Sashe 75
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___56💎
Saida suka gama shaqiyancin su day izgilanci tukuna suka baro wajen,
A hankali Inna Bilkisu ta tako zuwa bakin rumfar d'akinsu suna qoqarin shiga d'aki jikinta a sanyaye tace.
"Ruqayya, Ali kuji tsoron ALLAH, duniyar nan da kuke gani batada tabbas, shin ashe halin da Yaya hawwa take ciki bai isa yazame muna aya da kuma darasi ba?, Karku manta tare da muke zaune da ita acikin gidannan, itama mutumce kamarmu amma ALLAH yajarabci rayuwarta tahanyar komawa a cikin wannan yanayin da take ciki wanda muma bamufi qarfin ALLAH ya jarabcemu fiyema da yanda muke ganinta, I zuwa yanzu ya kamata ace mudukanmu munyi karatun ta natsu, mu zamo tsintsiya mad'aurinmu d'aya duk abunda yasamu d'ayanmu mu d'auka mu yasama kuma mu wa'aztu domin wannan halin da take ciki wlh iznane agaremu."
"To jikanyar limamai, Ina ruwanki meya shafeki da al'amarinmu?, Dama akace maki ke muke tsoro da zakizo kice muji tsoron ALLAH?, Ke nifa bilki bana son sa ido kiyi sha'aninki kibarmu muma muyi namu, yo Ina ruwanmu da halin da take ciki ai haukane ba'agareta farau ba kuma ta cancancesa, wlh Banda ALLAH ya isa tsakaninmu da ita bisa abunda taja akayi mana Babu abunda zamuyi mata, aikin banza in wa'azi kike son yi to jeki kiyi mata ita dake d'auke da haqqoqan mutane akanta take damunmu da kuwace kuwace tana hanamu bacci." Inna ruqayya tafad'a tana harararta, tsaki baffa Ali yaja had'e da juyowa yana kallonta cike da takaici yace.
"Ke Bilki, mufa yanzu babu ruwanmu da al-amarin kowa agidan nan don haka kifita harkarmu, baruwanki da duk abunda zamuyi koda kuwa kafirci ne, kabarinki daban namu daban kinajina ko!" Jinjina kai Inna Bilkisu tashigayi kafin tace
"Wal'iya zubillah, Ali meyakawo wannan zancen, ai _inni laku minnannaasihin (ni kawai agareku mai nasiha ce)_ ubangiji ALLAH kashiryemu kuma yabaku haquri."
Tana gama fad'an haka tajuyawarta tabar wajen tana maijin takaicin halin da suke ciki.
Muneera kam tutse baki tayi tana susar kai tace. "Inna wai meyasa kuke yima Inna Bilkisu haka?, ALLAH tanada kirki kawai don baku gane bane, amma lokacin da kuke rufe wajen 'yan sanda ALLAH duk ita take kula damu tana bamu abinci." A hasale Inna ruqayya tayo kanta tana fad'in
"Ke dallah rufemun baki, akace maki donku takeyi, duk wata maqarqashiyar rufemun da akayi ai da had'in bakinta ita da baffanninku, ai kinga kuwa dole su baku abinci ko don gudun duniya tazagesu."
"Kai Inna, ALLAH ba haka bane, ai mukad'ai ke zaune dasu ina duniyar take balle ta zagesu, kawai kice keda baffana bakwa son gaskiya kuma wlh sai anyi maku irin na inna hawwa idan baku dena ba, ni Babu ruwana, abunda ma nece mata (banqararriyar kaza) wlh da gaske ni haka naga takoma."
Kanta baffa Ali yayi da wani icce dake gefensa tafice da gudu daga gidan tana susar kai...
••• ••• •••
Baba da umma kuwa suna zamansu hankali kwance Babu wanda ke takurasu, gwargwado suna cin mai kyau kuma suna shan maikyau, hakama alhaji naqoqarin ganin ya kyautata masu saboda su samu kwanciyar hankali da natsuwa kuma Alhamdulillah ba laifi sun d'an fara ragewa kansu damuwa, wasu lokutanne kawai take bijiro masu idan suka tuna da 'yarsu sai 'yar matsalar hajia nafeesa dake musgunawa umma tahanyar yawan baqaqen maganganu da tsawar da take yimata duk kuwa da taka tsantsan da takeyi da ita, ga Rashin kunyar da yaranta keyi wanda shike sakesa hajia nafeesa fitina idan aka qiyi masu yanda suke so.
