Sashe 116
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_Gaisuwa da fatan alkhairi agareki Auntynah *AUNTY RASHIDA GARBA 😍* sincerely i rilly dont know how to start thanking you for all what you did to me, you have encouraged me so much in my difficult time when i lost hope that i could ever do something like this, you were the one to push me on things, i am really grateful that i have such a wonderful sister like you in my life, and i just want to express my gratitude and my thanks to you. You are truly wonderful sister so thank you for the support, like, luv and everything to me..haqiqa karamcinki agareni mai girmane da bazan tab'a iya mantawa dake ba, i pray almighty ALLAH to give you a wanderful charming husband dt will luv you, care with you, support you and Charis you for ever in life,👏 *LSM AUNTY RASHIDA*_
Page___86💎
Komawa yayi akan kujerar kusa da ita ya zauna ahankali yace.
"Gimbiya tah, meya jimaki a goshi?" Yana nuna wajen da yatsa inda yaga filista da hajia mama tasa mata jiya inda goshinta ya fashe.
'Dan shafa wajen tayi had'e dayin murmushi sannan tace.
"Abu sumayya ya kake?"
"A yanzu lafiya klw nake tunda gani gaki."
"Kaga yanda rayuwa ta sauya mana ko, meyasa hakan take faruwa damu, musamman ni da zuciyata gaba d'aya yakasa hango mun kowa sai kai, gashi sai wahala rayuwa ke bamu, mahaifina na matuqar sona, ya kula dani sosai, yabani farinciki fiye da tsammaninka, saidai yakasa karanto zuciyata yafahimci irin tsantsar qaunar da nake yimaka, d'ago kanta tayi tana kallonsa idanuwanta sun cika da hawaye tace.
" _Wish that i spend some time with you only the time where there would be two of us looking at the sky and gazing at the stars, wish that we would just run away from here and run away so far, i was thinking about this the whole day and i just want to say that my love for you is so true, no matter what the hardest time it's i will be thinking of you, when i think about you, my mind goes numb, i am not me, i become so dumb, because our love was so strong, It was to me you belong, then why all this happened, I miss you so much Abu sumayya_"
Kallon cikin kwayar idanuwanta ya dingayi yana karanto tabbacin gaskiyar duk wata kalma da take fad'a, yarasa wane irin so ne takeyi masa haka, yarasa dalilin da yasa ta qaunace haka, tabbas shima ya cancanci yabata dukkanin irin wannan soyayyar da take nuna masa koda hakan na nufin zai rasa farincikinsa da natsuwarsa nahar abada, wani sassanyan murmushi ya sakar mata lokacin data kai qarshen kalamanta had'e da cewa.
"Karki damu gimbiyata, a halin yanzu ina rayuwane wa sonki da qaunarki, nayi maki alqawarin zan iya bada rayuwata domin ceto soyayyarmu, ba ina nufin zanmutu bane akan soyayyarmu ba, Ina nufin na shirya tsaf akan zan fuskanci duk wata matsala ko qalubale don naga na killaceki a inda yakamata, zan rayu don in cika maki duk wasu burikanki da mafarkanki akaina, zan biya soyayyar da kika nuna mani da zallar halacci da kuma karamci don haka kidena damar da kanki, tun asali qaunace ALLAH yasaka tsakanin ni da kuma ke, so ya biyo baya ne kawai, kiyarda dani zan baki duk wata kulawa, zan maye maki farinciki da wannan quncin da kike ciki, zan share maki wud'annan zafafan hawayen na maye maki gurbinsu da sanyayyun hawayen farinciki, Ina so kisa aranki gimbiyata, Abu sumayyanki na sonki kuma yana qaunarki har zuwa fitar lumfashinsa naqarshe,"
Sun jima suna fad'awa junansu kalamai masu dad'i da kuma sanyaya zuciya da suka sake basu qwarin guiwar cewa komai rintsi komai wuya zasu rayune kad'ai idan suna tare a qarqashin inuwa d'aya, ganin lokaci na dad'a ja gashi Rashida tace dole yau yamaidata gida yasa yamiqe yaje kitchen ya d'ibo abinci ya zauna agabanta yana ci.
