Sashe 112
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kowanensu yi yayi tamkar bai lura ba har suka gama gaisawa sannan suka fita, tambayar kansa ya shigayi wanene wancan yaron to?, me sukazoyi a gidan?, Kardai ace sun kashe macijine basu sare kansa ba!, Idan kuwa hakane duk d'aukar fansarsu tazamo ta banza domin bahaka suke buqata ba, yafiso labarin nura harma da tarihinsa su shafe adoron qasa tayanda mahaifinsa zaifi jin rad'ad'i aransa.
Saida sukayi sallar magrib sannan baba balarabe da little suka wuce bayan sunje can gidan baffa sun gaisa da nusaiba kuma little yaga qannen mahaifinsa, itama konkad'an basu bayyana mata kowaye little ba duk da yasaki jiki suna fira da ita da yaran sosai Amma kasancewar Bata san Nuraddeen ba balle Rashida yasa bata gano komai ba,
Little da baffa kuwa ji sukayi tamkar garsu rabu aranar saboda wata irin sabuwar soyayyar junansu da sukeji na taso masu.
Haka little wanda gaba d'aya yanzu ya maida sunansa Abu sumayya saboda soyayyar batul d'insa da yake dako azuciyarsa yaci gaba dayin rayuwarsa cikin jin dad'i, yana matuqar taimakawa kakannin nasa guda biyu aduk lokacin da yasamu dama, haka tab'angaren karatunsa yana maida hankali sosai duk da kuwa akwai wud'anda suka fishi qoqari tare da jajircewa hakan bai hanasa qasa a guiwa ba yana iya qoqarinsa na ganin shima yasamu abunda yasamu koda bai kaisu ba, har baya son hutu ya qare saboda farincikin da yake samu awajen kakan nasa, haka ya kammala shekarun karatunsa hud'u a tsakanin b'oyayyiyar gaskiyar da sukayi alqawarin b'oyewa a tsakaninsu har zuwa ranar da gaskiya zata bayyana, Kuma yayi nasara samun kyakkyawan sakamako a mataki na biyu wato second class..
A ranar daya amshi saka makon jarabawarsa aranar yaquduri aniyar zuwa gidansu batool domin ya gabatar da kansa awajen mahaifinta bayan yanemo izini da kuma sa albarkar mahaifiyarsa kamar yanda ta alqawarta masa, Kuma ysha alwashin koda za'a rabasa da rayuwarsa aranar sai ya tabbatarwa da batool cewa shi d'in nata ne ita kad'ai kuma ita kad'ai ya tanadawa zuciyarsa da kuma gangar jikinsa...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
_Awannan gab'ar alqalamina bazai iya cigaba da rubutu ba har sai ya miqo saqon gaisuwa tare da jinjina had'e da fatan alkhairi agareku, *AUNTY MAIJIDDA MUSA* da kuma *AUNTY FAREEDA MUHAMMAD ABBAS* Bisa zallar karamci, k'auna da kuma halacci da kuka nuna mani wajen jajircewa bibiyar wannan littafi nawa duk da kuwa irin tafiyar hawainiyar da yakeyi hakan baisa kuka nuna qosawa ko kuma gazawarku ba, kun qara mani qwarin guiwa tare da addu'o'in fatan alkhairi agareni da sukasani himmatu da kuma samun quwwar cigaba da rubuto wannan littafin cikin nasara, Ina yimaku addu'ar dukkanin alkhairan ALLAH su lullub'eku tare da ahalinku, nagode sosai da samun goyan bayanku acikin kowane rubutu nawa, ubangiji ALLAH yatsare mani ku kuma yakula mani daku aduk inda kuke👏, Fillah! akoda yaushe zuciyata na matuqar yabawa d'imbin karamci irin naku tare da yimaku son so na har abada😍_
Page___83💎
Tana fad'in "Abu sumayya!" Cike da kokwanto hakan aranta har ta qarso da gudu bakin gate d'in, daidai lokacin ya aza qafarsa zai fita taja wani irin burki had'e da tsayawa tana fidda lumfashi d'aya bayan d'aya saboda gudun da tayi.
Cikin wani irin salo takira sunansa tace.
"Abuu.. sumay..yaaa."
