Sashe 77
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ransa ab'ace yanufi gidan Yaya Maryam yakirata tare da zayyane mata duk abunda kefaruwa, dama tayi mamakin ganinsa shida jiya suka rabu baran baran da ita sai gashi har yana fad'in ko mijin Rashida naso ko baya so duk inda yaje dolene ya saketa, kuma dole duk wata alaqa dake tsakaninsu su datseta koda hakan na nufin zasu mayar masa da d'ansa a hannun sane.
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___59💎
Baffa, baffa, baffa ga aunty tadawo, abunda Yusuf kefad'a kenan har ya isa bakin qofar shiga gida, karo yaci da mahaifin nasa wato baffa Ali shida Dr. nura dake qoqarin barin wajen fuskarsa a cunkushe babu alamun walwala atattare da ita, kad'an yarage Yusuf yafad'i garin kallon Dr nura daya ga yanufi inda su Rashida suke, da sauri ya riqo hannun baffa Ali yana jansa had'e da nufar inda ya gasu Rashida yana nuna masa wajen da hannu, gaba d'aya Yusuf ya rud'e ya manta da cewa ba mahaifinsa yakamata yasan da dawowar taba sanin irin matsayin da take dashi awurinsa.
Baffa Ali kuwa binsa yayi har suka isa wajen lado mai kalanzir, lokacin kuwa har su Rashida sunbar wajen saboda irin amsar da Dr nura nura yazo masu da ita,
"Lado Ina aunty?"
"Kai yusuf wace aunty kuma?."
"Haba lado! Anan fa nabarta ita da wata mata, nan wajen!." Yaqare maganar yana nuna masa inda suka tsaya.
"Aiho nan naga sunbi suda wani mutum." Lado yafad'a yana d'aure ledar daya zubawa wata yarinya kalanzir.
Dagudu Yusuf yabi hanyar baffa Ali shima yabi bayansa don yatabbatar da da hakan,
Suna kawowa su Rashida naqoqarin shiga mota ya shiga qwala mata kira.
"Aunty, auntyyyy.."
Juyowa tayi tana goge hawaye harya iso wajen, da sauri baffa Ali yab'oye bayan wani kango yana hangosu don kada taganshi.
"Aunty ina zaki tafi kuma, kizo muje gida don ALLAH, ya nura nason ganinki shida su baffa da Inna bilki, kowama nason ganinki munyi kewarki sosai don ALLAH kizo muje kinji aunty."
"Yusuf me zanje inyo agidanku Bayan wanda nazo don shi gaba d'aya yabar qasar, zantafi Kuma bazan sake dawowa acikin gidanku ba saboda bakwa sona." Tafad'a tana kuka tare da juyawa zata shiga motar, riqe hijab d'inta yayi shima yana kukan yace.
"A'a aunty muna sonki don ALLAH kada kitafi."
Hannunta tasa tacire hannunsa daga riqon daya yiwa hijabinta sannan tafad'a cikin motar Dr. Nura yaja sukabar wajen.
Kuka Yusuf keyi kamar ransa zai fita had'e da nufar hanyar zuwa gidan baffa, da sauri baffa Ali yafito daga mab'uyar daya shige yatare gabansa had'e da kamo hannunsa,
"Kai Yusuf ina zakaje ne acikin daren nan?"
Ya tambayesa had'e da d'aure fuska yana kallonsa.
Cikin sheshshekar kuka Yusuf yace.
"Gidan baffa zanje."
"Kaje kayo ubanmi acan?."
"Zanje infad'a masa Aunty tadawo amma ta tafi kuma tace bazata sake dawowa ba."
Saida ya sakar masa wani mugun ranqwashi akai sannan yace.
"To uban waye ya aikeka? idan Auntyn tadawo qanwar uwarka ce kota ubanka da zakaje kasanar dasu tunda tace bazata koma dawowa to meye naka aciki.?"
Qoqarin bud'e baki yayi don ya bashi amsa sai Kuma yayi saurin rufewa da hannunsa sanadiyar yanda ya murd'e masa kunne so had'e da cewa.