Cin abincin yakeyi yana kallonta tana yimasa dariya har ya canyesa tas batare daya ankara ba sannan yamaida plate d'in kitchen yadawo inda take yace.
"Gimbiya bari naje na watso ruwa mutafi kafin gwaggo tafito tasameni."
"Shikenan ka kula mani da kanka."
Bayan ya gyara cikin wata farar shaddarsa giznah da tamatuqar yimasa kyau yanufo falon bakinsa d'auke da sallama, tsabar kyawon da yayi batool batasan lokacin da ta sakar masa murmushi tare da cewa, "kamatuqar yin kyau Abu sumayya."
"Nagode oum sumayya." Yafad'a shima yana mayar mata da murmushi, kusan atare Rashida da Fatima suka fito daga cikin d'akunansu Fatima nariqe da makullin motar dasu little zasu tafi da ita tace.
"Har anfito little?."
"Eh mama."
"Ungo to ga makullin motar ubangiji ALLAH ya tsare hanya, don ALLAH akula da titi da kyau kaji?" tamiqa masa tana kallon batool da har lokacin kezaune kanta na aqasa, jitake kamar ta fusa ihu domin gaba d'aya bata buqatar komawa gida saboda abunda zata tarar.
Murmushi tayi had'e da cewa.
"Takwarata tashi kuje lokaci na tafiya kuma don ALLAH kihi haquri kibarwa ALLAH dukkanin lamurransa, kada kikoma yunqurin yin jayayya da mahaifanki domin hakan kuskurene kinji ko.?"
"In Sha ALLAH." Batool tafad'a muryarta na kakkarwa alamun tana so tayi kuka.
Dafata Rashida tayi had'e da cewa.
"Ashsha batool, kukan zaki komawa bayan nafad'a maki cewa kuyi hak'uri, bawa baya iya tab'a canza qaddararsa aduk inda yake don haka kuka bayada wani amfani ga abunda zartar maka dashi za'ayi bakai zaka zartar dashi ba, ungo wannan littafin hisnul Muslim ne, kintab'a amfani dashi.?"
"Eh dashi mamana tayi koyamun addu'o'in safiya da marece.,"
"Masha ALLAH, kiduba cikinsa akwai babin addu'o'in hammu wal hazan, kije ki laqancesu in Sha ALLAH zaki samu sassaucin quncin zuciya dana baqinciki da damuwa kinji ko."
Hannu biyu tasa takarb'a hawaye na zubo mata, Rashida tace.
"Au bazaki dena kukanba." Cikin sake d'aga sautin kukanta tace
"Ina matuqar jin tsorone gwaggo."
Shiru Rashida tayi kafin tace "shikenan, share hawayen naki kibani lambar shi mahaifin naki."
Fad'a mata tayi ta copy digit d'in awayarta sannan tace,
"Maza jiki yana jiranku, Allah yayi maki albarka kuma ya kaiku lafiya."
Amin batool tafad'a sannan tafice tana sharar qwalla, wani gauron nisha Fatima tayi had'e da cewa Rashida.
"Yarinyar nan tabani tausayi, wlh tana matuqar son little sosai, ALLAH yakawo mata d'auki don girman qur'ani,
"Amin." Rashida tafad'a sannan sukabi bayanta, Saida sukaga tashinsu sannan suka dawo cikin gida bayan Rashida ta tabbatarwa da little cewa yakula da batool sosai kuma yaje ahankali.
Kusan awanni biyar suka shafe akan hanya kafin su iso gida, tafiya ce sukayi mai cike da nishad'i da kuma jin dad'i wacce gaba d'aya ta mantar dasu halin da suke ciki saboda yanda suka d'ebawa juna kewa sosai, atarihin rayuwarsu wannan rana itace da bazasu tab'a mantawa da itaba soboda lokacin da suka samu wajen qara bayyanawa juna sirrin dake zuciyarsu.