Cak ya tsaya da qafarsa had'e da lumshe idanuwa jin dirar sautin muryarta da yanda takira sunan acikin kunnuwansa, a hankali yajuyo da duka gangar jikinsa izuwa gareta suna fuskantar juna, lokaci d'aya idanuwansu suka sarqe suna isar masu da wani saqo dake fassara tsantsar soyayya da adadin kewar da suka yiwa junansa,
Wata irin dariya had'e da kukan farinciki taji sun kucce mata alokaci d'aya ta durqushe agabansa saboda qafafuwanta da taji na gagarar imata tace,
"Wannan wace irin bazatace mai cike da burgewa da kuma qayatarwa Abu sumayya?, Ka qaraso izuwa gareni kafin tsantsar farinciki yasa lumfashina d'aukewa."
Taqarasa maganar tare dasa hannuwanta ta rufe bakinta hawayen farinci na zubo mata a fuska, nad'e hannuwansa yayi akan qirjinsa yana kallonta yana murmushi, duk da ayanayin da ya ganta baiyi masa dad'i ba Amma farincikin ganinta yasa yakasa matsawa kusa da ita saboda nauyin da qafafuwansa suka yimasa, sunfi mintuna biyu ahaka kafi yafara takowa izuwa gareta yana cewa.
"Haba gimbiyar Abu sumayya! Wannan kukan da kikeyi ai saikisa hawayen dake zubowa daga idanuwanki su narkarmun da zuciya, kitashi mana na kalleki da kyau naga ko kin kula mani da kanki kamar yanda kika alqawarta mani kinji 'yan matanaaaa..." Yaja qarshen cikin wani salon sigar lallashi da yasa batasan lokacin data saki dariya ba had'e da miqewa tana rufe fuska.
"Sannu da zuwa annurin zuciyata, farincikina kuma uban 'ya'yanah." tafad'a cikin murmushi tana jifarsa da wani kallo mai cike da tarin ma'anoni kala kala.
Tsabar jin dad'in kalaman da yaji na fito daga bakinta ya sashi d'aga kansa yana murmushi tare da kallon fitillun da suka haskaka harabar gidan, gyara tsayuwarsa yayi idanuwansa na akan fuskarta yana kallonta sanna yace.
"Yawwa uwar 'ya'yana, makullin zuciyata da kuma mabud'inta, Ina fatar dai nasameki cikin amincin ALLAH da kuma yardarsa."
"Sosai kuwa, domin badon amincin ALLAH dake tare dani ba da tuni kewarka da rashinka sun kaini kushewata."
Saida yayi dariya sannan ya d'ago kai yana kallonta yace.
"Godiya ta tabbata agaresa daya tsare mani ke daga zuwa kushe don tseratar da rayuwar Abu sumayya daga fad'awa gararin duniya nahar abada, ya kike gimbiyata?.
"Ina lafiya yanzu tunda gani ga ka kuma."
"Alhamdulillah, nayi farinciki sosai duk da dai naga kamar kinyi k'wabron kula mani da kanki, Ina fatar akwai banbancin kulawar da ajiyar dana baki acikin zuciyarki."
"Babu buqatar tabbatar maka da hakan domin ance labarin zuciya atambayi fuska, ai tsantsar kula da ajiyar kane dake cikin zuciyata ya haifarwa da gangar jikina shiga cikin wannan hali, kaine kawai na shiga taraddadin cewa ka kula mani da tawa ajiyar ko kuwa?."
"Haba 'yan mata!, Ai wanzuwata awannan lokacin tare dake shine zai baki tabbacin cewa naba ajiyarki cikakkiyar kulawa, Alhamdulillah yau na karb'i sakamakon dake tabbatar da na kammala karatuna bayan adadin shekaru hud'u dana d'auka inayi cike da tarairayar qaunarki acikin zuciyata, hakan yasa na gaggauta dawowa agareki adaidai wannan lokacin da zimmar zamowa mijinki ke kuma mata kamar yanda na d'aukar maki alwashi, inafatar zaki amsheni hannu biyu ki maidani a gurbin da tun farko kika bani."
"Kash!..a gaskiya bazaka samu hakan ba domin na dad'e da cireka a wannan gurbin."
Tafad'a cike da zolayarsa tare da d'aure fuska ta juyar da kanta gefe, cikin fad'uwar gaba ya koma ta gefen data maida kanta yana kallonta.
