Sashe 136
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'ah bari dai in shiga ciki." Yafad'a yana tsille da qafa yana qoqarin shiga cikin rumfar, saurin d'auko masa iccen da yake tokarawa dashi baffa yayi had'e da taimaka masa ya daidaita shi sannan yace.
"Ali kacire damuwa mu zauna mu natsu musamo mafita, damuwar da kake qara cilla kanka aciki bafa zata haifama komaiba sai wahala, tunda dai har kayi nadama to kayi Imani da qaddararka mai kyau da marar kyau, in Sha ALLAH zaka samu mafita."
Nan ma kukan ya sake fashe masa dashi saida yayi daqyar yasamu suka koma zauren, Inna Bilkisu dake tsaye gefe ta shiga girgiza kai cike da tausayinsa, Wai yau alin da tasani ne fitinanne da hatsabibanci ke russunawa duniya haka, lallai rayuwar duniya ba komai bace kuma batada tabbas ko kad'an, sanin yana matuqar son fura yasa tashiga d'aki ta d'auko dawon da tasaye d'azu tunda taji yace bazai iya cin abincin ba ta dama masa takai masa acan zauren ya d'ago kai cikin sanyin murya had'e da cewa.
"Sannu balkisu, nagode ALLAH yasaka maki da alkhairi."
"Amin ya rabbi, ka d'aure kasha furar ko kad'an ce, ba a biyewa damuwa azauna da yunwa domin had'uwa sukeyi waje d'aya su illata mutum."
Har zata fita yakira sunanta tadawo, ya sake fashewa da kuka tare da roqonta tayafe masa abubuwan daya yimata don ALLAH, da yake mace ce mai raunin zuciya nan take sai itama tafashe da kukan tana fad'in.
"Ali nayafe maka duk abunda kayi mani wanda kasani da wanda baka sani ba duniya da lahira, kuma Ina roqon kaima ALLAH ya yafe maka ya dawo da hankalin iyalinka agareka ta zauna ta kula dakai kaima."
Girgiza kai kawai yayi don yasan inna ruqayya bazata tab'a hankalta ba sai ranar da duniya ta hankaltar da ita, "nagode sosai Bilkisu ALLAH ya albarkaci yaranki yakaresu da rud'in duniya."
Da ita har baffa Usman suka amsa da amin sannan tabar wajen, kallonsa baffa Usman yayi had'e da cewa.
"Ali idanfa kana tuna abubuwan da suka riga suka wuce to tabbas ka dingi kuka kenan har iya qarshen rayuwarka, Ina baka shawara kayi haquri ka godewa ALLAH daya ganar dakai kafin lokaci yaqure maka."
Saida ya goge kwallan da suka zubo masa sannan ya saki wata ajiyar zuciya had'e da cewa.
"Dole na zubda hawaye Usman, wallahi aduk lokacin da naga kuna hidima dani da yaran nan dake wajenku duk irin cin kashi da kuma mutunci da nayi maku sai naji waninirin nauyi da kunya sun dabai bayeni, nacutar daku amma gashi kunata kyautata mani, wlh da mutane zasu gane da sun daina cutarwa ga mutanen dake Shire da kyautata masu, don wannan abun da kike yimani shine mafi girman horon da kuke hukunta zuciyata dashi, zaifi sauqi ace cutar da mutum akayi kamar yanda ya cutar da adinga binsa da kyautatawa da kuma alkhairai domin yafi shiga kunya da nadamar da zuciyarsa zatayita d'awainiya da abubuwan daya aikata."
"Kamanta da komai, ni babu sauran zarginka ko kuma tsanarka araina, fatana ALLAH yayafe maka laifinka kuma yabamu mafita, din natabbata shi kad'aine zaisa yaya yasake baka damar jingina dashi akaro na biyu duk da dai tsananin b'acin rai yasa yakai ga yanke maka wannan hukunci amma inada yaqini akan zai sauko kuma ya yafe maka shima."
"ALLAH ya qaddara hakan, Amma girman laifina na cancanci hukuncin da yayi mani kuma koda ya gagara yafemun bayada laifi." Yaqara fashewa da wani kukan.