Yauma umma na kitchen tsaye tana jiran albasar data yanka acikin ruwan mai tasoyu sannan tazuba kayan miyan da zata dafa jallof dasu sai ga yaronta d'an shekara goma mai suna Shakur ya shigo, dube dube ya farayi cikin kitchen d'in kafin yace.
"Ke umma zuba mun abinci."
"Yi haquri Shakur abincin bai ida nuna ba."
"Nidai kizuba mun haka zanci."
"A'a bari dai nahad'a maka qanzon nan naturawa (cornflaks) kafin ka qarasa sha nagama kaji ko."
Bubbuga qafa yafarayi zai b'are mata baki da kuka tayi saurin jawo plate ta zuba masa shinkafar data yiwa per boiling gudun kada kukan nasa ya jaxa mata walaqanci awajen mahaifiyarsa,
"Ungo gashi" tafad'a tana miqo masa plate d'in farar shinkafar data zuba man da take soyawa da magi mai star akai yanda zaiji dad'inta ya karb'a yawuce abinsa.
A daidai saman inda dining table ke ajiye yaje ya zauna qafafuwansa na reto a qasa ya fara cin abincinsa hankali kwance ko d'an sauran qarfin shinkafar daya rage tanuna baya ji tunda yunwa yakeji.
Jim kad'an hajia nafeesa tafito cikin wani material mai shegen kyau yasha d'unkin riga bubu waya laqame akunnenta tana takawa d'ai d'ai, da alama wayace takeyi da wata, idanuwa ta qwalalo awaje hango d'an tsakiyar ranta wato Shakur yana cin shinkafar da kallo d'aya zakayi mata kasan Bata dahuba saboda yanda take tsaitsaye, wajensa taqaraso ta d'auke plate d'in dake gabansa tana fad'in.
"Ina zuwa hajia hafsat, zankira daga baya."
"Kai shakur a ina kasamu wannan?."
"Momy a kitchen ne nasamu."
"Waya baka?"
"Umma mai aiki..." Tun kafin yarufe baki tashiga qwallawa umma kira da qarfi, umma najin haka tasan a fusace take.
Tsoron qasqanci da walaqancinta yasa umma fitowa da sauri alokacin da tasake kiranta tana fad'in.
"Na'am hajia, gani."
Jeho mata plate d'in da sauran shinkafar tayi ya bugi goshinta sannan yafad'i qasa duk shinkafar ta wawwatse mata ajiki.
"Har ke waye da zaki bawa yarona abinci gaya babu miya kuma d'anye wanda be nuna ba, ke wace nake tambayarki?" Hajiyar tafad'a a tsawace.
Qasa umma tayi da kanta saboda batajin duk qasqancinta zata iya sa'insa da matar dako sa'ar qanwarta mawiyya batayi ba.
Masifa tashigayi inda taka shiga ba nan take fita ba har tan fad'in umma tadena ganin tagirmeta zata iya zabga mata mari akan yaronta wai so takeyi takashe mata shi shiyasa tabashi d'anyen abinci salon cikinsa ya kumbure masa, cikin fushi tace. "To wlh maza ki tattarata ki kwashe kuma sai kin zauna anan gabana kincinyeta tas kamar yanda kikasa yarona yacita."
Haka tayita masifa da ita har alhaji dake tsaye a harabar gate shida wani abokinsa suna magana yajiyo harshen nata, hakan yasa yayi cikin gidan ransa a d'an b'ace da zimmar yimata magana ya tadda umma durqushe a gabanta tana kakkab'e shinkafar dake jikinta had'e da qoqarin tattara wadda ta zube qasa ita kuma tana tsaye kanta tana faman jijjiga jiki, motsin da taji ya sata juyowa tana kallonsa had'e da cewa.
