Sashe 81
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba qaramar rawar gani Dr nura da Fatima ke takawa ba wajen kula da farinciki da kuma walwalar Rashida ba ita da d'anta, duk wani abu da take buqata basa bari har saita kai ga furta cewa tana so suke yimata, mutanene su day sukasan haqqin zaman takewa da kuma sanin kimar d'an Adam, ko kad'an abunsu baya rufe masu idanuwa balle ya had'a ka dasu, sosai suka nuna mata cewa dasu da ita duk abu d'aya ne babu wani banbanci don haka tanada 'yancin tayi rayuwarta yanda takeso acikin gidan ita da yaronta matuqar hakan bai sab'awa musulunci ba.
Hakan yasa tafara sakewa kamar yanda suke buqata saboda taga tasasu farinciki yanda suke qoqarin sata itama.
Sunada sati d'aya da dawowa Dr nura yaje ya sanar da iyayensa batun zaman Rashida agidansa da irin taimakon da yayi mata wanda daga qarshe har danginta suka roqesa akan tazauna wajensu nawani d'an lokaci kafin ALLAH yadawo da mijinta lafiya.
Sun jinjina al-amarin sosai har ammie nayi masa fad'an meyasa tun farkon faruwar al'amarin bai sanar dasu ba sai yanzu, gashi sanadiyar banzar tunaninsa ya haifar mata da rasa iyayenta wanda da ansanar dasu dawuri da duk haka bata faru ba, haquri yabata tare da fad'a mata iya qoqarin yin hakan da yayi alokacin amma ALLAH beyarda ba sanadiyar wannan rubutacciyar qaddarar daya tsaro masu.
Dady kuwa tunda Dr yafara bada labarin yake ganin kamancece niyarsa da nasu umma duk da dai bakomai yafad'a masu ba, jin dayayi Dr nura ya ambaci cewa ita mijin nata na qasar waje yaje karatu yasa ya janye hankalinsa daga wannan tunanin, a tsammaninsa ma yarinyar 'yar masu kud'ice don haka sai dai kawai ya nuna masa yanda yaji dad'in taimakon da yayi da kuma qara qarfafa masa wajen sanin kima da kuma darajar d'an Adam, ya sake horonsa akan ya taimaki duk wani mabuqaci shima ALLAH zai taimakesa domin shi alkhairi aduk inda kayishi to tabbas zai biyoka aduk inda kake.
Haka ammie itama ta sake gargad'insa akan yariqa sanar dasu duk wani abu dayasan yinsa zai iya basa wata matsala ko akasin haka saboda suriqa bashi shawarwarin daya kamata harma da taimako idan akwai buqatar yin hakan, yadena yin gaban kansa akan wasu abubuwa matuqar suna raye dominsu har yanzu yaro yake agaresu, ya matuqar jin dad'in nasihohin da suka yimasa kafin yayi madu sallama yawuce gida suna masu sanya masa albarka da addu'ar ALLAH ya albarkacesa da zuri'a d'ayyaba.
Zama mai cike da girmamawa da kuma mutunta juna ke tsakaninsu da Rashida, basuda matsala da ita haka itama batada wata matsala dasu, rayuwarsu sukeyi mai tsabta inganci da kuma nagarta har little Nuraddeen ya cika wata goma aduniya lokacin har yafara takawa Babu inda bai zuwa, yayi wayau sosai gwanin ban sha'awa dashi ga surutu, koda yafara iya magana da gwaggo yake kiran Rashida saboda sunan da yaji ana kiran mai aikin gidan dashi kenan sai yazata itama sunanta kenan yake kiranta dashi, Amma yanayin shaquwa da sabon da yayi da Fatima ita mama yake kiranta shi kuma Dr da Abba yake kiransa saboda tunda suka dawo kusan duka renonsa a hannunsa yakoma, iyakar Rashida dashi bashi nono sai wasu lokutta da idan uzuri ya gittowa Fatima sai tayi masa wanka da gyarashi, hatta bacci wani lokacin awajensu yakeyi ataqaice duk wata kulawa daya dace uwaye suyiwa 'ya'yansu su suke yimasa, kallo d'aya zakayi masa kasan d'an d'an 'yan gayune saboda irin gyaran da yake samu daga wajensu, wata irin mahaukaciyar soyayya sukeyi marar misaltuwa daga shi har mahaifiyarsa, idanko zasu fita sau goma ayini yadinga ihu kenan yana zallo har sai sun tafi dashi, ita abun har mamaki yake bata don ba qaramin shaquwa yayi dasu ba, Babu abunda ma yafi bata mamaki irin kud'in da suke kashikke masa aduk lokacin da suka fita dashi sai take tunanin kamar tad'ora masu hidima sosai akansa, lokacin data roqesu surage yimasu hidima kada abun yayi yawa nan take suka b'ata rai had'e da nuna mata rashin jin dad'insu akan haka, dole tabasu haquri taci gaba da yimasu addu'a suma ALLAH yakawo masu nasu 'ya'yan masu albarka kusa kusa kamar yanda tasaba akoda yaushe.
