← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 160

Sashe 40

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___29💎

Bayan tagama tayi gyatsa had'e dayin hamma sannan yace.

"Habiby bacci?"

"Kuma?" Yafad'a yana kallonta, kashe electric d'in tayi sannan tajuyo ta d'ora kanta saman qirjinsa tana sake sakin wata hammar akaro na biyu ta sake cewa."bacci nakeji."

Muje nima shi nakeji, Nuraddeen yafad'a tare da sunkutarta yanufi d'aki da ita, cikin muryar dake nuna baccin takeji sosai tace. "Habiby jiyafa tsoro aka bani a falon nan!."

"Kamarya habibty, tsoro anan falon Kuma? to sai Kikayi qaqa." Yafad'a tare da direta saman gadon, Saida tasaki wata hammar sannan tace. "Addu'a nayi."

"Shine baku tasheni ba yafad'a yana kwanciya bayanta tare da jawo masu mayafin lullubinsu ya lullub'esu, cikin nauyin baccin dake d'ibarsa take basa labari shikuma yana isar da saqonsa ba tare daya fahimci sauran abubun da take fad'a masa ba har ya cimma burinsa, gyara kwanciyarta tayi yace. "Yihaquri Bari muyi wanka tukuna saikiyi baccinki" daqyar yasamu ta tashi suka tsarkakikke jikinsu sannan suka koma sukayi kwanciyarsu.

Kamar yanda Nuraddeen ya fad'a haka akayi, ya sanarwa baffa da cewa ya samoma Rashida maganin macijin ciki dana basir take fama dasu, da baffa yasamo yazo ya gyarasu Inna Bilkisu na gefe tana gyaran ayarta ya miqo mata, "ungo maganin nan ki kaiwa yarinyar nan Rashida tun shekaranjiya Nuraddeen yafad'amun tana fama da matsalar macijin ciki da basir asamo mata, to bansamu shiga dajin ba sai yau, wannan ganyen dafashi zatayi tasha, shi kuma wannan sassaqen ta dakesa sai tarinqa sha tare da hura ko kunu, yarane basuda aiki sai cin maiqo ALLAH dai ya kyauta."

Dariya tafaryi had'e da cewa, "yanzu shi nuran yafad'a maka cewa tana fama da basir da macijin ciki?"

"Haka yace mun mana tunda tana yawan bacci da cin abinci sosai bini bini yace taji yunwa, ai kinga wud'an matsalolin ke damunta ko kuwa.?"

"Ikon ALLAH, malan kenan sake dai tunani, ai akwai d'ayansu dake iya haifar da irin wud'an matsalolin koma fiye dasu, be cemaka yaga tana haskeba ka had'o mata da maganin shawarah ba?" Inna Bilkisu taqarasa maganar dariya na kuccikke mata cike da mamakin Nuraddeen daya kasa gane matarsa nada ciki, kodon yaga ALLAH yabata lafiyayyene, shiru baffa Usman yayi na tsawon mintota kafin yagano inda zancen Inna Bilkisun ya nufa, murmushi yayi irin nasu na manya sannan yace. "To.to..to haka ankayi? Masha ALLAH, ubangiji ALLAH ya inganta, ja'iri zaisa in tafkawa kaina b'arna."

"Ai kuwa dai, Ina ruwan malan Nuraddeen, to bai d'au hannu ba shiyasa." Tafad'a tana dariya.

Daidai lokacin Nuraddeen yafito sashensa yayo inda Inna Bilkisu take a hirgitse,

"Inna Bilki Rashida ce ba lafiya tun jiya da daddare take fama da zazzabi mai zafi yanzu haka gata can sai amai take faman yi ko za'a kaita asibiti ne?" Kallonsa baffa Usman yayi had'e dayin murmushi cikin xolaya yace. "To ko dai macijin cikinne yataso mata Nuraddeen?"

"A'a inaga dai wannan karon qila shawara ce ko?" Inna Bilkisu tafad'a tana kallonsa, "Inna Bilki inaga itace ko akwai sauran maganin da baffa ya d'ebowa fadeela kwanakki abata har zuwa anjima inga ko zamu samo aron mota muje asibiti..."