"Yawwa qwanda daka shigo ka ganewa kanka abunda tayi, irin wannan iskancin da sukeyi kesa kake ganin kamar ina wulaqanta 'yan aiki, farar shinkafa na isko fa taba Shakur ko nina batayi ba salon taja masa wahalar da zata kashesa, musamman idan ta kumbura masa ciki."
"Sai ke kuma kika yimata me?" yatambaya ransa a b'ace."
"Shine da raina yab'aci nawatsa matashi kuma nace ta tattarar dashi ita tacinye."
"Ok. Ni ina wahalar samo abinci ke kina zubarwa qasa, shikenan umma ajiye ki tashi wajen." Yafad'a tare da matsowa wajen ita kuma umma takoma gefe ta makure,
"Duqa ki tsincemun abina tas ki miqomun keda kika watsar dashi." Yace ma hajia nafeesa tare da nufar inda shakur yake zaune.
Sanin halinsa yasa hajia nafeesa duqawa tsince abincin tana hararar umma tana kumbure fuska sai kace wacce aka hurawa mabusa.
Riqo hannun shakur yayi had'e da cewa.
"Shakur d'in baba ya akayi kake cin waccan shinkafar haka?"
"Abba yunwa nakeji kuma umma bata gama abinci ba da nace tazubomun haka sai tace inbari ta had'amun cornflakes shine nace bana so da taga zanyi kuka sai ta zubomun a haka saboda nace zanci."
"Bakasan cin shinkafa have done zata iya kumbura maka ciki ba."
"Abba bazata yimani komai ba yunwa nakeji."
Daidai lokacin hajia nafeesa tagama tsincikke shinkafar tazo tamiqo masa tana faman cika da batsewa,
Murmushi yayi sannan ya karb'a ya ajiyewa Shakur agabansa yace
"Ungo kayi bisimillah ka qarasa canye abinka kaji ko, Amma kada kasake yin haka Babu kyau."
"Alhaji fa yayi qasa." Hajia nafeesa tafada kamar zatayi kuka.
"Eh yaci babu abunda zai yimasa in sha ALLAH, Ina kinsan da haka amma kikace ita tacinye sa ko."
Juyawa yayi yana kallon umma yace.
"Umma kiyi haquri, kuma daga yau bazaki sake yin aiki agidannan ba."
"A'a alhaji kada ayi haka, indai akan wannan ne babu komai zanci gaba dayi, bana son na zaunane waje d'aya, nafi son ind'an dinga mommotsa jikin."
"A'a baza'ayi haka ba, aishi d'an adam daraja ne dashi yakamata ace angirmamashi musamman wanda ya girmeka, walaqanci bayada dad'i ko kad'an don haka kije zanyi magana da hajia fareeda sai ki koma acan b'angarenta inaga zaifi tunda kinfiso kina motsa jikin naki."
"To shikenan alhaji ngd, bari na qarasa wannan girkin."
"A'a umma kibarshi ita zata qarasa da kanta."
Da qarfi hajia nafeesa ta d'ago kai tana kallonsa yayin da umma tafice daga part d'in tana godiya ga ALLAH daya kawo alhaji ya kub'utar da ita daga cin mutuncin da tayi niyar yimata kuma ya yaye mata damuwar zama da ita da kalolin walaqanci da cin kashin da takeyi mata.
Jinjina mata kai yayi idanuwansa acikin nata alamun da gaske yakeyi sannan yace. "Kuma ba wannan girkin kad'ai zaki ida da kanki ba, daga yau nayi maki alqawarin babu wata macce da zata koma zama part d'inki da sunan yi maki aiki har sai lokacin da kika canza kuma kika san darajar mutane, don haka ya rage wajenki kidafawa kanki da yaranki abinci ko karki dafa duka ruwanki, wannan shine hukuncin dana yanke akai, idan kuma kikak'i ji to wlh kinji na rantse bakyaqi gani ba.
Yana gama fad'ar haka ya juyawarsa ya fice, dama tuntuni yake son d'aukar mata mataki akan cin zarafin da take yiwa bayin ALLAHn dake qarqashinta ALLAH bai bashi iko ba sai yau.