Rashida kuwa saida ta kwatanta sun kusa isa sannan takira mahaifin batool, lokacin yana kwance gaba d'aya duniya tayi masa zafi saboda neman batool da aka shigayi tun safe ba'a ganta ba, Wanda hakan yasa 'yan uwansa suka fito masa da b'acin ransu qarara akan cewa duk abunda yasamu batool laifinsa ne kuma ALLAH zai kamashi dashi, a matsayinsa na mahaifi bashi kad'ai ALLAH yad'orawa haqqin 'ya'yansa ba, hatta qannensa, yannensa da mahaifiyarta da qannen mahaifiyarta da qannenta duk sunada haqqi akanta don haka sun gaji da zuba masa idanuwa yana neman cilla 'yarsu cikin halaka, ada sunyi tunanin barmasa 'yarsa kamar yanda yake iqirarin cewa 'yarsa ce, Amma ayanzu zasu had'a qarfi da qarfe suyi mata abunda take so, zasu bata zab'in ranta matuqar shine kwanciyar hankalinta koda hakan na nufin zai yakicesu daga jikinsa, sun shirya tsaf wajen nuna masa cewa suma 'yarsu ce kuma zasu bata gatar daya kasa bata ayanzu,
Maganganu masu zafi suka yab'a masa kafin su sake tabbatar masa da cewa zasu je su nemo 'yarsu da kansu amma ya tabbata yazare hannunsa acikin lamurranta don su suna buqatarta idan shi baya buqatarta, baban abunda yafi b'ata masa rai shine a gabansa suka kira wanda yayiwa alqawarin aurawa ita suka sheda masa cewa yayi haquri yazo yakarb'i kayansa, dayayi yunqurin magantawa gaba d'aya suka had'a masa baki wajen cewa matuqar yasake dakatar dasu akaro nabiyu acikin sha'anin 'yarsa to bazasu sake amsa sunan cewa su qannensa bane, Kuma zasu barmasa gidan suda iyalinsu in yaso yayi yanda yake so, sannan suka fice suka barsa cike da damuwar matakin da 'yan uwan nasa suka d'auka,
Jin da yayi wayarsa naqara yasashi tashi zaune had'e da miqa hannu ya d'auko wayar dake kan kujera, ganin sabuwar lambar da yayi yasa ya maida wayar ya ajiye tare da komawarsa ya kwanta fuskarsa na kallon sama,
Sake kira Rashida tayi akaro na biyu amma har ta tsinke bai d'aga ba sai akaro na uku taji ya d'aga.
Sallama tayi masa a mutunce cikin girmamawa ya amsa sannan tace.
"Sunana barrister Rashida bashar maitakalma, ni haifaffiyar cikin garin kano ce awani qauye da ake kira yarimawa amma yanzu ina zaunene agarin borno ni da mahaifiyata da kuma mahifina da ALLAH yayiwa rasuwa duk anan borno d'in.
Wata zabura Abba yayi daga kwancen da yake had'e da miqewa tsaye yana bin wayar da wani irin kallon tsana kai kace ita d'ince Rashida, jin da yayi taci gaba da magana had'e da cewa "ni..." Yasa yayi saurin dakatar da ita cikin b'acin rai tahanyar cewa.
"Kece uwar wannan yaron da bayada uba, yaron da bayada asali, yaron da duniya tasan rauninsa da rashin nagartarsa, yaron da ba'ada tabbaci akan koshi waye?, Yaron daya nacewa 'yata yake neman lalatata izuwa tahanyar da aka samosa, meye dalilin kirana?, meyasa bazaki jawa yaronki kunnuwaba daya nisanta kansa da 'yatah?, meyasa bazaki lusar dashi cewa wutsiyar raqomi tayiwa qasa nisa?, meyasa amatsayinki na uwa bazaki zaunar dashi kinuna masa banbancin aya da tsakuwa ba?, oh! Wato kinaso yaronki ya zama kiyashi ja abunda yafi qarfinsa saboda son zuciya da sakarci irin naki, me kike so akiraki uwa ko kuma uwar kawai tunda kin kasa banbancewa d'anki tsakanin fari da baqi?, To bari nafad'a maki yayi kuskuren neman aure a inda bai dace da shiba kuma da sannu zan nusar dashi wannan kuskuren da yayi tunda ke kin kasa."