"Karka sake inji kafidda wannan maganar waje kaji nagaya maka, inba haka ba yanda Yaya hawwa ta b'addata kaima haka zansa a b'adda kai, kaga shikenan baka ba ganin kowa naka wata qilama kamutu gaba d'aya ahuta, shashashan yaro kawai, har kamanta akanta akaje aka kullemu ni da mahaifiyarka, babu kalar azaba da kuma dukan da bamu sha ba ahannun 'yan sanda kuma duk ta dalilinta, to bari kaji duk kasake naji wannan maganar abakin wani sai nayi maka d'an banzan duka kuma wlh kadena cin abincin gidana kenan har kamatu, shegen yaro da bansan halin waye kad'auko ba, maza kawuce gida kafin in jijjimaka anan"
Sosai Yusuf ya tsorata dajin kalaman da baffansa ya fad'a masa don haka yanufi gida yana kuka kamar ransa zai fita, kasa shiga d'akin mahaifiyarsa yayi yakoma saman barandar part d'insu ya Nuraddeen dake rufe ya had'a kai d guiwa yanaci gaba da kukansa, tun qarfe takwas yake zune wajen yana kuka har wucewar goma da rabi nadare kan kace me tuni zazzab'i ya taso masa ya fara rawar sanyi, Inna Bilkisu ce tafito zata zagaya bayi tagansa wajen a kwance had'e da cewa.
"Kai Yusuf lafiya kazo nan ka kwanta ko sanyin nan bakaji?, Maza tashi kawuce d'aki kar mura takama ka"
Ba tare data tsaya sauraren amsar da zai bata ba tawuce bayi don yin lalurar data fiddota, koda tadawo ta tarar har lokacin yana a wajen kwance ko motsawa baiyi ba daga inda tabarshi
"Ikon ALLAH, wai bakaji me nace maka bane Yusuf.?"
Tafad'a tare da qarasawa wajen tana d'agosa, yanda taji jikinsa ya gashe da zafi sai faman rawar sanyi yakeyi yasa tayi saurin rungumosa ajiki tana daddafa kansa.
"Subhanallahi, Yusuf dama baka lafiya shine kazo nan ka kwanta."
'Dago kansa yayi yana qoqarin yimata magana saiga baffa Ali ya shigo shida baffa Usman, ai yana ganin haka da sauri yaqarasa wajen yana fad'in.
"Kai Yusuf mekakeyi wajen? Ko munafuccin ne kaima zaka koya." Ya zata maganarce yake fad'a mata,
Inna Bilkisu najin haka tacire Yusuf daga jikinta had'e da zaunar dashi saman barandar tanufi inda mijinta yake tsaye yana jinjina irin kalaman da d'an uwansa ke alqanta iyalinsa dasu, shi kuwa baffa qiiiii...yaja hannun Yusuf har yana neman fad'uwa yana fad'in.
"Wannan yaron anyi mai kunnen qashi, ina dai kasan abunda nace maka shine zakazo nan kasaki baki don rashin jin magana" hed'e da jefasa saman gadonsu d'an bono bayan sun shiga d'aki,
••• ••• •••
Dr kuwa banda tunanin kalaman da baffa yafad'a masa babu abunda yakeyi, wannan wace irin rayuwace muke ciki aduniya?, Wanda ma kayarda dashi alokaci d'aya sai ya sauya maka, ancuci yarinya kuma ankoma ana binta da sharri, a iya saninsa inzai tuna Rashida tafad'a masa cewa mahaifin mijinta na qaunarta Amma sai gashi maganganun daya fad'a masa akanta sunsha banban da irin kalaman daya dace afad'a ga wanda ake so, saita madubinsa yayi yana kallon yanda hawaye ke tsiyayowa daga cikin idanuwanta dake rufe ya saki wata irin ajiyar zuciya, tabbas ta cancanci tayi kuka ba kad'an ba, ko kad'an bazai hanata tayi shiba awannan karon saboda abubuwan sunyi mata yawa, a qaramcin shekarunta bai kamata ace tafuskanci irin wud'annan damuwowin ba donma Allah yataimaka ansamu jininta yakoma normal da tuni qila zuciyarta tabuga, duk da dai bai sanar da ita gaskiyar abunda yafaru tsakaninsa da baffa Ali ba daya nuna masa cewa shine mahaifin Nuraddeen, kawai dai ya fad'a mata cewa ance baya nan yabar qasar.