Hakama dady da ammie suna matuqar son yaron sosai don duk lokacin da Dr zasuje tare suke zuwa dashi, shi kuma baba randa yafara ganin yaron saida gabansa yafad'i saboda yanda ya hango tsantsar kamarsa da 'yarsa da kuma ummanta atare dashi, yadad'e yana tunanin anya wannan yaron ba jininsa bane kuwa?, Amma sanin cewa jikane ga alhaji tunda baisan alaqar dake tsakanin yaron da kuma Dr ba yasa yakama bakinsa yayi shiru daga bayama sai yashiga tambayar kansa taya hakan zai faru tunda yasan kosu waye iyayen yaron?.duk lokacin daya ga yaron sai yaji gabansa na tsananta fad'uwa, ji yake tamkar Rashidarsa ce hakan yasa yafara qoqarin jan yaron ajiki,
Dady ma ranar daya ga little kai tsaye yacewa ammie yana kama da umma tayi dariya had'e da cewa.
"Ikon ALLAH dama haka abun yake, qila idan anyo taliyo yanada alaqa da ita tunda dama mutane 'yan uwan junane idan an bincika."
Basu wani d'auki maganar da muhimmanci ba shiyasa suka barta abakin nan batare da tayi tsayi ba.
Yau da misalin qarfe biyar na marece Fatima tafito riqe da hannun little suna takawa ahankali kamar yanda take tafiya yasha manyan kayansa irin na cikakkun hausawa hadda babbar riga da hannuwa masu clips kai karantse kace babban mutumne, kansa saye da 'yar madaidaiciyar hula irin mai qube d'innan da takalma have cover yayi matuqar kyau sosai har yagaji, murmushi Rashida tayi had'e da cewa Masha ALLAH aranta kafin tace "Haba aunty, uncle fa nawaje yana jira kin tsaya biyewa tafiyar wannan yaron da sai magrib tawuce baku qaraso ba,"
"Eh munji dai, ai SANNU SANNU bata hana zuwa ko my boy."
Taqarasa maganar had'e da d'aukeshi sannan taqaraso wajen tana d'agawa Rashida gira tana dariya had'e da kallon little tace.
"To ya kikaga yarona?."
"Ba kyau, kuma am jealous." Rashida tabata amsa had'e da wucewa gaba tana dariya.
"Lallai ma maman boy, kawai kice dai jealous d'inne yahana kiga zallar kyan dake zuba anan.?"
Saida suka iso suka shiga cikin motar sannan itama Rashida ta shiga sukabar qofar gidan, bayan sun hau titi sunfara tafiya Dr nura ya kalli Fatima yanda tayi kyau ita da little tamkar ace d'anta ne yace.
"Wow..Masha ALLAH, matar yau kincini tukuici, wannan wankan na takwara dole yahau Instagram, yaro sai kace donsa aka halitto kayan nan na hausawa, gaskiya badon kar ace nayi sonkai da yawa ba da nace maman boy kinfi kowace uwa azamanin nan dacewa da kyakkyawan yaro kamar takwarana."