Haka sukaci gaba da maganganunsu baffa Usman naqara yimasa nasiha akan illar biyewa son zuciya da kuma sharrin duniya da rud'in shed'an har aka kira sallar magrib sukayi arwala suka wuce masallaci, bayan angama sallah baffa Usman yamiqe had'e da kallon baffa Ali yace.
"Bari naje wajen Yaya naga halin da yake ciki ina tsoron kar shima yashiga damuwa irin yanda kake ciki!"
"Shikenan bari nad'an gincira kafin akira sallar isha'i, seka dawo."
"To madallah, amma karka kwanta domin babu kyau bacci tsakanin sallar magrib da isha'i, annabinmu yayi hani ga hakan, zaifi kazauna kiyita yimasa sakati da zikiri da kuma hailala har akira sallar ko kuma ka d'auko qur'ani kayi tilawa, bari namaza naje na dawo."
Yana kaiwa nan yafice da sauri don baya son ya rasa jam'i shi kuma ya d'auko qur'aninsa yafara tilawa kamar yanda d'an uwansa ya shawartai.
Koda baffa Usman yaje gidan baffa ya iskoshi tsakar gida 'ya'yansa duka sun zagayesa anata fira ana dariya, murmushin jin dad'in ganinsa haka babu abunda yasamesa yayi had'e da qarasawa ciki yana fad'in.
"Allah ya taimaki uban d'iya yaja da tsawon rai." Yana wani d'aga hannu tare da dudduqawa kamar yanda fadawan sarki keyi gaba d'aya duk sukasa dariya hadda baffa tare da miqa masa hannu sukayi musabaha sannan yace.
"Ai kaine uban d'iya malan Usmanu ko yau kabar mani d'iyan baka so."
"Inaaa.. Yaya nakai ga manyan d'iya haka tubarkallah kace in barmaka, ai Abba kawai ne banayi shida aka yimani rashin kara akansa."
Gaishesa suka shigayi d'aya bayan d'aya yana amsawa kafin akawo ga Abba yamiqa masa hannu yana fad'in.
"Assalamu alaikum baffa barka da dare." Lokacin yanada shekara goma sha biyu.
Dariya baffa yayi had'e da kallon baffa Usman daya kama hannunsa yariqe gam yana dariya yace.
"Aminina kenan, gaisuwarsa ba irin tasu bace."
Nan shima Baffa Usman yayi zaunensa akaci gaba da firar dashi har aka kira sallar isha'i yamiqe da sauri had'e da yimasa sallama sannan yabar gidan, yaso yayi masa maganar baffa Ali amma yanda yaga farinciki kwance afuskokin gidan yasa yafasa don kada yarusa masu shi izuwa damuwa aransa yana yabawa 'yar 'yar uwar matar tasa data iya gusar da yanayin damuwar da yayan nasa yafita dashi d'azun alokaci d'aya, tabbas Babu abunda yakai matar qwarai samun kwanciya da cikakkiyar natsuwar namiji aduniya..
Bayan anqare sallah duk suka nufi gida suna tafe suna shawara akan maganar da baffa Ali yafad'a cewa ya samu mafita akan maganarsu ta d'azu, Inna ruqayya zasu tuntub'a tunda tare sukayi komai da ita ya tabbata ita bazata manta wajen ba, damuwar d'aya ce shine daqyar in zata amince tagwada masu wajen tunda tasan sharad'in da malamin tsibbon nasu yabayar, daga karshe dai baffa Ali yace abarshi da ita zai san yanda za'ayi ta gwada masa don kai tsaye idan aka fuskanceta da maganar bazata yarda ba, da haka suka shiga shiga ya tadda ita zaune tsakar d'aki da gani bata dad'e da dawowa wajen baran ba ta bubbud'e qafafuwa ta zube kud'ad'en da tasamo tana qidaya, sallama yayi har sau biyu bata tanka shiba sai da yayi ta uku tukuna ta d'ago kai cikin tsiwa irin ta fitinannun tsofaffin matannan tace.