Tare suka shiga gidan da ita lokacin da suka iso yaya Maryam na tsaye tsakar gida tana jijjiga little da sai faman kuka yakeyi tun d'azu.
Miqa hannunta tayi ta karb'esa kanta naduqe aqasa batare data bari sun had'a ido da yaya Maryam ba data zuba mata ido tana kallo.
'Daki tawuce, su kuma suka tsaya suna gaisawa da ita,
"Sannu Dr har kin dawo.?"
"Eh ya gida yaya Maryam."
"Gida Alhamdulillah Dr, kunbarni da yaro sai faman tsula Mani kuka yakeyi?"
Murmushi yayi had'e da cewa.
"Afuwan ai gamu mun dawo, dama kwana biyu Fatima tadameni da zancen ta shine nace bari muzo dubata sai gashi munci karo da ita, ganin babu alamun walwala atattare da fuskarta yasa nace bara muje da ita wani wurin taraka mu, I fatar za'ayi mana afuwa bisa wannan kuskuren?" Yafad'i hakanne saboda yasan ran Yaya Maryam b'aci zaiyi idan tasan gaskiyar inda sukaje.
"Ba komai Dr, ai kaga Fatima gaisawa kawai mukayi tabi bayansu saboda sukad'ai tadamu dasu"
Shiru yayi na tsawon wasu 'yan sakanni kafin yace.
"Amm! Dama yaya maryam cewa nayi yakamata ariqa kwantarwa da Rashida hankali saboda yanayin damuwowin da suka tarar mata azuciya don kar takoma shiga wani halin, nasan kuna qoqari sosai tunda gashi naga cikin kwanakinnan tacanza ba kamar yanda muka zoba saboda yanayin natsuwar da tasamu, amma don ALLAH aqara bata kulawa, sha'aninta akwai bantausayi aciki sosai."
"Ikon ALLAH!, Ai dama nasan dole qara tace zata kai wajenka Dr tunda muna ganin mutuncinka, yakamata ace rashida ta fahimci abunda muke guje mata faruwarsa saidai takasa gane hakan..."
Nan takwashe komai tafad'a masa akan abunda yafaru ba qari balle ragi, sosai Dr yashiga rud'ani daya auna maganganun guda biyu, da wud'anda baffa yafad'a masa da kuma na yaya Maryam yagano akwai wani abun aqasa wanda ba daidai ba, ko meye kuma ALLAH kad'ai yasani."
Haquri yabata tare da sake roqonta a lallab'ata in Sha ALLAH da sannu zata fahimcesu sannan ya koma bakin motarsa yana jiran fitowar Fatima.
Rashida kuwa saida taba little nono yasha ya qoshi Fatima na gefenta tana dad'a bata haquri tare da rarrashinta sannan tamiqa mata shi ta kwanta saman qatuwar katifar dake cikin d'akin nata, anan maganganun da suka faru tsakaninta dashi a daren ranar suka shiga dawo mata a kwakwalwa, tabbas ita ta qarfafa masa yin wannan tafiyar kuma ko kad'an hakan da yayi ba laifi bane, Amma meyasa ya aikata hakan batare daya sanar da iyayenta ba.? Meyasa baiyi tunanin abunda zai iya faruwa ba akan wannan kuskuren da yayi, kamata yayi ace ya fahimci cewa komai na duniya kan iya sauyawa idan aka samu sauyin al'amurra, kama daga ra'ayi, buqata, lafiya, wajen zama da kuma yanayi na yau da kullum, gashi yanzu yaje yabar baya da qura, babbar damuwarta shine rashin sanin har tsawon wane adadin lokaci zai d'auka kafin yadawo.
Jitayi Fatima nafad'in "maman boy zamu tafi, yana waje yana jirana, don ALLAH kimaida al-amurranki agaresa kidena kukannan bayada amfani, ga wannan wayace uncle d'inki ya siya maki zamu rinqa magana, akwai lambata da tashi aciki kuma na saka maki ta yaya maryam data aunty marwiyya saiki kirasu, kada kiyarda inkira injita akashe, ko yaushe ina son ki kasance tare da ita kinji ko?."