"Kai uncle to ai wannan zancen naka ga mamansa nan azaune ita kad'ai zata iya fahimtarsa amma nikam yanzu haka nahango yaron daya fishi kyau da komai akan titin nan."
"Jealousy jealousy.."
Fatima tafad'a tana dariya.
"Yawwa maman boy yaufa wajen su ammie zan kaiki kugaisa, tun satin can take cewa na kaiki wajensu kugaisa amma ko yaushe sai namanta saboda abubuwa da sukayi mani yawa, Yauma matar ce tatuna mani ganin Ina shirin tafiya can nida takwara shine nace tafad'a maki kigyara sai muje gaba d'aya, Ina fatan bamu takuraki ba ko?"
"Laaa..uncle wace irin takurawa, ai nima matsayin iyaye suke agareni kuma kamata yayi ace tuntuni nayi wannan tunanin na zuwa nagaishesu lura da irin saqon gaisuwar da akoda yaushe suke aiko mana dashi amma rashin kammaluwar cikakken tunani irin nawa yasa nakasa yin hakan, babu komai kuma naji dad'i sosai koba komai naje naga mahaifiyar da tayi sa'ar samun nagartaccin 'ya'yaye kamarku, inada yaqini akan cewa tafi kowa sa'ar samun surukar qwarai irin aunty Fatima kuma nasan tana alfahari da ita sosai.
"Hakane maman boy, mahaifiyata nason Fatima fiye da son da takeyimun, a kullum tana fad'a cewa itace cikar farincikin mu kuma hasken gidana." Yaqare maganar yana kallon Fatima data qura masa idanuwa had'e da d'aga mata gira.
Haka sukayita firarsu har suka isa qofar gidan wanda yayi daidai da shigowar baba yanufi sashen da aka basu.
••• ••• •••
Baffa kam tuni yagama haqura tare da fitar da rai akan komai, yanzu tunaninsa gaba d'aya yakoma akan d'ansa da tunda yatafi baya samunsa awaya kuma shi bai kiraba gashi yanzu kimanin watanni bakwai kenan da tafiyarsa,
Ganin baffa na neman shiga wata damuwar yasa baffa Usman yakoma wajen iyayen matarsa Inna Bilkisu akan zancen auren 'yar yayarta da akayi da baffa mai suna nusaiba, nan take aka fara shire shiren biki nan da sati mai zuwa, fenti marar tsada baffa Usman ya siyo don yanzu bashida isashshin kud'ad'en a hannunsa saboda lalurorin da sukayita fuskanta yasa akaje akayowa baffa awancan gidan inda yake zaune lokacin yana kasuwa, koda yadawo yatarar da anyi fenti kuma anmaida komai yanda yake ya tambayi baffa Usman yafad'a masa cewa ai zancen auren sane yatashi, tabbas yasan yanada buqatar natsuwa ahalin yanzu saidai bayada tunanin ta inda natsuwar zata zo masa, dole yana buqatar taimako takowace irin fuska don haka dole yasawa d'an uwansa ido yayi abunda yakamata wataqil hakan shine zai sama masa natsuwa.
Inna Bilkisu kuwa 'yan kud'in adashinta data karb'a tayiwa baffa magana yaqara mata wasu duk da kuwa basuda yawa tasa aka sawo mata akwati d'an madaidaici ta sayi atamfuna guda biyar masu sauqin kud'i da leshi d'aya mai d'an kyau da takalma kala d'aya da jikka d'aya sai hijab da mayafi shima qwaya d'ai d'aya, foda, turare, sabulu da 'yan sauran kwantsammai da basu taka kara suka kawo ba daidai gwargwado irin kayan auren da aka sani anayi aqauye takai amatsayin lefen da baffa yayiwa yarinyar.
Duk da kayan basuda yawa an amshesu hannu biyu cike da farinciki anata saka albarka.