Bai qarasa ba Inna Bilkisu tace "Kai don ALLAH rufemun baki, ba don dai nasan kayi boko ba da nace maka takkwali kuma Mai qaton kai" tana gama fad'a tanufi sashen nasa baffa Usman na dariya ya shige d'aki suka barshi tsaye yana bitar kalaman Inna Bilkisu, can ya zaro idanuwa cike da mamaki har yana rufe baki yabi bayanta da sauri don samun qarin bayani cike da jin dad'i.

Kwance ta iskota saman kujera mai zaman mutum uku cikin bargo sai rawar sanyi takeyi, sannu tayi mata sannan tajuyo ta kallesa tana fad'in, "yanzu kai Nuraddeen kan shirin zama baba amma har yanzu akwai wauta atare da kai, tana cikin wannan hali tun jiya ko ince kwanakin baya amma ka kasa kaita koda nan chemest ce adubata sai kira mata basir da macijin ciki kakeyi?"

Cikin jin kunya yashiga sosa k'eyar kansa yana sissinne kansa qasa, murmushi tayi kafin suga Rashida tamiqe tayi waje da gudu da d'an sauran qarfin da take dashi, da sauri yaje ya kamata tana kwarara amai tamkar zata amaye hanjinta, ji yakeyi kamar yayi kuka ko ya maido da ciwon ajikinsa saboda tsantsar tausayinta, rungumota yayi gaba d'aya ajiki yana zuba mata sannu jikinta duk yayi yaushi, ruwan daya ajiye gefe abokiti ya d'iba ya wanke mata bakinta sannan ya d'agota tamkar 'yar baby ya maidota d'aki tana sakin lumfashi da qyar, gaba d'aya ya mance da zancen Inna Bilkisu awajen sai daya gama gyara wajen yakoma cikin d'akin tace.

"Idan akwai 'yan ruwan zafi ka d'ebo mata ka lallab'ata tasha ko kad'anne in sha ALLAH Aman zai tsaya, bari naje nadubo maqwabcinnan namu idan motarsa nanan kayi masa magana kuje asibit, sannu Rashida sai hanquri Kuma yanzu har lokacin da ALLAH yarabaku dashi lafiya, ALLAH ya inganta kuma yaqara sauki."
Tana gama fad'a bata jira me zaice ba tafito tazari hijab d'inta, baffa Usman ta tarar bakin gida zaune ta sanar dashi halin da ake ciki, cikin sa'a mutumen nana yajawo motar Inna Bilkisu ta taimaka masa aka fito da Rashida, har zata bisu baffa Usman yace a'a tadawo taje can cikin gida ta sanar masu da halin da ake ciki, su kuma yace su wuce idan akwai buqatar wani yazo to yakira sai Inna Bilkisu tabiyosu a baya tunda nan cikin garine ba nesa ba.

Suna isa nan take aka d'ebi jininta don ayo mata gwajin ciki bayan an bata taimakon gaggawa irin nasu na qauye, tashin farko ana aunawa a kaga tana d'auke da ciki har na tsawon wata hud'u da sati d'aya, duk da Nuraddeen yasan da haka tun gida da Inna Bilkisu tafad'a masa Amma bai gasgata hakan ba sai yanzu da likita ya tabbatar masa, tsabar farinciki ji yakeyi yau tamkar ya take kan jariri sai faman washe haqora yakeyi yana yiwa yiwa likita godiya, likita kam abun har dariya ya soma bashi ganin yanda gaba d'aya murna da farinciki suka rud'ar dashi,.
Girgiza kai yayi yana dariya yace "malan Nuraddeen wanna irin farinciki haka inaga haihuwar farko ce za'ayi maka ko?" Murmushi yayi yana sosa kai likitan yaci gaba da cewa

"Ahhh.. Masha ALLAH Ina tayaka murnar zama fresh baba, ALLAH ya inganta."

"Amin Dr. nagode sosai" Nuraddeen yafad'a yana miqa masa hannu cike da farinciki.