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___59💎
Baffa, baffa, baffa ga aunty tadawo, abunda Yusuf kefad'a kenan har ya isa bakin qofar shiga gida, karo yaci da mahaifin nasa wato baffa Ali shida Dr. nura dake qoqarin barin wajen fuskarsa a cunkushe babu alamun walwala atattare da ita, kad'an yarage Yusuf yafad'i garin kallon Dr nura daya ga yanufi inda su Rashida suke, da sauri ya riqo hannun baffa Ali yana jansa had'e da nufar inda ya gasu Rashida yana nuna masa wajen da hannu, gaba d'aya Yusuf ya rud'e ya manta da cewa ba mahaifinsa yakamata yasan da dawowar taba sanin irin matsayin da take dashi awurinsa.
Baffa Ali kuwa binsa yayi har suka isa wajen lado mai kalanzir, lokacin kuwa har su Rashida sunbar wajen saboda irin amsar da Dr nura nura yazo masu da ita,
"Lado Ina aunty?"
"Kai yusuf wace aunty kuma?."
"Haba lado! Anan fa nabarta ita da wata mata, nan wajen!." Yaqare maganar yana nuna masa inda suka tsaya.
"Aiho nan naga sunbi suda wani mutum." Lado yafad'a yana d'aure ledar daya zubawa wata yarinya kalanzir.
Dagudu Yusuf yabi hanyar baffa Ali shima yabi bayansa don yatabbatar da da hakan,
Suna kawowa su Rashida naqoqarin shiga mota ya shiga qwala mata kira.
"Aunty, auntyyyy.."
Juyowa tayi tana goge hawaye harya iso wajen, da sauri baffa Ali yab'oye bayan wani kango yana hangosu don kada taganshi.
"Aunty ina zaki tafi kuma, kizo muje gida don ALLAH, ya nura nason ganinki shida su baffa da Inna bilki, kowama nason ganinki munyi kewarki sosai don ALLAH kizo muje kinji aunty."
"Yusuf me zanje inyo agidanku Bayan wanda nazo don shi gaba d'aya yabar qasar, zantafi Kuma bazan sake dawowa acikin gidanku ba saboda bakwa sona." Tafad'a tana kuka tare da juyawa zata shiga motar, riqe hijab d'inta yayi shima yana kukan yace.
"A'a aunty muna sonki don ALLAH kada kitafi."
Hannunta tasa tacire hannunsa daga riqon daya yiwa hijabinta sannan tafad'a cikin motar Dr. Nura yaja sukabar wajen.
Kuka Yusuf keyi kamar ransa zai fita had'e da nufar hanyar zuwa gidan baffa, da sauri baffa Ali yafito daga mab'uyar daya shige yatare gabansa had'e da kamo hannunsa,
"Kai Yusuf ina zakaje ne acikin daren nan?"
Ya tambayesa had'e da d'aure fuska yana kallonsa.
Cikin sheshshekar kuka Yusuf yace.
"Gidan baffa zanje."
"Kaje kayo ubanmi acan?."
"Zanje infad'a masa Aunty tadawo amma ta tafi kuma tace bazata sake dawowa ba."
Saida ya sakar masa wani mugun ranqwashi akai sannan yace.
"To uban waye ya aikeka? idan Auntyn tadawo qanwar uwarka ce kota ubanka da zakaje kasanar dasu tunda tace bazata koma dawowa to meye naka aciki.?"
Qoqarin bud'e baki yayi don ya bashi amsa sai Kuma yayi saurin rufewa da hannunsa sanadiyar yanda ya murd'e masa kunne so had'e da cewa.