"Kai nifa Ali ba nison tsarguwa, dolene amsa sallamar koko dai dolene, in banda gulma baka tashi dawowa ba sai yanzu da kaga ina kikkimtsa abunda ALLAH yabani, to ALLAH yasani idan ma da biyu kayi ko shishi (sisi) bazan baka ba, badai bazaka bara ba? To ni kuma bazan baka shishi (sisi) naba, in shigowa zakayi ka shigo bana son talla kawani hankad'e mani labule, dama haqoranta wasu duk sun fita shiyasa bata iya fad'an sisin da kyau take cewa shishi, batare daya tanka taba ya wucikkewarsa ya zauna gefen gado yana kallonta har tagama qidayar kud'inta sannan tajawo wata leda taciro lemu da biredi sai kuma nama atakarda tahauci abunta, qille bata raga ba har saida ta cinyesa tas batare data sammashi ko kad'an ba sannan tabuga gyatsarta tamiqe tana yimasa habaice habaice, dama shi kota bashi bazai karb'a ba don yasan haramun ne tunda roqa tayi ba bata akayi ba, kuma shi roqo baida kyau awani nassima an haramta yinsa inba da wata babbar lalura ba.
So yake ya d'auko mata zancen amma ganin abubuwan da takeyi yasa yarasa ta inama zai fara, can dai yayi qarfin hali ya daure cikin yanayin da bazata kawo komai ba yace
"Nikuwa ruqayya wai a inane muka binne maganin nan.", juyowa tayi daga kan gadonta data haye had'e da cewa.
"Lafiya kake tambayata?, Ina ai tare mukaje ko?"
"Eh wlh, shaf namanta ko inane, kinsan anyi gine gine a wajen sai nake ganin kamar anginesa.?"
"Hehehe ai nasani, tuntuni nake roqon ALLAH yasa wani ya gine wajen yanda shikenan babu yanda za'a iya tonesa amma har yanzu wajen na nan fili ba'ayi gini wajen ba, shiyasa kullum nake sa ido awajen kar wani d'an ta tsinanniya yaje yatone manashi muboni mu lalace."
Cikin wani farincikin daya kasa b'oyuwa a fuskar baffa Ali ya taso daga d'an kishin gid'awar da yayi had'e da cewa.
"Da gaske ruqayya?, Kai Alhamdulillah wlh naji dad'i, a Ina ne?, Wane wajene ruqayya."
Binsa tayi da wani irin mugun kallo da zai tabbatar maka data fara zargin wani abu akansa kafin tace.
"Kai Ali, kallanni nan Kar nake kallonka, wato kaje 'yan iwan naka su lallashe maka baki don kawai sun taimaka ancire maka wannan 'yar qafar taka data gama rub'ewa shine kakeso a tonikke maganin, ka manta da wannan karon ba qafa zaka iya rasawa ba rayuwarka ko tawa gaba d'aya ko?, to wlh saidai su mutu bazan fad'i inda wajen yake ba, ban shiryawa mutuwa yanzu ba don haka kaji dashi can dakai dasu d'in, iyyeee! Wato sun turoka tunda karasa qafa d'aya bari su ida sallama rayuwarka don baqar mugunta da mugun nufi, to aniyarsu tabisu wlh, na maji dad'i daka mance don Ina baqin cikin lalacewar rayuwarka yanzu Ali, kazama raqumi da akala sai yanda akayi da kai wato?."
Taqarasa maganar had'e da fashewa da kuka tanaci gaba da cewa.
"Allah ya isa ga idrisu, da usmanun da baliksu, da waccan tsinanniyar ta tsallake (baba nusaiba) da waccan mokad'ad'd'iyar tsohuwar data nad'e waje d'aya ita Bata mutuba ita Bata rayuba, duk ita taja mana shiga wannan rayuwar da muke ciki yanzu data haifa tsinannen d'an daya zama silar guntule qafarka, wlh indai Ina raye su dashi har abada sai dai su haifo wani."
Shiru baffa Ali yayi yana kallonta cike da b'acin rai da wata irin tsanarta da bazai iya kwatanta adadin yawanta azuciyar saba, wato ita ba'ayi mata ALLAH ya isaba ita keyi har tana tsine masu, murmushin da yafi kuka ciwo yayi tare da cewa.