Baffa Ali kuwa da Inna ruqayya yanda kukasan auren da baffa zaiyi abun kunyane haka sukabi gari duk inda suka zauna basuda tsogumin daya wuce wai baffa zai auri qaramar yarinya tsofai tsofai dashi don abun kunya bai isheshi ba, haka sukayita yad'a wannan maganar har ta zagaye garin, yayinda wasu ke kallon abun ba wani abune tunda ansaba yin hakan a qauyen wasu kuma suke kallon auren amatsayin abun kunyane agaresa.
Hakan yasa tafara sakewa kamar yanda suke buqata saboda taga tasasu farinciki yanda suke qoqarin sata itama.
Sunada sati d'aya da dawowa Dr nura yaje ya sanar da iyayensa batun zaman Rashida agidansa da irin taimakon da yayi mata wanda daga qarshe har danginta suka roqesa akan tazauna wajensu nawani d'an lokaci kafin ALLAH yadawo da mijinta lafiya.
Sun jinjina al-amarin sosai har ammie nayi masa fad'an meyasa tun farkon faruwar al'amarin bai sanar dasu ba sai yanzu, gashi sanadiyar banzar tunaninsa ya haifar mata da rasa iyayenta wanda da ansanar dasu dawuri da duk haka bata faru ba, haquri yabata tare da fad'a mata iya qoqarin yin hakan da yayi alokacin amma ALLAH beyarda ba sanadiyar wannan rubutacciyar qaddarar daya tsaro masu.
Dady kuwa tunda Dr yafara bada labarin yake ganin kamancece niyarsa da nasu umma duk da dai bakomai yafad'a masu ba, jin dayayi Dr nura ya ambaci cewa ita mijin nata na qasar waje yaje karatu yasa ya janye hankalinsa daga wannan tunanin, a tsammaninsa ma yarinyar 'yar masu kud'ice don haka sai dai kawai ya nuna masa yanda yaji dad'in taimakon da yayi da kuma qara qarfafa masa wajen sanin kima da kuma darajar d'an Adam, ya sake horonsa akan ya taimaki duk wani mabuqaci shima ALLAH zai taimakesa domin shi alkhairi aduk inda kayishi to tabbas zai biyoka aduk inda kake.
Haka ammie itama ta sake gargad'insa akan yariqa sanar dasu duk wani abu dayasan yinsa zai iya basa wata matsala ko akasin haka saboda suriqa bashi shawarwarin daya kamata harma da taimako idan akwai buqatar yin hakan, yadena yin gaban kansa akan wasu abubuwa matuqar suna raye dominsu har yanzu yaro yake agaresu, ya matuqar jin dad'in nasihohin da suka yimasa kafin yayi madu sallama yawuce gida suna masu sanya masa albarka da addu'ar ALLAH ya albarkacesa da zuri'a d'ayyaba.
Zama mai cike da girmamawa da kuma mutunta juna ke tsakaninsu da Rashida, basuda matsala da ita haka itama batada wata matsala dasu, rayuwarsu sukeyi mai tsabta inganci da kuma nagarta har little Nuraddeen ya cika wata goma aduniya lokacin har yafara takawa Babu inda bai zuwa, yayi wayau sosai gwanin ban sha'awa dashi ga surutu, koda yafara iya magana da gwaggo yake kiran Rashida saboda sunan da yaji ana kiran mai aikin gidan dashi kenan sai yazata itama sunanta kenan yake kiranta dashi, Amma yanayin shaquwa da sabon da yayi da Fatima ita mama yake kiranta shi kuma Dr da Abba yake kiransa saboda tunda suka dawo kusan duka renonsa a hannunsa yakoma, iyakar Rashida dashi bashi nono sai wasu lokutta da idan uzuri ya gittowa Fatima sai tayi masa wanka da gyarashi, hatta bacci wani lokacin awajensu yakeyi ataqaice duk wata kulawa daya dace uwaye suyiwa 'ya'yansu su suke yimasa, kallo d'aya zakayi masa kasan d'an d'an 'yan gayune saboda irin gyaran da yake samu daga wajensu, wata irin mahaukaciyar soyayya sukeyi marar misaltuwa daga shi har mahaifiyarsa, idanko zasu fita sau goma ayini yadinga ihu kenan yana zallo har sai sun tafi dashi, ita abun har mamaki yake bata don ba qaramin shaquwa yayi dasu ba, Babu abunda ma yafi bata mamaki irin kud'in da suke kashikke masa aduk lokacin da suka fita dashi sai take tunanin kamar tad'ora masu hidima sosai akansa, lokacin data roqesu surage yimasu hidima kada abun yayi yawa nan take suka b'ata rai had'e da nuna mata rashin jin dad'insu akan haka, dole tabasu haquri taci gaba da yimasu addu'a suma ALLAH yakawo masu nasu 'ya'yan masu albarka kusa kusa kamar yanda tasaba akoda yaushe.