"Karka sake inji kafidda wannan maganar waje kaji nagaya maka, inba haka ba yanda Yaya hawwa ta b'addata kaima haka zansa a b'adda kai, kaga shikenan baka ba ganin kowa naka wata qilama kamutu gaba d'aya ahuta, shashashan yaro kawai, har kamanta akanta akaje aka kullemu ni da mahaifiyarka, babu kalar azaba da kuma dukan da bamu sha ba ahannun 'yan sanda kuma duk ta dalilinta, to bari kaji duk kasake naji wannan maganar abakin wani sai nayi maka d'an banzan duka kuma wlh kadena cin abincin gidana kenan har kamatu, shegen yaro da bansan halin waye kad'auko ba, maza kawuce gida kafin in jijjimaka anan"
Sosai Yusuf ya tsorata dajin kalaman da baffansa ya fad'a masa don haka yanufi gida yana kuka kamar ransa zai fita, kasa shiga d'akin mahaifiyarsa yayi yakoma saman barandar part d'insu ya Nuraddeen dake rufe ya had'a kai d guiwa yanaci gaba da kukansa, tun qarfe takwas yake zune wajen yana kuka har wucewar goma da rabi nadare kan kace me tuni zazzab'i ya taso masa ya fara rawar sanyi, Inna Bilkisu ce tafito zata zagaya bayi tagansa wajen a kwance had'e da cewa.
"Kai Yusuf lafiya kazo nan ka kwanta ko sanyin nan bakaji?, Maza tashi kawuce d'aki kar mura takama ka"
Ba tare data tsaya sauraren amsar da zai bata ba tawuce bayi don yin lalurar data fiddota, koda tadawo ta tarar har lokacin yana a wajen kwance ko motsawa baiyi ba daga inda tabarshi
"Ikon ALLAH, wai bakaji me nace maka bane Yusuf.?"
Tafad'a tare da qarasawa wajen tana d'agosa, yanda taji jikinsa ya gashe da zafi sai faman rawar sanyi yakeyi yasa tayi saurin rungumosa ajiki tana daddafa kansa.
"Subhanallahi, Yusuf dama baka lafiya shine kazo nan ka kwanta."
'Dago kansa yayi yana qoqarin yimata magana saiga baffa Ali ya shigo shida baffa Usman, ai yana ganin haka da sauri yaqarasa wajen yana fad'in.
"Kai Yusuf mekakeyi wajen? Ko munafuccin ne kaima zaka koya." Ya zata maganarce yake fad'a mata,
Inna Bilkisu najin haka tacire Yusuf daga jikinta had'e da zaunar dashi saman barandar tanufi inda mijinta yake tsaye yana jinjina irin kalaman da d'an uwansa ke alqanta iyalinsa dasu, shi kuwa baffa qiiiii...yaja hannun Yusuf har yana neman fad'uwa yana fad'in.
"Wannan yaron anyi mai kunnen qashi, ina dai kasan abunda nace maka shine zakazo nan kasaki baki don rashin jin magana" hed'e da jefasa saman gadonsu d'an bono bayan sun shiga d'aki,
••• ••• •••
Dr kuwa banda tunanin kalaman da baffa yafad'a masa babu abunda yakeyi, wannan wace irin rayuwace muke ciki aduniya?, Wanda ma kayarda dashi alokaci d'aya sai ya sauya maka, ancuci yarinya kuma ankoma ana binta da sharri, a iya saninsa inzai tuna Rashida tafad'a masa cewa mahaifin mijinta na qaunarta Amma sai gashi maganganun daya fad'a masa akanta sunsha banban da irin kalaman daya dace afad'a ga wanda ake so, saita madubinsa yayi yana kallon yanda hawaye ke tsiyayowa daga cikin idanuwanta dake rufe ya saki wata irin ajiyar zuciya, tabbas ta cancanci tayi kuka ba kad'an ba, ko kad'an bazai hanata tayi shiba awannan karon saboda abubuwan sunyi mata yawa, a qaramcin shekarunta bai kamata ace tafuskanci irin wud'annan damuwowin ba donma Allah yataimaka ansamu jininta yakoma normal da tuni qila zuciyarta tabuga, duk da dai bai sanar da ita gaskiyar abunda yafaru tsakaninsa da baffa Ali ba daya nuna masa cewa shine mahaifin Nuraddeen, kawai dai ya fad'a mata cewa ance baya nan yabar qasar.