Page___86💎
Komawa yayi akan kujerar kusa da ita ya zauna ahankali yace.
"Gimbiya tah, meya jimaki a goshi?" Yana nuna wajen da yatsa inda yaga filista da hajia mama tasa mata jiya inda goshinta ya fashe.
'Dan shafa wajen tayi had'e dayin murmushi sannan tace.
"Abu sumayya ya kake?"
"A yanzu lafiya klw nake tunda gani gaki."
"Kaga yanda rayuwa ta sauya mana ko, meyasa hakan take faruwa damu, musamman ni da zuciyata gaba d'aya yakasa hango mun kowa sai kai, gashi sai wahala rayuwa ke bamu, mahaifina na matuqar sona, ya kula dani sosai, yabani farinciki fiye da tsammaninka, saidai yakasa karanto zuciyata yafahimci irin tsantsar qaunar da nake yimaka, d'ago kanta tayi tana kallonsa idanuwanta sun cika da hawaye tace.
" _Wish that i spend some time with you only the time where there would be two of us looking at the sky and gazing at the stars, wish that we would just run away from here and run away so far, i was thinking about this the whole day and i just want to say that my love for you is so true, no matter what the hardest time it's i will be thinking of you, when i think about you, my mind goes numb, i am not me, i become so dumb, because our love was so strong, It was to me you belong, then why all this happened, I miss you so much Abu sumayya_"
Kallon cikin kwayar idanuwanta ya dingayi yana karanto tabbacin gaskiyar duk wata kalma da take fad'a, yarasa wane irin so ne takeyi masa haka, yarasa dalilin da yasa ta qaunace haka, tabbas shima ya cancanci yabata dukkanin irin wannan soyayyar da take nuna masa koda hakan na nufin zai rasa farincikinsa da natsuwarsa nahar abada, wani sassanyan murmushi ya sakar mata lokacin data kai qarshen kalamanta had'e da cewa.
"Karki damu gimbiyata, a halin yanzu ina rayuwane wa sonki da qaunarki, nayi maki alqawarin zan iya bada rayuwata domin ceto soyayyarmu, ba ina nufin zanmutu bane akan soyayyarmu ba, Ina nufin na shirya tsaf akan zan fuskanci duk wata matsala ko qalubale don naga na killaceki a inda yakamata, zan rayu don in cika maki duk wasu burikanki da mafarkanki akaina, zan biya soyayyar da kika nuna mani da zallar halacci da kuma karamci don haka kidena damar da kanki, tun asali qaunace ALLAH yasaka tsakanin ni da kuma ke, so ya biyo baya ne kawai, kiyarda dani zan baki duk wata kulawa, zan maye maki farinciki da wannan quncin da kike ciki, zan share maki wud'annan zafafan hawayen na maye maki gurbinsu da sanyayyun hawayen farinciki, Ina so kisa aranki gimbiyata, Abu sumayyanki na sonki kuma yana qaunarki har zuwa fitar lumfashinsa naqarshe,"
Sun jima suna fad'awa junansu kalamai masu dad'i da kuma sanyaya zuciya da suka sake basu qwarin guiwar cewa komai rintsi komai wuya zasu rayune kad'ai idan suna tare a qarqashin inuwa d'aya, ganin lokaci na dad'a ja gashi Rashida tace dole yau yamaidata gida yasa yamiqe yaje kitchen ya d'ibo abinci ya zauna agabanta yana ci.
Cin abincin yakeyi yana kallonta tana yimasa dariya har ya canyesa tas batare daya ankara ba sannan yamaida plate d'in kitchen yadawo inda take yace.