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___56💎
Saida suka gama shaqiyancin su day izgilanci tukuna suka baro wajen,
A hankali Inna Bilkisu ta tako zuwa bakin rumfar d'akinsu suna qoqarin shiga d'aki jikinta a sanyaye tace.
"Ruqayya, Ali kuji tsoron ALLAH, duniyar nan da kuke gani batada tabbas, shin ashe halin da Yaya hawwa take ciki bai isa yazame muna aya da kuma darasi ba?, Karku manta tare da muke zaune da ita acikin gidannan, itama mutumce kamarmu amma ALLAH yajarabci rayuwarta tahanyar komawa a cikin wannan yanayin da take ciki wanda muma bamufi qarfin ALLAH ya jarabcemu fiyema da yanda muke ganinta, I zuwa yanzu ya kamata ace mudukanmu munyi karatun ta natsu, mu zamo tsintsiya mad'aurinmu d'aya duk abunda yasamu d'ayanmu mu d'auka mu yasama kuma mu wa'aztu domin wannan halin da take ciki wlh iznane agaremu."
"To jikanyar limamai, Ina ruwanki meya shafeki da al'amarinmu?, Dama akace maki ke muke tsoro da zakizo kice muji tsoron ALLAH?, Ke nifa bilki bana son sa ido kiyi sha'aninki kibarmu muma muyi namu, yo Ina ruwanmu da halin da take ciki ai haukane ba'agareta farau ba kuma ta cancancesa, wlh Banda ALLAH ya isa tsakaninmu da ita bisa abunda taja akayi mana Babu abunda zamuyi mata, aikin banza in wa'azi kike son yi to jeki kiyi mata ita dake d'auke da haqqoqan mutane akanta take damunmu da kuwace kuwace tana hanamu bacci." Inna ruqayya tafad'a tana harararta, tsaki baffa Ali yaja had'e da juyowa yana kallonta cike da takaici yace.
"Ke Bilki, mufa yanzu babu ruwanmu da al-amarin kowa agidan nan don haka kifita harkarmu, baruwanki da duk abunda zamuyi koda kuwa kafirci ne, kabarinki daban namu daban kinajina ko!" Jinjina kai Inna Bilkisu tashigayi kafin tace
"Wal'iya zubillah, Ali meyakawo wannan zancen, ai _inni laku minnannaasihin (ni kawai agareku mai nasiha ce)_ ubangiji ALLAH kashiryemu kuma yabaku haquri."
Tana gama fad'an haka tajuyawarta tabar wajen tana maijin takaicin halin da suke ciki.
Muneera kam tutse baki tayi tana susar kai tace. "Inna wai meyasa kuke yima Inna Bilkisu haka?, ALLAH tanada kirki kawai don baku gane bane, amma lokacin da kuke rufe wajen 'yan sanda ALLAH duk ita take kula damu tana bamu abinci." A hasale Inna ruqayya tayo kanta tana fad'in
"Ke dallah rufemun baki, akace maki donku takeyi, duk wata maqarqashiyar rufemun da akayi ai da had'in bakinta ita da baffanninku, ai kinga kuwa dole su baku abinci ko don gudun duniya tazagesu."
"Kai Inna, ALLAH ba haka bane, ai mukad'ai ke zaune dasu ina duniyar take balle ta zagesu, kawai kice keda baffana bakwa son gaskiya kuma wlh sai anyi maku irin na inna hawwa idan baku dena ba, ni Babu ruwana, abunda ma nece mata (banqararriyar kaza) wlh da gaske ni haka naga takoma."
Kanta baffa Ali yayi da wani icce dake gefensa tafice da gudu daga gidan tana susar kai...
••• ••• •••
Baba da umma kuwa suna zamansu hankali kwance Babu wanda ke takurasu, gwargwado suna cin mai kyau kuma suna shan maikyau, hakama alhaji naqoqarin ganin ya kyautata masu saboda su samu kwanciyar hankali da natsuwa kuma Alhamdulillah ba laifi sun d'an fara ragewa kansu damuwa, wasu lokutanne kawai take bijiro masu idan suka tuna da 'yarsu sai 'yar matsalar hajia nafeesa dake musgunawa umma tahanyar yawan baqaqen maganganu da tsawar da take yimata duk kuwa da taka tsantsan da takeyi da ita, ga Rashin kunyar da yaranta keyi wanda shike sakesa hajia nafeesa fitina idan aka qiyi masu yanda suke so.