"Ali kacire damuwa mu zauna mu natsu musamo mafita, damuwar da kake qara cilla kanka aciki bafa zata haifama komaiba sai wahala, tunda dai har kayi nadama to kayi Imani da qaddararka mai kyau da marar kyau, in Sha ALLAH zaka samu mafita."
Nan ma kukan ya sake fashe masa dashi saida yayi daqyar yasamu suka koma zauren, Inna Bilkisu dake tsaye gefe ta shiga girgiza kai cike da tausayinsa, Wai yau alin da tasani ne fitinanne da hatsabibanci ke russunawa duniya haka, lallai rayuwar duniya ba komai bace kuma batada tabbas ko kad'an, sanin yana matuqar son fura yasa tashiga d'aki ta d'auko dawon da tasaye d'azu tunda taji yace bazai iya cin abincin ba ta dama masa takai masa acan zauren ya d'ago kai cikin sanyin murya had'e da cewa.
"Sannu balkisu, nagode ALLAH yasaka maki da alkhairi."
"Amin ya rabbi, ka d'aure kasha furar ko kad'an ce, ba a biyewa damuwa azauna da yunwa domin had'uwa sukeyi waje d'aya su illata mutum."
Har zata fita yakira sunanta tadawo, ya sake fashewa da kuka tare da roqonta tayafe masa abubuwan daya yimata don ALLAH, da yake mace ce mai raunin zuciya nan take sai itama tafashe da kukan tana fad'in.
"Ali nayafe maka duk abunda kayi mani wanda kasani da wanda baka sani ba duniya da lahira, kuma Ina roqon kaima ALLAH ya yafe maka ya dawo da hankalin iyalinka agareka ta zauna ta kula dakai kaima."
Girgiza kai kawai yayi don yasan inna ruqayya bazata tab'a hankalta ba sai ranar da duniya ta hankaltar da ita, "nagode sosai Bilkisu ALLAH ya albarkaci yaranki yakaresu da rud'in duniya."
Da ita har baffa Usman suka amsa da amin sannan tabar wajen, kallonsa baffa Usman yayi had'e da cewa.
"Ali idanfa kana tuna abubuwan da suka riga suka wuce to tabbas ka dingi kuka kenan har iya qarshen rayuwarka, Ina baka shawara kayi haquri ka godewa ALLAH daya ganar dakai kafin lokaci yaqure maka."
Saida ya goge kwallan da suka zubo masa sannan ya saki wata ajiyar zuciya had'e da cewa.
"Dole na zubda hawaye Usman, wallahi aduk lokacin da naga kuna hidima dani da yaran nan dake wajenku duk irin cin kashi da kuma mutunci da nayi maku sai naji waninirin nauyi da kunya sun dabai bayeni, nacutar daku amma gashi kunata kyautata mani, wlh da mutane zasu gane da sun daina cutarwa ga mutanen dake Shire da kyautata masu, don wannan abun da kike yimani shine mafi girman horon da kuke hukunta zuciyata dashi, zaifi sauqi ace cutar da mutum akayi kamar yanda ya cutar da adinga binsa da kyautatawa da kuma alkhairai domin yafi shiga kunya da nadamar da zuciyarsa zatayita d'awainiya da abubuwan daya aikata."
"Kamanta da komai, ni babu sauran zarginka ko kuma tsanarka araina, fatana ALLAH yayafe maka laifinka kuma yabamu mafita, din natabbata shi kad'aine zaisa yaya yasake baka damar jingina dashi akaro na biyu duk da dai tsananin b'acin rai yasa yakai ga yanke maka wannan hukunci amma inada yaqini akan zai sauko kuma ya yafe maka shima."
"ALLAH ya qaddara hakan, Amma girman laifina na cancanci hukuncin da yayi mani kuma koda ya gagara yafemun bayada laifi." Yaqara fashewa da wani kukan.