"Kamarya! Ban fahimceki ba gimbiya?, Wai kina nufin kin d'aukeni daga wannan gurbin kin bawa wani.. how? " yafad'a yana tsareta da idanuwansa da suka soma canza kala.
Kwashewa tayi da dariya harda tafa hannuwa tana nunasa, sake d'aure fuska yayi yana binta da wani irin kallo da yasa dole ta tsaida dariyar had'e da cewa.
"Afuwan Abu sumayya!, Ba haka nake nufiba, taya kake tsammanin zan iya cireka ga wuri har in aza wani?, Wannan abune da bazai yuyuba kama dena tunanin hakan."
"Taya tunanina bazai bani hakan ba bayan da bakinki kikace.."
"Don ALLAH kayi haquri da wasa nakeyi.."
Kafeta yayi da idanuwa kafin yayi wata irin ajiyar zuciya ya juya mata baya.
"Pls kayi haquri mana.."
"Em'ehm..ni nayi fushi, dama d'azun kin b'atan rai da kikace natafi bakya buqatar ganina, sonki ne da yayi mun yawa yasa na iya dawowa garemu da kika fito"
"Wayyo...kayi haquri mana, plsss..."
Tafad'a tare da komawa gabansa tariqe kunnuwa,
Dariya ya saki sannan yace.
"Shikenan nahaqura, bari natafi dare ya somayi."
Nan take kamannin fuskarta suka sauya daga farinciki zuwa damuwa.
"Meye gimbiya?"
"Bana son katafi Abu sumayya, gaba d'aya shekarunnan hud'u a jigace na qarar dasu saboda rashinka da kuma ganinka, ka qaramun lokaci mana ko hasken daya d'iga azuciyata zai qara yawan da zai haskamun yau zuwa gobena."
"Kamar ya gimbiya?, So kikeyi na kwana anan ne? Ko bakiga lokaci naqara qurewa bane?"
Saida ya duba agogon dake hannunsa sannan yace.
"Kin gafa har goma da rabi takusa, gashi akwai nisa da inda zanje gidan baffan mamana, in dai akaina ne ki kwantar da hankalinki yanzu kullum muna tare kinji ko?"
"Ka kasa fahimtata ne, Taya hakan zai faru abbana na nema ya aura mani duk wanda yaga dama naqi amincewa, sanadiyar hakan ya sanya mani tsauraran matakai,"
"To kinga ya kamata ace natafi yanzu kamin ya sameni, na tabbata ko yanzu don baya gida shiyasa muka samu wannan damar, don haka kiyi haquri kinji ko?"
'Daga masa kai tayi idanuwanta na tsiyayar da hawaye yacire hankacif daga cikin aljihunsa yamiqa mata.
"Ki share wud'annan hawayen bana son ganinsu."
Karb'a tayi tayi kamar yanda yace sannan tamiqa masa ya karb'a ya mayar cikin aljihu,
"In fad'a maki wani Abu?"
Kad'a masa kai tayi yace "to yi murmushi mana tukuna, idan ba haka ba sai nafasa fad'a."
Murmushin da seda haqoranta suka bayyana tayi shima ya mayar mata had'e da cewa.
"Yawwa gimbiyar Abu sumayya, ummu sumayya, haka nake son akoda yaushe ki kasance, in Sha ALLAH su dady na nan tafe gobe su nema mani aurenki, saboda haka kidena damuwa soon zan d'aukeki izuwa duniyar farincikinDana tanada mana kinji ko?"
Saboda yanda farinciki ya rufeta batasan lokacin da tayi tsalleba had'e dayin dariya tana fad'in "da gaske Abu sumayya?."
"To kijira mana gobe kigani."
Ciro wata leda yayi a aljihunsa ya miqa mata sannan yace
"Ina wayarki?"
"Tana cikin nabaro."
"Ok ungo saka mani lambarki nasan yanzu kin canza layi ko?"
"Eh amma ni ai inada naka, kaje kawai zan kiraka"
"Nima fa na canza layi 'yan matana"
"Eh nasani mana."
Sallama yayi mata sannan yawuce saboda ganin takafe tanada sabon layinsa, wanda yake ganin abun da kamar wuya...
