dinga yiwa dady godiya har saida yafara jin kunya don kusan duka sun girmesa, musamman baffa, Dr kuwa shidai mamakine ya ishesa da aka nuna masa baffa amatsayin mahaifin baban little wanda yasan ranar da sukaje qauyen shida Rashida bashine sukayi magana dashib amatsayin kakan little, asalima gaba d'aya baya cikin su biyun don haka sai yafara tunanin tabbas akwai wata aqasa acikin al_amarin Wanda su Basu sani ba, koma dai meye shi Wanda yagani tabbas yanada nasaba dasu don ga kamanninsu da shi nan, yana wannan tunanin ne suka miqe zasu tafi can gidansu batool d'in, saidai awannan karon qin binsu yayi saboda aganinsa su hud'un sun wadatar a matsayinsu na manyan iyaye agaresa.
Dady shike jan motar sai baffa Usman a gefensa, baba balarabe kuwa da baffa suna baya sannan suka bar qofar gidan tare da nufar unguwar sharad'a phase 1.
Dama tuni little ya sake kiran batool ya jaddada mata zancen zuwan iyayen nata don itama ta sanar da nata iyayen, cikin farinciki batare da wani shakku ko shayi ba taje ta iske su uncle Hassan da Hussain lokacin suna zaune tare da mahaifin nata da ko kallo bata ishesa ba a harabar gidan tasanar dasu,
Murmushi uncle Hassan yayi had'e da cewa.
"To yaushe!"
"Yanzu uncle h."
"To Allah ya saukeka lafiya ya karemun kai daga sharrin qarfe, mutum da kuma aljani."
"Amin gimbiya," yafad'a cike dajin dad'in addu'arta.
••• ••• •••
A can borno kuwa hajia nafeesa najen qesheqeshin cewa dady zaije nemawa little auren batool hankalinta ya tashi, tasan tabbas ba abunda zai hana dady zuwa sai in baya raye kuma duk yanda zaiyi ya wanke little daga kashin kajin data shafa masa awajen mahaifin batool sai yayi, don haka takasa zaune ta kasa tsaye har saida dady ya shigo, da yake yau zai dawo part d'in nata, ALLAH ALLAH tadingayi yayi sauri yagama cin abincin don ta maganta masa abunda ta qudurta aranta.
Yana kammalawa tace.
"Am Alhaji nikuwa Ina son yin magana dakai idan ka amince."
"Ina jinki hajiya nafeesa, injin dai ko lafiya?"
Yafad'a tare da d'aukar jarida yakoma can saman kujerun dake tsakiyar falon ya zauna, biyo bayansa tayi ta zauna kusa dashi had'e dayin shiru na 'yan mintota be sannan yace.
"Shin kasan ko yaron nan shima son batool yakeyi naji ana zancen zakaje nemawa wanda bayada asali ita."
Kar ya fahimci inda zancenta yanufa amma sai yabasar yana qoqarin bud'o wani shafin jaridar yace.
"Wane yaro kike zancen kuma wace batool d'in." 'dan muskutawa tayi daga zaunen da take sannan tace.
"Shakur mana da batool 'ya gidan kawuna alhaji umar fari dake zaune kano, yanzu hakan yana can kwance baya jin dad'i saboda yaji kana shirin zuwa nemoma wani bare ita gashi shi daya jima yana sonta, wlh alhaji zai iya rasa rayuwarsa akanta, shiyasa nace bari nafad'a maka don ya kamata kaduba wannan al'amarin.
Cigaba yayi da bud'a jaridarsa batare daya tankata ba har natsawon mintota da tagaji tace.
"Haba Alhaji!, Dakai fa nake magana kayi mani shiru.."
"Mts..shin mema kike cewa?"
Duk da ranta ya b'aci haka tasake daurewa ta maimaita masa tanaji kamar ta qwalla ihu saboda abunda yayi mata, ajiye jaridar yayi sannan ya aza qafarsa d'aya akan d'aya yana kallon yanda tacika tayi fam, yasan kad'an take jira yanzu tafitinesa ta hanasa bacci mai dad'i don haka sai yace.
"Shikenan naji, Kuma in sha ALLAH kafin muje zanyi tunani akai, idan naga yafi dacewa da ita shikenan sai ayo maganar dashi, duk da shima yaron da kikacewa bayada asali kakarsa na acikin gidannan kuma a matsayin matata baza'a ce abawa daji gida bai qoshi ba, don haka in sha ALLAH za'ayi abunda ya dace, Ina shi shakur d'in?."
Washe baki tayi saboda taji dad'in yanda haqarta zata cimma ruwa anata tunanin sannan tace.
"Yana can sashensa kwance tun safe ba inda yaje."
"Ok Bari nadubosa."