Tare suka shiga gidan da ita lokacin da suka iso yaya Maryam na tsaye tsakar gida tana jijjiga little da sai faman kuka yakeyi tun d'azu.
Miqa hannunta tayi ta karb'esa kanta naduqe aqasa batare data bari sun had'a ido da yaya Maryam ba data zuba mata ido tana kallo.
'Daki tawuce, su kuma suka tsaya suna gaisawa da ita,
"Sannu Dr har kin dawo.?"
"Eh ya gida yaya Maryam."
"Gida Alhamdulillah Dr, kunbarni da yaro sai faman tsula Mani kuka yakeyi?"
Murmushi yayi had'e da cewa.
"Afuwan ai gamu mun dawo, dama kwana biyu Fatima tadameni da zancen ta shine nace bari muzo dubata sai gashi munci karo da ita, ganin babu alamun walwala atattare da fuskarta yasa nace bara muje da ita wani wurin taraka mu, I fatar za'ayi mana afuwa bisa wannan kuskuren?" Yafad'i hakanne saboda yasan ran Yaya Maryam b'aci zaiyi idan tasan gaskiyar inda sukaje.
"Ba komai Dr, ai kaga Fatima gaisawa kawai mukayi tabi bayansu saboda sukad'ai tadamu dasu"
Shiru yayi na tsawon wasu 'yan sakanni kafin yace.
"Amm! Dama yaya maryam cewa nayi yakamata ariqa kwantarwa da Rashida hankali saboda yanayin damuwowin da suka tarar mata azuciya don kar takoma shiga wani halin, nasan kuna qoqari sosai tunda gashi naga cikin kwanakinnan tacanza ba kamar yanda muka zoba saboda yanayin natsuwar da tasamu, amma don ALLAH aqara bata kulawa, sha'aninta akwai bantausayi aciki sosai."
"Ikon ALLAH!, Ai dama nasan dole qara tace zata kai wajenka Dr tunda muna ganin mutuncinka, yakamata ace rashida ta fahimci abunda muke guje mata faruwarsa saidai takasa gane hakan..."
Nan takwashe komai tafad'a masa akan abunda yafaru ba qari balle ragi, sosai Dr yashiga rud'ani daya auna maganganun guda biyu, da wud'anda baffa yafad'a masa da kuma na yaya Maryam yagano akwai wani abun aqasa wanda ba daidai ba, ko meye kuma ALLAH kad'ai yasani."
Haquri yabata tare da sake roqonta a lallab'ata in Sha ALLAH da sannu zata fahimcesu sannan ya koma bakin motarsa yana jiran fitowar Fatima.
Rashida kuwa saida taba little nono yasha ya qoshi Fatima na gefenta tana dad'a bata haquri tare da rarrashinta sannan tamiqa mata shi ta kwanta saman qatuwar katifar dake cikin d'akin nata, anan maganganun da suka faru tsakaninta dashi a daren ranar suka shiga dawo mata a kwakwalwa, tabbas ita ta qarfafa masa yin wannan tafiyar kuma ko kad'an hakan da yayi ba laifi bane, Amma meyasa ya aikata hakan batare daya sanar da iyayenta ba.? Meyasa baiyi tunanin abunda zai iya faruwa ba akan wannan kuskuren da yayi, kamata yayi ace ya fahimci cewa komai na duniya kan iya sauyawa idan aka samu sauyin al'amurra, kama daga ra'ayi, buqata, lafiya, wajen zama da kuma yanayi na yau da kullum, gashi yanzu yaje yabar baya da qura, babbar damuwarta shine rashin sanin har tsawon wane adadin lokaci zai d'auka kafin yadawo.
Jitayi Fatima nafad'in "maman boy zamu tafi, yana waje yana jirana, don ALLAH kimaida al-amurranki agaresa kidena kukannan bayada amfani, ga wannan wayace uncle d'inki ya siya maki zamu rinqa magana, akwai lambata da tashi aciki kuma na saka maki ta yaya maryam data aunty marwiyya saiki kirasu, kada kiyarda inkira injita akashe, ko yaushe ina son ki kasance tare da ita kinji ko?."