Ai kuwa bai qarasa gida ba sai gashi yaga ankirasa da sabuwar lamba,
Sanin yanda sukayi da ita yasa bai wani b'ata lokaci ba ya d'aga, muryarta yaji tace.
"Kasamu abun hawa kuwa?"
Saida sukayi sallar magrib sannan baba balarabe da little suka wuce bayan sunje can gidan baffa sun gaisa da nusaiba kuma little yaga qannen mahaifinsa, itama konkad'an basu bayyana mata kowaye little ba duk da yasaki jiki suna fira da ita da yaran sosai Amma kasancewar Bata san Nuraddeen ba balle Rashida yasa bata gano komai ba,
Little da baffa kuwa ji sukayi tamkar garsu rabu aranar saboda wata irin sabuwar soyayyar junansu da sukeji na taso masu.
Haka little wanda gaba d'aya yanzu ya maida sunansa Abu sumayya saboda soyayyar batul d'insa da yake dako azuciyarsa yaci gaba dayin rayuwarsa cikin jin dad'i, yana matuqar taimakawa kakannin nasa guda biyu aduk lokacin da yasamu dama, haka tab'angaren karatunsa yana maida hankali sosai duk da kuwa akwai wud'anda suka fishi qoqari tare da jajircewa hakan bai hanasa qasa a guiwa ba yana iya qoqarinsa na ganin shima yasamu abunda yasamu koda bai kaisu ba, har baya son hutu ya qare saboda farincikin da yake samu awajen kakan nasa, haka ya kammala shekarun karatunsa hud'u a tsakanin b'oyayyiyar gaskiyar da sukayi alqawarin b'oyewa a tsakaninsu har zuwa ranar da gaskiya zata bayyana, Kuma yayi nasara samun kyakkyawan sakamako a mataki na biyu wato second class..
A ranar daya amshi saka makon jarabawarsa aranar yaquduri aniyar zuwa gidansu batool domin ya gabatar da kansa awajen mahaifinta bayan yanemo izini da kuma sa albarkar mahaifiyarsa kamar yanda ta alqawarta masa, Kuma ysha alwashin koda za'a rabasa da rayuwarsa aranar sai ya tabbatarwa da batool cewa shi d'in nata ne ita kad'ai kuma ita kad'ai ya tanadawa zuciyarsa da kuma gangar jikinsa...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
_Awannan gab'ar alqalamina bazai iya cigaba da rubutu ba har sai ya miqo saqon gaisuwa tare da jinjina had'e da fatan alkhairi agareku, *AUNTY MAIJIDDA MUSA* da kuma *AUNTY FAREEDA MUHAMMAD ABBAS* Bisa zallar karamci, k'auna da kuma halacci da kuka nuna mani wajen jajircewa bibiyar wannan littafi nawa duk da kuwa irin tafiyar hawainiyar da yakeyi hakan baisa kuka nuna qosawa ko kuma gazawarku ba, kun qara mani qwarin guiwa tare da addu'o'in fatan alkhairi agareni da sukasani himmatu da kuma samun quwwar cigaba da rubuto wannan littafin cikin nasara, Ina yimaku addu'ar dukkanin alkhairan ALLAH su lullub'eku tare da ahalinku, nagode sosai da samun goyan bayanku acikin kowane rubutu nawa, ubangiji ALLAH yatsare mani ku kuma yakula mani daku aduk inda kuke👏, Fillah! akoda yaushe zuciyata na matuqar yabawa d'imbin karamci irin naku tare da yimaku son so na har abada😍_
Page___83💎
Tana fad'in "Abu sumayya!" Cike da kokwanto hakan aranta har ta qarso da gudu bakin gate d'in, daidai lokacin ya aza qafarsa zai fita taja wani irin burki had'e da tsayawa tana fidda lumfashi d'aya bayan d'aya saboda gudun da tayi.
Cikin wani irin salo takira sunansa tace.
"Abuu.. sumay..yaaa."