"Ai daka bari har nan da zuwa safiya, don inaga yasamu yayi bacci yanzu kada atashesa."
Tafad'a gabanta na fad'uwa don bata masan inda yaron nata take ba tana qoqarin dakatar dashi, cigaba yayi da tafiyarsa yana fad'in.
"Eh bara dai nadubosa, ai kamata yayi tun wuri ki sanar dani, yanzu idan har ciwon yayi masa tsanani ya cutar dashi ban sani ba, sai kice a'a." Yasa kai ya ficewarsa.
Da sauri taje ta d'au wayarta takira shakur lokacin yana zaune yana game da wayarsa hankali kwance.
"Kai shashasha, me kakeyi yanzu?"
"Zaune nake Ina game awayana lafiya mom?"
"Maza, maza, kanemi waje ka kwanta kuma katabbatar ka lullub'a, nafad'awa dadynku cewa bakada lafiya saboda kaji zaije nemawa wannan shegen auren batool, shine zaizo dubaka, maza ka kwanta kafin ya qaraso."
"Mom nifa Ina da.."
"dallah rufamun baki sakaran banza, kayi abunda nace kawai."
Jefar da wayar yayi agefe tare da komawa yakwanta saman gadonsa ya lullub'e yana qunquni, kasancewar qofar d'akin abud'e take kuma ga fitila akunne yasa har dady yaqaraso bai sani ba,
Shikuwa dady qunqunin da yakeyi ya tabbatar masa da cewa idanuwansa biyu, shigowa yayi ciki ya tako har gaban gadon nasa ya zauna wajen gefen kansa cikin muryar dake tabbatarwa da Shakur bawasa atattare da mahaifin nasa yaji yace.
"Kai Shakur tashi!"
Aikuwa kamar jira yakeyi yayi zumbur yamiqe yayi zaune tsakiyar gadon idanuwansa wuqiwuqi babu alamun ko ciwon kai yayi balle zazzab'i,
Saida dady yaqare masa kallo sannan yayi murmushi had'e da cewa.
"Meyake damunka ne?"
"Ba.ba.babu komai dady zazzab'ine kawai" yafad'a cikin rawar murya yana b'ab'b'ata rai, d'aure fuska dady yayi sosai had'e da cewa
"Ok. To meye alaqarka da batool qanwar mahaifiyarka, naji ance kamar kana sonta, meye gaskiya?"
Har zaiyi magana dady ya nunasa da yatsa yana zaro masa idanuwa. "Ka tabbatar kafad'amun gaskiya, idan nace gaskiya Ina nufin magana qwaya d'aya tilo wacce batada tabiyu, samuwar ta biyunta kan iyasa na d'auki mummunan mataki akanka, Ina saurarenka!"
Wani qugi Shakur cikinsa yayi don yasan halin abban nasa, idan yace abu to tabbas zaiyisa, wani irin zufane ya keto masa ya shiga sharewa tare da kallon mahaifinnasa yace.
"Dady maganar gaskiya ni bana son batool, asalima bamu fiye jituwa da ita ba, mom ce ke matsamun akan innemi aurenta saboda dani tafi dacewa ba little ba, nayi qoqarin nuna mata banison yarinyar saboda cin mutuncin da take jawowa tana yimani amma taqi ta fahimta, Dana matsa matsa mata da zancen sai tace idan har nakoma musa mata akan maganar zan fuskanci fushinta, shiyasa kawai nahaqura Ina qoqarin cusawa zuciyata yarinyar."
Murmushi dady yayi had'e da bubbuga bayansa sannan yace.
"Gud, kanada wacce kake so yanzu?"
"Eh dady, amma mom bata son na aureta."
"Wacece ita?, kuma meyasa bata sonta?."
"Qanwar matar ya faruq ce dady, sunanta hafsat amma ana kiranta iman, mom Bata sonta ne wai saboda ammie tunda yayarta surukar tace." Tsaki dady yayi saboda gaba d'aya alamurran hajia nafeesa ba komai acikin Inba tarin hauka da shirme ba, bata tab'a tanadar qwaqqwarar hujja cmai ma'ana sai shirme,
"Katabbata yarinyar na sonka kamar yanda kake sonta?" Dady yafad'a yana kallonsa.
"Eh dady."
"Shikenan! Koma ka kwantawarka, Kuma katabbatar kayo arwala ka kashe fitilar d'akin kafin ka koma kaji nafad'a maka."
"To dady nagode saida safe."
"ALLAH yatashemu lafiya, ubangiji yayi maku albarka."
"Amin dady" Shakur yafad'a tare da yaye bargon daya lullub'a dashi ya sauko daga saman gadon tare da wucewa toilet yana maijin wani sanyi aransa, dama duk abunda yake yiwa batool mom d'insa ke sashi, shi kuma sai yana amfani da wannan damar don ya tunzura batool taqara tsanarsa aranta yanda koda ance za'a had'a aurensa da ita bazata yarda ba.