"Gimbiya bari naje na watso ruwa mutafi kafin gwaggo tafito tasameni."
"Shikenan ka kula mani da kanka."
Bayan ya gyara cikin wata farar shaddarsa giznah da tamatuqar yimasa kyau yanufo falon bakinsa d'auke da sallama, tsabar kyawon da yayi batool batasan lokacin da ta sakar masa murmushi tare da cewa, "kamatuqar yin kyau Abu sumayya."
"Nagode oum sumayya." Yafad'a shima yana mayar mata da murmushi, kusan atare Rashida da Fatima suka fito daga cikin d'akunansu Fatima nariqe da makullin motar dasu little zasu tafi da ita tace.
"Har anfito little?."
"Eh mama."
"Ungo to ga makullin motar ubangiji ALLAH ya tsare hanya, don ALLAH akula da titi da kyau kaji?" tamiqa masa tana kallon batool da har lokacin kezaune kanta na aqasa, jitake kamar ta fusa ihu domin gaba d'aya bata buqatar komawa gida saboda abunda zata tarar.
Murmushi tayi had'e da cewa.
"Takwarata tashi kuje lokaci na tafiya kuma don ALLAH kihi haquri kibarwa ALLAH dukkanin lamurransa, kada kikoma yunqurin yin jayayya da mahaifanki domin hakan kuskurene kinji ko.?"
"In Sha ALLAH." Batool tafad'a muryarta na kakkarwa alamun tana so tayi kuka.
Dafata Rashida tayi had'e da cewa.
"Ashsha batool, kukan zaki komawa bayan nafad'a maki cewa kuyi hak'uri, bawa baya iya tab'a canza qaddararsa aduk inda yake don haka kuka bayada wani amfani ga abunda zartar maka dashi za'ayi bakai zaka zartar dashi ba, ungo wannan littafin hisnul Muslim ne, kintab'a amfani dashi.?"
"Eh dashi mamana tayi koyamun addu'o'in safiya da marece.,"
"Masha ALLAH, kiduba cikinsa akwai babin addu'o'in hammu wal hazan, kije ki laqancesu in Sha ALLAH zaki samu sassaucin quncin zuciya dana baqinciki da damuwa kinji ko."
Hannu biyu tasa takarb'a hawaye na zubo mata, Rashida tace.
"Au bazaki dena kukanba." Cikin sake d'aga sautin kukanta tace
"Ina matuqar jin tsorone gwaggo."
Shiru Rashida tayi kafin tace "shikenan, share hawayen naki kibani lambar shi mahaifin naki."
Fad'a mata tayi ta copy digit d'in awayarta sannan tace,
"Maza jiki yana jiranku, Allah yayi maki albarka kuma ya kaiku lafiya."
Amin batool tafad'a sannan tafice tana sharar qwalla, wani gauron nisha Fatima tayi had'e da cewa Rashida.
"Yarinyar nan tabani tausayi, wlh tana matuqar son little sosai, ALLAH yakawo mata d'auki don girman qur'ani,
"Amin." Rashida tafad'a sannan sukabi bayanta, Saida sukaga tashinsu sannan suka dawo cikin gida bayan Rashida ta tabbatarwa da little cewa yakula da batool sosai kuma yaje ahankali.
Kusan awanni biyar suka shafe akan hanya kafin su iso gida, tafiya ce sukayi mai cike da nishad'i da kuma jin dad'i wacce gaba d'aya ta mantar dasu halin da suke ciki saboda yanda suka d'ebawa juna kewa sosai, atarihin rayuwarsu wannan rana itace da bazasu tab'a mantawa da itaba soboda lokacin da suka samu wajen qara bayyanawa juna sirrin dake zuciyarsu.