Cak ya tsaya da qafarsa had'e da lumshe idanuwa jin dirar sautin muryarta da yanda takira sunan acikin kunnuwansa, a hankali yajuyo da duka gangar jikinsa izuwa gareta suna fuskantar juna, lokaci d'aya idanuwansu suka sarqe suna isar masu da wani saqo dake fassara tsantsar soyayya da adadin kewar da suka yiwa junansa,
Wata irin dariya had'e da kukan farinciki taji sun kucce mata alokaci d'aya ta durqushe agabansa saboda qafafuwanta da taji na gagarar imata tace,
"Wannan wace irin bazatace mai cike da burgewa da kuma qayatarwa Abu sumayya?, Ka qaraso izuwa gareni kafin tsantsar farinciki yasa lumfashina d'aukewa."
Taqarasa maganar tare dasa hannuwanta ta rufe bakinta hawayen farinci na zubo mata a fuska, nad'e hannuwansa yayi akan qirjinsa yana kallonta yana murmushi, duk da ayanayin da ya ganta baiyi masa dad'i ba Amma farincikin ganinta yasa yakasa matsawa kusa da ita saboda nauyin da qafafuwansa suka yimasa, sunfi mintuna biyu ahaka kafi yafara takowa izuwa gareta yana cewa.
"Haba gimbiyar Abu sumayya! Wannan kukan da kikeyi ai saikisa hawayen dake zubowa daga idanuwanki su narkarmun da zuciya, kitashi mana na kalleki da kyau naga ko kin kula mani da kanki kamar yanda kika alqawarta mani kinji 'yan matanaaaa..." Yaja qarshen cikin wani salon sigar lallashi da yasa batasan lokacin data saki dariya ba had'e da miqewa tana rufe fuska.
"Sannu da zuwa annurin zuciyata, farincikina kuma uban 'ya'yanah." tafad'a cikin murmushi tana jifarsa da wani kallo mai cike da tarin ma'anoni kala kala.
Tsabar jin dad'in kalaman da yaji na fito daga bakinta ya sashi d'aga kansa yana murmushi tare da kallon fitillun da suka haskaka harabar gidan, gyara tsayuwarsa yayi idanuwansa na akan fuskarta yana kallonta sanna yace.
"Yawwa uwar 'ya'yana, makullin zuciyata da kuma mabud'inta, Ina fatar dai nasameki cikin amincin ALLAH da kuma yardarsa."
"Sosai kuwa, domin badon amincin ALLAH dake tare dani ba da tuni kewarka da rashinka sun kaini kushewata."
Saida yayi dariya sannan ya d'ago kai yana kallonta yace.
"Godiya ta tabbata agaresa daya tsare mani ke daga zuwa kushe don tseratar da rayuwar Abu sumayya daga fad'awa gararin duniya nahar abada, ya kike gimbiyata?.
"Ina lafiya yanzu tunda gani ga ka kuma."
"Alhamdulillah, nayi farinciki sosai duk da dai naga kamar kinyi k'wabron kula mani da kanki, Ina fatar akwai banbancin kulawar da ajiyar dana baki acikin zuciyarki."
"Babu buqatar tabbatar maka da hakan domin ance labarin zuciya atambayi fuska, ai tsantsar kula da ajiyar kane dake cikin zuciyata ya haifarwa da gangar jikina shiga cikin wannan hali, kaine kawai na shiga taraddadin cewa ka kula mani da tawa ajiyar ko kuwa?."
"Haba 'yan mata!, Ai wanzuwata awannan lokacin tare dake shine zai baki tabbacin cewa naba ajiyarki cikakkiyar kulawa, Alhamdulillah yau na karb'i sakamakon dake tabbatar da na kammala karatuna bayan adadin shekaru hud'u dana d'auka inayi cike da tarairayar qaunarki acikin zuciyata, hakan yasa na gaggauta dawowa agareki adaidai wannan lokacin da zimmar zamowa mijinki ke kuma mata kamar yanda na d'aukar maki alwashi, inafatar zaki amsheni hannu biyu ki maidani a gurbin da tun farko kika bani."
"Kash!..a gaskiya bazaka samu hakan ba domin na dad'e da cireka a wannan gurbin."
Tafad'a cike da zolayarsa tare da d'aure fuska ta juyar da kanta gefe, cikin fad'uwar gaba ya koma ta gefen data maida kanta yana kallonta.
"Kamarya! Ban fahimceki ba gimbiya?, Wai kina nufin kin d'aukeni daga wannan gurbin kin bawa wani.. how? " yafad'a yana tsareta da idanuwansa da suka soma canza kala.