Yauma umma na kitchen tsaye tana jiran albasar data yanka acikin ruwan mai tasoyu sannan tazuba kayan miyan da zata dafa jallof dasu sai ga yaronta d'an shekara goma mai suna Shakur ya shigo, dube dube ya farayi cikin kitchen d'in kafin yace.
"Ke umma zuba mun abinci."
"Yi haquri Shakur abincin bai ida nuna ba."
"Nidai kizuba mun haka zanci."
"A'a bari dai nahad'a maka qanzon nan naturawa (cornflaks) kafin ka qarasa sha nagama kaji ko."
Bubbuga qafa yafarayi zai b'are mata baki da kuka tayi saurin jawo plate ta zuba masa shinkafar data yiwa per boiling gudun kada kukan nasa ya jaxa mata walaqanci awajen mahaifiyarsa,
"Ungo gashi" tafad'a tana miqo masa plate d'in farar shinkafar data zuba man da take soyawa da magi mai star akai yanda zaiji dad'inta ya karb'a yawuce abinsa.
A daidai saman inda dining table ke ajiye yaje ya zauna qafafuwansa na reto a qasa ya fara cin abincinsa hankali kwance ko d'an sauran qarfin shinkafar daya rage tanuna baya ji tunda yunwa yakeji.
Jim kad'an hajia nafeesa tafito cikin wani material mai shegen kyau yasha d'unkin riga bubu waya laqame akunnenta tana takawa d'ai d'ai, da alama wayace takeyi da wata, idanuwa ta qwalalo awaje hango d'an tsakiyar ranta wato Shakur yana cin shinkafar da kallo d'aya zakayi mata kasan Bata dahuba saboda yanda take tsaitsaye, wajensa taqaraso ta d'auke plate d'in dake gabansa tana fad'in.
"Ina zuwa hajia hafsat, zankira daga baya."
"Kai shakur a ina kasamu wannan?."
"Momy a kitchen ne nasamu."
"Waya baka?"
"Umma mai aiki..." Tun kafin yarufe baki tashiga qwallawa umma kira da qarfi, umma najin haka tasan a fusace take.
Tsoron qasqanci da walaqancinta yasa umma fitowa da sauri alokacin da tasake kiranta tana fad'in.
"Na'am hajia, gani."
Jeho mata plate d'in da sauran shinkafar tayi ya bugi goshinta sannan yafad'i qasa duk shinkafar ta wawwatse mata ajiki.
"Har ke waye da zaki bawa yarona abinci gaya babu miya kuma d'anye wanda be nuna ba, ke wace nake tambayarki?" Hajiyar tafad'a a tsawace.
Qasa umma tayi da kanta saboda batajin duk qasqancinta zata iya sa'insa da matar dako sa'ar qanwarta mawiyya batayi ba.
Masifa tashigayi inda taka shiga ba nan take fita ba har tan fad'in umma tadena ganin tagirmeta zata iya zabga mata mari akan yaronta wai so takeyi takashe mata shi shiyasa tabashi d'anyen abinci salon cikinsa ya kumbure masa, cikin fushi tace. "To wlh maza ki tattarata ki kwashe kuma sai kin zauna anan gabana kincinyeta tas kamar yanda kikasa yarona yacita."
Haka tayita masifa da ita har alhaji dake tsaye a harabar gate shida wani abokinsa suna magana yajiyo harshen nata, hakan yasa yayi cikin gidan ransa a d'an b'ace da zimmar yimata magana ya tadda umma durqushe a gabanta tana kakkab'e shinkafar dake jikinta had'e da qoqarin tattara wadda ta zube qasa ita kuma tana tsaye kanta tana faman jijjiga jiki, motsin da taji ya sata juyowa tana kallonsa had'e da cewa.