Haka sukaci gaba da maganganunsu baffa Usman naqara yimasa nasiha akan illar biyewa son zuciya da kuma sharrin duniya da rud'in shed'an har aka kira sallar magrib sukayi arwala suka wuce masallaci, bayan angama sallah baffa Usman yamiqe had'e da kallon baffa Ali yace.
"Bari naje wajen Yaya naga halin da yake ciki ina tsoron kar shima yashiga damuwa irin yanda kake ciki!"
"Shikenan bari nad'an gincira kafin akira sallar isha'i, seka dawo."
"To madallah, amma karka kwanta domin babu kyau bacci tsakanin sallar magrib da isha'i, annabinmu yayi hani ga hakan, zaifi kazauna kiyita yimasa sakati da zikiri da kuma hailala har akira sallar ko kuma ka d'auko qur'ani kayi tilawa, bari namaza naje na dawo."
Yana kaiwa nan yafice da sauri don baya son ya rasa jam'i shi kuma ya d'auko qur'aninsa yafara tilawa kamar yanda d'an uwansa ya shawartai.
Koda baffa Usman yaje gidan baffa ya iskoshi tsakar gida 'ya'yansa duka sun zagayesa anata fira ana dariya, murmushin jin dad'in ganinsa haka babu abunda yasamesa yayi had'e da qarasawa ciki yana fad'in.
"Allah ya taimaki uban d'iya yaja da tsawon rai." Yana wani d'aga hannu tare da dudduqawa kamar yanda fadawan sarki keyi gaba d'aya duk sukasa dariya hadda baffa tare da miqa masa hannu sukayi musabaha sannan yace.
"Ai kaine uban d'iya malan Usmanu ko yau kabar mani d'iyan baka so."
"Inaaa.. Yaya nakai ga manyan d'iya haka tubarkallah kace in barmaka, ai Abba kawai ne banayi shida aka yimani rashin kara akansa."
Gaishesa suka shigayi d'aya bayan d'aya yana amsawa kafin akawo ga Abba yamiqa masa hannu yana fad'in.
"Assalamu alaikum baffa barka da dare." Lokacin yanada shekara goma sha biyu.
Dariya baffa yayi had'e da kallon baffa Usman daya kama hannunsa yariqe gam yana dariya yace.
"Aminina kenan, gaisuwarsa ba irin tasu bace."
Nan shima Baffa Usman yayi zaunensa akaci gaba da firar dashi har aka kira sallar isha'i yamiqe da sauri had'e da yimasa sallama sannan yabar gidan, yaso yayi masa maganar baffa Ali amma yanda yaga farinciki kwance afuskokin gidan yasa yafasa don kada yarusa masu shi izuwa damuwa aransa yana yabawa 'yar 'yar uwar matar tasa data iya gusar da yanayin damuwar da yayan nasa yafita dashi d'azun alokaci d'aya, tabbas Babu abunda yakai matar qwarai samun kwanciya da cikakkiyar natsuwar namiji aduniya..
Bayan anqare sallah duk suka nufi gida suna tafe suna shawara akan maganar da baffa Ali yafad'a cewa ya samu mafita akan maganarsu ta d'azu, Inna ruqayya zasu tuntub'a tunda tare sukayi komai da ita ya tabbata ita bazata manta wajen ba, damuwar d'aya ce shine daqyar in zata amince tagwada masu wajen tunda tasan sharad'in da malamin tsibbon nasu yabayar, daga karshe dai baffa Ali yace abarshi da ita zai san yanda za'ayi ta gwada masa don kai tsaye idan aka fuskanceta da maganar bazata yarda ba, da haka suka shiga shiga ya tadda ita zaune tsakar d'aki da gani bata dad'e da dawowa wajen baran ba ta bubbud'e qafafuwa ta zube kud'ad'en da tasamo tana qidaya, sallama yayi har sau biyu bata tanka shiba sai da yayi ta uku tukuna ta d'ago kai cikin tsiwa irin ta fitinannun tsofaffin matannan tace.