Rashida kuwa saida ta kwatanta sun kusa isa sannan takira mahaifin batool, lokacin yana kwance gaba d'aya duniya tayi masa zafi saboda neman batool da aka shigayi tun safe ba'a ganta ba, Wanda hakan yasa 'yan uwansa suka fito masa da b'acin ransu qarara akan cewa duk abunda yasamu batool laifinsa ne kuma ALLAH zai kamashi dashi, a matsayinsa na mahaifi bashi kad'ai ALLAH yad'orawa haqqin 'ya'yansa ba, hatta qannensa, yannensa da mahaifiyarta da qannen mahaifiyarta da qannenta duk sunada haqqi akanta don haka sun gaji da zuba masa idanuwa yana neman cilla 'yarsu cikin halaka, ada sunyi tunanin barmasa 'yarsa kamar yanda yake iqirarin cewa 'yarsa ce, Amma ayanzu zasu had'a qarfi da qarfe suyi mata abunda take so, zasu bata zab'in ranta matuqar shine kwanciyar hankalinta koda hakan na nufin zai yakicesu daga jikinsa, sun shirya tsaf wajen nuna masa cewa suma 'yarsu ce kuma zasu bata gatar daya kasa bata ayanzu,
Maganganu masu zafi suka yab'a masa kafin su sake tabbatar masa da cewa zasu je su nemo 'yarsu da kansu amma ya tabbata yazare hannunsa acikin lamurranta don su suna buqatarta idan shi baya buqatarta, baban abunda yafi b'ata masa rai shine a gabansa suka kira wanda yayiwa alqawarin aurawa ita suka sheda masa cewa yayi haquri yazo yakarb'i kayansa, dayayi yunqurin magantawa gaba d'aya suka had'a masa baki wajen cewa matuqar yasake dakatar dasu akaro nabiyu acikin sha'anin 'yarsa to bazasu sake amsa sunan cewa su qannensa bane, Kuma zasu barmasa gidan suda iyalinsu in yaso yayi yanda yake so, sannan suka fice suka barsa cike da damuwar matakin da 'yan uwan nasa suka d'auka,
Jin da yayi wayarsa naqara yasashi tashi zaune had'e da miqa hannu ya d'auko wayar dake kan kujera, ganin sabuwar lambar da yayi yasa ya maida wayar ya ajiye tare da komawarsa ya kwanta fuskarsa na kallon sama,
Sake kira Rashida tayi akaro na biyu amma har ta tsinke bai d'aga ba sai akaro na uku taji ya d'aga.
Sallama tayi masa a mutunce cikin girmamawa ya amsa sannan tace.
"Sunana barrister Rashida bashar maitakalma, ni haifaffiyar cikin garin kano ce awani qauye da ake kira yarimawa amma yanzu ina zaunene agarin borno ni da mahaifiyata da kuma mahifina da ALLAH yayiwa rasuwa duk anan borno d'in.
Wata zabura Abba yayi daga kwancen da yake had'e da miqewa tsaye yana bin wayar da wani irin kallon tsana kai kace ita d'ince Rashida, jin da yayi taci gaba da magana had'e da cewa "ni..." Yasa yayi saurin dakatar da ita cikin b'acin rai tahanyar cewa.
"Kece uwar wannan yaron da bayada uba, yaron da bayada asali, yaron da duniya tasan rauninsa da rashin nagartarsa, yaron da ba'ada tabbaci akan koshi waye?, Yaron daya nacewa 'yata yake neman lalatata izuwa tahanyar da aka samosa, meye dalilin kirana?, meyasa bazaki jawa yaronki kunnuwaba daya nisanta kansa da 'yatah?, meyasa bazaki lusar dashi cewa wutsiyar raqomi tayiwa qasa nisa?, meyasa amatsayinki na uwa bazaki zaunar dashi kinuna masa banbancin aya da tsakuwa ba?, oh! Wato kinaso yaronki ya zama kiyashi ja abunda yafi qarfinsa saboda son zuciya da sakarci irin naki, me kike so akiraki uwa ko kuma uwar kawai tunda kin kasa banbancewa d'anki tsakanin fari da baqi?, To bari nafad'a maki yayi kuskuren neman aure a inda bai dace da shiba kuma da sannu zan nusar dashi wannan kuskuren da yayi tunda ke kin kasa."