Koda dady yakoma bai cema hajia nafeesa komai ba yayi shirinsa na kwanciya ya kwanta yana mai addua'ar ALLAH yatashesa lafiya.
Da sassafe yakira faruq qanen dr, yace yaturo masa lambar mahaifin surayya matarsa, bayan yaturo masa sukayi magana mai tsawo sannan yakashe yakira dr, shima nan sun d'an jima kafin yakashe yafad'a toilet yayo wanka.
Misalin qarfe 9:30 na safe dady yagama shirin tafiyarsa kano yashiga sukayi sallama dasu umma da ammie sannan yadawo itama hajia nafeesa sukayi sallama batare daya nuna mata komai ba, so take ta taddo masa da zancen amma ayanayin da tagansa ciki sai tad'auka haqartace ta cimma ruwa.
Koda yafito tana biye dashi ta rakoshi Dr da faruq na tsaye bakin mota suna jiran fitowarsa don tare zasu fita tawani galla masu harara aranta tana mai jin kamar takamo su tashaqe tsabar tsanar da tayi masu.
Kai tsaye gidan iyayen matar faruq suka nufa su uku lokacin mahifinta shima yakirawo 'yan uwansa su uku sun iso suka nemawa shakur auren hafsat (iman), iyayen nata sun tarbesu hannu biyu kuma sun amince da maganar don seda suka tambayeta tace eh tana sonsa sannan suka bashi ita, yarage sadaki da sa rana yarage, saida sukayi masu godiya sosai sannan suka baro gidan suna yabawa nagartar sarakanan na faruq.
A bakin titi suka ajiye faruq su kuma suka kama hanyar kano.
Suna Isa misalin qarfe uku na rana suka nufi gidan baba balarabe kai tsaye suka samu anhad'a masu 'yar qwarya qwaryar liyafa don dama yasan da maganar.
Bayan sunci sun sha sun qoshi baba balarabe ya d'auko masu zancen mahaifan little ta b'angaren mahaifinsa inda ya nuna masu bai kamata aje nema masa aureba bada suba saboda haqinsu ne, asalima sun fisu qarfi dashi, nan dai yazauna ya labarta masu duk abunda yafaru da yanda yahad'asa da dangin mahaifina nasa tacikin sirri, sun matuqar gamsuwa tare da fahimtarsa, kuma sunyaba masa bisa qoqarin da yayi inda suka d'aukar masa alqawarin cewa suma zasu riqe wannan sirrin batare da sun bari umma da Rashida sunji ba har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta, anan yake sanar dasu cewa ai yariga daya fad'amasu baffa zancen yanzu haka shi little yana can tare zasu dawo dasu.
Ana kiraye kirayen sallar la'asar su baffa suka iso gidan baba balarabe, sunji dad'in yanda ya nuna muhimmancinsu acikin sha'anin tare da yimasa godiya sannan baba balarabe ya gabatar masu dasu Dr.
Yauma baffa seda yayi kuka yanata sakawa Dr albarka bisa taimakon da yayiwa Rashida da kuma gudan jininsa little alokacin da suke matuqar buqatar sa, hakama suka taru shida baffa Usman suka dinga yiwa dady godiya har saida yafara jin kunya don kusan duka sun girmesa, musamman baffa, Dr kuwa shidai mamakine ya ishesa da aka nuna masa baffa amatsayin mahaifin baban little wanda yasan ranar da sukaje qauyen shida Rashida bashine sukayi magana dashib amatsayin kakan little, asalima gaba d'aya baya cikin su biyun don haka sai yafara tunanin tabbas akwai wata aqasa acikin al_amarin Wanda su Basu sani ba, koma dai meye shi Wanda yagani tabbas yanada nasaba dasu don ga kamanninsu da shi nan, yana wannan tunanin ne suka miqe zasu tafi can gidansu batool d'in, saidai awannan karon qin binsu yayi saboda aganinsa su hud'un sun wadatar a matsayinsu na manyan iyaye agaresa.
Dady shike jan motar sai baffa Usman a gefensa, baba balarabe kuwa da baffa suna baya sannan suka bar qofar gidan tare da nufar unguwar sharad'a phase 1.
Dama tuni little ya sake kiran batool ya jaddada mata zancen zuwan iyayen nata don itama ta sanar da nata iyayen, cikin farinciki batare da wani shakku ko shayi ba taje ta iske su uncle Hassan da Hussain lokacin suna zaune tare da mahaifin nata da ko kallo bata ishesa ba a harabar gidan tasanar dasu,
Murmushi uncle Hassan yayi had'e da cewa.
"To yaushe!"
"Yanzu uncle h."