"Yawwa qwanda daka shigo ka ganewa kanka abunda tayi, irin wannan iskancin da sukeyi kesa kake ganin kamar ina wulaqanta 'yan aiki, farar shinkafa na isko fa taba Shakur ko nina batayi ba salon taja masa wahalar da zata kashesa, musamman idan ta kumbura masa ciki."
"Sai ke kuma kika yimata me?" yatambaya ransa a b'ace."
"Shine da raina yab'aci nawatsa matashi kuma nace ta tattarar dashi ita tacinye."
"Ok. Ni ina wahalar samo abinci ke kina zubarwa qasa, shikenan umma ajiye ki tashi wajen." Yafad'a tare da matsowa wajen ita kuma umma takoma gefe ta makure,
"Duqa ki tsincemun abina tas ki miqomun keda kika watsar dashi." Yace ma hajia nafeesa tare da nufar inda shakur yake zaune.
Sanin halinsa yasa hajia nafeesa duqawa tsince abincin tana hararar umma tana kumbure fuska sai kace wacce aka hurawa mabusa.
Riqo hannun shakur yayi had'e da cewa.
"Shakur d'in baba ya akayi kake cin waccan shinkafar haka?"
"Abba yunwa nakeji kuma umma bata gama abinci ba da nace tazubomun haka sai tace inbari ta had'amun cornflakes shine nace bana so da taga zanyi kuka sai ta zubomun a haka saboda nace zanci."
"Bakasan cin shinkafa have done zata iya kumbura maka ciki ba."
"Abba bazata yimani komai ba yunwa nakeji."
Daidai lokacin hajia nafeesa tagama tsincikke shinkafar tazo tamiqo masa tana faman cika da batsewa,
Murmushi yayi sannan ya karb'a ya ajiyewa Shakur agabansa yace
"Ungo kayi bisimillah ka qarasa canye abinka kaji ko, Amma kada kasake yin haka Babu kyau."
"Alhaji fa yayi qasa." Hajia nafeesa tafada kamar zatayi kuka.
"Eh yaci babu abunda zai yimasa in sha ALLAH, Ina kinsan da haka amma kikace ita tacinye sa ko."
Juyawa yayi yana kallon umma yace.
"Umma kiyi haquri, kuma daga yau bazaki sake yin aiki agidannan ba."
"A'a alhaji kada ayi haka, indai akan wannan ne babu komai zanci gaba dayi, bana son na zaunane waje d'aya, nafi son ind'an dinga mommotsa jikin."
"A'a baza'ayi haka ba, aishi d'an adam daraja ne dashi yakamata ace angirmamashi musamman wanda ya girmeka, walaqanci bayada dad'i ko kad'an don haka kije zanyi magana da hajia fareeda sai ki koma acan b'angarenta inaga zaifi tunda kinfiso kina motsa jikin naki."
"To shikenan alhaji ngd, bari na qarasa wannan girkin."
"A'a umma kibarshi ita zata qarasa da kanta."
Da qarfi hajia nafeesa ta d'ago kai tana kallonsa yayin da umma tafice daga part d'in tana godiya ga ALLAH daya kawo alhaji ya kub'utar da ita daga cin mutuncin da tayi niyar yimata kuma ya yaye mata damuwar zama da ita da kalolin walaqanci da cin kashin da takeyi mata.
Jinjina mata kai yayi idanuwansa acikin nata alamun da gaske yakeyi sannan yace. "Kuma ba wannan girkin kad'ai zaki ida da kanki ba, daga yau nayi maki alqawarin babu wata macce da zata koma zama part d'inki da sunan yi maki aiki har sai lokacin da kika canza kuma kika san darajar mutane, don haka ya rage wajenki kidafawa kanki da yaranki abinci ko karki dafa duka ruwanki, wannan shine hukuncin dana yanke akai, idan kuma kikak'i ji to wlh kinji na rantse bakyaqi gani ba.
Yana gama fad'ar haka ya juyawarsa ya fice, dama tuntuni yake son d'aukar mata mataki akan cin zarafin da take yiwa bayin ALLAHn dake qarqashinta ALLAH bai bashi iko ba sai yau.
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