Kwashewa tayi da dariya harda tafa hannuwa tana nunasa, sake d'aure fuska yayi yana binta da wani irin kallo da yasa dole ta tsaida dariyar had'e da cewa.
"Afuwan Abu sumayya!, Ba haka nake nufiba, taya kake tsammanin zan iya cireka ga wuri har in aza wani?, Wannan abune da bazai yuyuba kama dena tunanin hakan."
"Taya tunanina bazai bani hakan ba bayan da bakinki kikace.."
"Don ALLAH kayi haquri da wasa nakeyi.."
Kafeta yayi da idanuwa kafin yayi wata irin ajiyar zuciya ya juya mata baya.
"Pls kayi haquri mana.."
"Em'ehm..ni nayi fushi, dama d'azun kin b'atan rai da kikace natafi bakya buqatar ganina, sonki ne da yayi mun yawa yasa na iya dawowa garemu da kika fito"
"Wayyo...kayi haquri mana, plsss..."
Tafad'a tare da komawa gabansa tariqe kunnuwa,
Dariya ya saki sannan yace.
"Shikenan nahaqura, bari natafi dare ya somayi."
Nan take kamannin fuskarta suka sauya daga farinciki zuwa damuwa.
"Meye gimbiya?"
"Bana son katafi Abu sumayya, gaba d'aya shekarunnan hud'u a jigace na qarar dasu saboda rashinka da kuma ganinka, ka qaramun lokaci mana ko hasken daya d'iga azuciyata zai qara yawan da zai haskamun yau zuwa gobena."
"Kamar ya gimbiya?, So kikeyi na kwana anan ne? Ko bakiga lokaci naqara qurewa bane?"
Saida ya duba agogon dake hannunsa sannan yace.
"Kin gafa har goma da rabi takusa, gashi akwai nisa da inda zanje gidan baffan mamana, in dai akaina ne ki kwantar da hankalinki yanzu kullum muna tare kinji ko?"
"Ka kasa fahimtata ne, Taya hakan zai faru abbana na nema ya aura mani duk wanda yaga dama naqi amincewa, sanadiyar hakan ya sanya mani tsauraran matakai,"
"To kinga ya kamata ace natafi yanzu kamin ya sameni, na tabbata ko yanzu don baya gida shiyasa muka samu wannan damar, don haka kiyi haquri kinji ko?"
'Daga masa kai tayi idanuwanta na tsiyayar da hawaye yacire hankacif daga cikin aljihunsa yamiqa mata.
"Ki share wud'annan hawayen bana son ganinsu."
Karb'a tayi tayi kamar yanda yace sannan tamiqa masa ya karb'a ya mayar cikin aljihu,
"In fad'a maki wani Abu?"
Kad'a masa kai tayi yace "to yi murmushi mana tukuna, idan ba haka ba sai nafasa fad'a."
Murmushin da seda haqoranta suka bayyana tayi shima ya mayar mata had'e da cewa.
"Yawwa gimbiyar Abu sumayya, ummu sumayya, haka nake son akoda yaushe ki kasance, in Sha ALLAH su dady na nan tafe gobe su nema mani aurenki, saboda haka kidena damuwa soon zan d'aukeki izuwa duniyar farincikinDana tanada mana kinji ko?"
Saboda yanda farinciki ya rufeta batasan lokacin da tayi tsalleba had'e dayin dariya tana fad'in "da gaske Abu sumayya?."
"To kijira mana gobe kigani."
Ciro wata leda yayi a aljihunsa ya miqa mata sannan yace
"Ina wayarki?"
"Tana cikin nabaro."
"Ok ungo saka mani lambarki nasan yanzu kin canza layi ko?"
"Eh amma ni ai inada naka, kaje kawai zan kiraka"
"Nima fa na canza layi 'yan matana"
"Eh nasani mana."
Sallama yayi mata sannan yawuce saboda ganin takafe tanada sabon layinsa, wanda yake ganin abun da kamar wuya...
Ai kuwa bai qarasa gida ba sai gashi yaga ankirasa da sabuwar lamba,
Sanin yanda sukayi da ita yasa bai wani b'ata lokaci ba ya d'aga, muryarta yaji tace.
"Kasamu abun hawa kuwa?"