"Kai nifa Ali ba nison tsarguwa, dolene amsa sallamar koko dai dolene, in banda gulma baka tashi dawowa ba sai yanzu da kaga ina kikkimtsa abunda ALLAH yabani, to ALLAH yasani idan ma da biyu kayi ko shishi (sisi) bazan baka ba, badai bazaka bara ba? To ni kuma bazan baka shishi (sisi) naba, in shigowa zakayi ka shigo bana son talla kawani hankad'e mani labule, dama haqoranta wasu duk sun fita shiyasa bata iya fad'an sisin da kyau take cewa shishi, batare daya tanka taba ya wucikkewarsa ya zauna gefen gado yana kallonta har tagama qidayar kud'inta sannan tajawo wata leda taciro lemu da biredi sai kuma nama atakarda tahauci abunta, qille bata raga ba har saida ta cinyesa tas batare data sammashi ko kad'an ba sannan tabuga gyatsarta tamiqe tana yimasa habaice habaice, dama shi kota bashi bazai karb'a ba don yasan haramun ne tunda roqa tayi ba bata akayi ba, kuma shi roqo baida kyau awani nassima an haramta yinsa inba da wata babbar lalura ba.
So yake ya d'auko mata zancen amma ganin abubuwan da takeyi yasa yarasa ta inama zai fara, can dai yayi qarfin hali ya daure cikin yanayin da bazata kawo komai ba yace
"Nikuwa ruqayya wai a inane muka binne maganin nan.", juyowa tayi daga kan gadonta data haye had'e da cewa.
"Lafiya kake tambayata?, Ina ai tare mukaje ko?"
"Eh wlh, shaf namanta ko inane, kinsan anyi gine gine a wajen sai nake ganin kamar anginesa.?"
"Hehehe ai nasani, tuntuni nake roqon ALLAH yasa wani ya gine wajen yanda shikenan babu yanda za'a iya tonesa amma har yanzu wajen na nan fili ba'ayi gini wajen ba, shiyasa kullum nake sa ido awajen kar wani d'an ta tsinanniya yaje yatone manashi muboni mu lalace."
Cikin wani farincikin daya kasa b'oyuwa a fuskar baffa Ali ya taso daga d'an kishin gid'awar da yayi had'e da cewa.
"Da gaske ruqayya?, Kai Alhamdulillah wlh naji dad'i, a Ina ne?, Wane wajene ruqayya."
Binsa tayi da wani irin mugun kallo da zai tabbatar maka data fara zargin wani abu akansa kafin tace.
"Kai Ali, kallanni nan Kar nake kallonka, wato kaje 'yan iwan naka su lallashe maka baki don kawai sun taimaka ancire maka wannan 'yar qafar taka data gama rub'ewa shine kakeso a tonikke maganin, ka manta da wannan karon ba qafa zaka iya rasawa ba rayuwarka ko tawa gaba d'aya ko?, to wlh saidai su mutu bazan fad'i inda wajen yake ba, ban shiryawa mutuwa yanzu ba don haka kaji dashi can dakai dasu d'in, iyyeee! Wato sun turoka tunda karasa qafa d'aya bari su ida sallama rayuwarka don baqar mugunta da mugun nufi, to aniyarsu tabisu wlh, na maji dad'i daka mance don Ina baqin cikin lalacewar rayuwarka yanzu Ali, kazama raqumi da akala sai yanda akayi da kai wato?."
Taqarasa maganar had'e da fashewa da kuka tanaci gaba da cewa.
"Allah ya isa ga idrisu, da usmanun da baliksu, da waccan tsinanniyar ta tsallake (baba nusaiba) da waccan mokad'ad'd'iyar tsohuwar data nad'e waje d'aya ita Bata mutuba ita Bata rayuba, duk ita taja mana shiga wannan rayuwar da muke ciki yanzu data haifa tsinannen d'an daya zama silar guntule qafarka, wlh indai Ina raye su dashi har abada sai dai su haifo wani."
Shiru baffa Ali yayi yana kallonta cike da b'acin rai da wata irin tsanarta da bazai iya kwatanta adadin yawanta azuciyar saba, wato ita ba'ayi mata ALLAH ya isaba ita keyi har tana tsine masu, murmushin da yafi kuka ciwo yayi tare da cewa.