Hakama dady da ammie suna matuqar son yaron sosai don duk lokacin da Dr zasuje tare suke zuwa dashi, shi kuma baba randa yafara ganin yaron saida gabansa yafad'i saboda yanda ya hango tsantsar kamarsa da 'yarsa da kuma ummanta atare dashi, yadad'e yana tunanin anya wannan yaron ba jininsa bane kuwa?, Amma sanin cewa jikane ga alhaji tunda baisan alaqar dake tsakanin yaron da kuma Dr ba yasa yakama bakinsa yayi shiru daga bayama sai yashiga tambayar kansa taya hakan zai faru tunda yasan kosu waye iyayen yaron?.duk lokacin daya ga yaron sai yaji gabansa na tsananta fad'uwa, ji yake tamkar Rashidarsa ce hakan yasa yafara qoqarin jan yaron ajiki,
Dady ma ranar daya ga little kai tsaye yacewa ammie yana kama da umma tayi dariya had'e da cewa.
"Ikon ALLAH dama haka abun yake, qila idan anyo taliyo yanada alaqa da ita tunda dama mutane 'yan uwan junane idan an bincika."
Basu wani d'auki maganar da muhimmanci ba shiyasa suka barta abakin nan batare da tayi tsayi ba.
Yau da misalin qarfe biyar na marece Fatima tafito riqe da hannun little suna takawa ahankali kamar yanda take tafiya yasha manyan kayansa irin na cikakkun hausawa hadda babbar riga da hannuwa masu clips kai karantse kace babban mutumne, kansa saye da 'yar madaidaiciyar hula irin mai qube d'innan da takalma have cover yayi matuqar kyau sosai har yagaji, murmushi Rashida tayi had'e da cewa Masha ALLAH aranta kafin tace "Haba aunty, uncle fa nawaje yana jira kin tsaya biyewa tafiyar wannan yaron da sai magrib tawuce baku qaraso ba,"
"Eh munji dai, ai SANNU SANNU bata hana zuwa ko my boy."
Taqarasa maganar had'e da d'aukeshi sannan taqaraso wajen tana d'agawa Rashida gira tana dariya had'e da kallon little tace.
"To ya kikaga yarona?."
"Ba kyau, kuma am jealous." Rashida tabata amsa had'e da wucewa gaba tana dariya.
"Lallai ma maman boy, kawai kice dai jealous d'inne yahana kiga zallar kyan dake zuba anan.?"
Saida suka iso suka shiga cikin motar sannan itama Rashida ta shiga sukabar qofar gidan, bayan sun hau titi sunfara tafiya Dr nura ya kalli Fatima yanda tayi kyau ita da little tamkar ace d'anta ne yace.
"Wow..Masha ALLAH, matar yau kincini tukuici, wannan wankan na takwara dole yahau Instagram, yaro sai kace donsa aka halitto kayan nan na hausawa, gaskiya badon kar ace nayi sonkai da yawa ba da nace maman boy kinfi kowace uwa azamanin nan dacewa da kyakkyawan yaro kamar takwarana."
"Kai uncle to ai wannan zancen naka ga mamansa nan azaune ita kad'ai zata iya fahimtarsa amma nikam yanzu haka nahango yaron daya fishi kyau da komai akan titin nan."
"Jealousy jealousy.."
Fatima tafad'a tana dariya.