Takardar magani da ruwan da za'a qara mata da allurai ya miqa masa yana fad'in. "Amma zakuyi haquri zuwa nan da anjima koda za'a sallameku don tana buqatar qarin ruwa sosai, ALLAH yaqara sauqi"

"Amin Dr mungode" Nuraddeen yafad'a tare da ficewa daga cikin d'an office d'in nasa.
A can gida kuwa koda Inna Bilkisu ta sanarwa da Yaya hawwa dasu Inna ruqayya babu wacce ta nuna tadamu acikinsu don duk a tunaninsu aikin bokansu ne yafara aiki, tana fita sashen Yaya hawwa ta kece da dariya tana fad'in. "Wani aikin sai malan bakada imani, ba kince ke taurin kaiba yarinya, anturo maki su mutsibbata da janjabilu su tsorataki yanda bazaki iya zama a d'akin ba sunce kinfi qarfinsu, anturo maki ashiq ya shiga jikinki amma yayi duk shawaginsa da dubarunsa shima ya kasa, na dasa na binne don ashiga tsakaninki da d'ana ya dakeki muhuta duka shima mun kasa nasara saboda baqin naci irin naki, shiyasa nace ayi maki mai kankat aturo maki mugun ciwon da zaisa kidinga wari kina sakin quraje dole ko baiso ya gujeki, kuma da dukkan alamu malan bakada imani yasa munyi nasara a kanki wannan karo, shegiya tsigitsila sai kinbar gidannan tunda bana ubanki bane, ba inda zanje ALLAH ma yasa kimutu.
Haka kuwa akayi har marece yayi aka sallamota babu wanda yatafi daga cikinsu inba baffa Usman dasu Aysha da fadeela ba saboda Inna Bilkisu ta tsaya yin girki da gyara gidan sai Kuma yusuf d'an baffa Ali,
Allah sarki baffa duk ji yayi ba dad'i da aka sanar dashi halin da take ciki, yaso ace lafiya take da babu abunda zai hanashi kai jiki asibitin, duk da yanzu sanadiyar addu'ar data bashi yanayi wata ran kuma tayi masa ko kuma baffa Usman yayi masa yafara samun sauqi sosai, Yaya hawwa kuwa sai yakwan biyu baiga ko qwayar idanuwanta ba, Inka gata tazo wajensa to wasu tarako cikin 'yan uwa dake zuwa dubasa ko intake karb'ar kud'in da zatayi abincin da zataci duk da kuwa ko yaushe Rashida na kai mata idan tayi.
Addu'a yayi mata sosai akan ALLAH yabata lafiya yanajin wata irin qaunarta na ratsa zuciyarsa musamman ma da akayi masa albishir tana d'auke da juna biyu, sai yaji kamar ya taka saboda tsantsar farinciki, nan yasa aka kira masa Nuraddeen yace kada yasake yafad'awa kowa cewa tanada juna biyu koda mahaifiyarsa ce har sai cikin yafito, haka ma Inna Bilkisu da baffa Usman duk ya roqesu su b'oye wannan sirrin na jikansa domin komai zai iya faruwa dashi idan har wani abun ya Sami yarinyar da abunda ke cikinta. Baffa Usman dama ba mutumne mai surutu ba ita kuma Inna Bilkisu tafi kowa son a b'oye zancen cikin gudun kada acutar da ita.

Bayan an sallamosu sun dawo gida baffa yasa su baffa Usman suka riqasa yaje har d'akinta yayi mata ya jiki, akunya ce ta amsa yayi mata addu'a tare da gargad'inta akan cikin sannan suka mai dashi, yanda take d'an miqewa yana d'an aza qafafuwansa a qasa shi zaisa kana kallonsa kasan ya samu sauqi sab'anin da dako tashi tsaye baya iyayi balle har ya iya aza qafafuwansa a qasa, dudduqe yake kuma bai iya miqewa tsaye koda an riqasa, Amma yanzu cikin yardar ALLAH yana miqewa yayi tafiya idan anriqasa saidai baya aza qafafuwan da kyau ya taka qasa shiyasa mutanen gidan keta kallonsa cike da mamaki suna jero masa sannu.
Chapter 40 · 0% Book details