"Yawwa maman boy yaufa wajen su ammie zan kaiki kugaisa, tun satin can take cewa na kaiki wajensu kugaisa amma ko yaushe sai namanta saboda abubuwa da sukayi mani yawa, Yauma matar ce tatuna mani ganin Ina shirin tafiya can nida takwara shine nace tafad'a maki kigyara sai muje gaba d'aya, Ina fatan bamu takuraki ba ko?"
"Laaa..uncle wace irin takurawa, ai nima matsayin iyaye suke agareni kuma kamata yayi ace tuntuni nayi wannan tunanin na zuwa nagaishesu lura da irin saqon gaisuwar da akoda yaushe suke aiko mana dashi amma rashin kammaluwar cikakken tunani irin nawa yasa nakasa yin hakan, babu komai kuma naji dad'i sosai koba komai naje naga mahaifiyar da tayi sa'ar samun nagartaccin 'ya'yaye kamarku, inada yaqini akan cewa tafi kowa sa'ar samun surukar qwarai irin aunty Fatima kuma nasan tana alfahari da ita sosai.
"Hakane maman boy, mahaifiyata nason Fatima fiye da son da takeyimun, a kullum tana fad'a cewa itace cikar farincikin mu kuma hasken gidana." Yaqare maganar yana kallon Fatima data qura masa idanuwa had'e da d'aga mata gira.
Haka sukayita firarsu har suka isa qofar gidan wanda yayi daidai da shigowar baba yanufi sashen da aka basu.
••• ••• •••
Baffa kam tuni yagama haqura tare da fitar da rai akan komai, yanzu tunaninsa gaba d'aya yakoma akan d'ansa da tunda yatafi baya samunsa awaya kuma shi bai kiraba gashi yanzu kimanin watanni bakwai kenan da tafiyarsa,
Ganin baffa na neman shiga wata damuwar yasa baffa Usman yakoma wajen iyayen matarsa Inna Bilkisu akan zancen auren 'yar yayarta da akayi da baffa mai suna nusaiba, nan take aka fara shire shiren biki nan da sati mai zuwa, fenti marar tsada baffa Usman ya siyo don yanzu bashida isashshin kud'ad'en a hannunsa saboda lalurorin da sukayita fuskanta yasa akaje akayowa baffa awancan gidan inda yake zaune lokacin yana kasuwa, koda yadawo yatarar da anyi fenti kuma anmaida komai yanda yake ya tambayi baffa Usman yafad'a masa cewa ai zancen auren sane yatashi, tabbas yasan yanada buqatar natsuwa ahalin yanzu saidai bayada tunanin ta inda natsuwar zata zo masa, dole yana buqatar taimako takowace irin fuska don haka dole yasawa d'an uwansa ido yayi abunda yakamata wataqil hakan shine zai sama masa natsuwa.
Inna Bilkisu kuwa 'yan kud'in adashinta data karb'a tayiwa baffa magana yaqara mata wasu duk da kuwa basuda yawa tasa aka sawo mata akwati d'an madaidaici ta sayi atamfuna guda biyar masu sauqin kud'i da leshi d'aya mai d'an kyau da takalma kala d'aya da jikka d'aya sai hijab da mayafi shima qwaya d'ai d'aya, foda, turare, sabulu da 'yan sauran kwantsammai da basu taka kara suka kawo ba daidai gwargwado irin kayan auren da aka sani anayi aqauye takai amatsayin lefen da baffa yayiwa yarinyar.
Duk da kayan basuda yawa an amshesu hannu biyu cike da farinciki anata saka albarka.
Baffa Ali kuwa da Inna ruqayya yanda kukasan auren da baffa zaiyi abun kunyane haka sukabi gari duk inda suka zauna basuda tsogumin daya wuce wai baffa zai auri qaramar yarinya tsofai tsofai dashi don abun kunya bai isheshi ba, haka sukayita yad'a wannan maganar har ta zagaye garin, yayinda wasu ke kallon abun ba wani abune tunda ansaba yin hakan a qauyen wasu kuma suke kallon auren amatsayin abun kunyane agaresa.