Sashe 90
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dawowa cikin falon baba yayi fuskarsa d'auke da farinciki ya taya su hajia murna had'e da fatan ALLAH ya sauketa lafiya sannan yajuya yafita.
Miqewa dady yayi shima had'e da cewa.
"Dota congrat, ALLAH yakawo mana rayayyi masu albarka." Sannn shima yajuya yafice, ammie na dariya tasa hannu ta d'ago fuskar Fatima da tayi sharkaf da hawaye tana fad'in.
"Kai 'yata wannan duk kukan farincikine ko kuma na shagwab'a ne akeyiwa ammie ankusa zama mama." Kasa tanka mata tayi saima faman share qwallar da takeyi tana wasa da gefen hijab d'inta had'e da sissinne kai qasa, karo nafarko kenan arayuwarta data fara jin kunyar ammie irin haka, arayuwa babu abunda take b'oyewa ammie, ta d'auketa tamkar uwar data haifeta da cikinta, hatta wani abun cikin rayuwr aure idan Bata sani ba ita take tambaya tafad'a mata, haka ab'angaren kayan jiki na gyaran mata duka ammie nahad'a mata tabata kuma tayi mata bayani batare da taji kunyarta ba, sai gashi yau gaba d'aya takasa d'aga kai takalli ammie su had'a ido.
Murmushi irin na manya ammie tayi had'e da cewa, "ikon ALLAH, karmuyi haka dake 'yata, kisaki jikinki ni mahaifiyarkice don haka dena wani jin kunya akan wannan abun farinciki daya kamata muyi sharing happiness d'inmu atare, let celebrate together my dota bawani abubane, show me how much appy you feel about this, i will support you and make you enjoy it better kinji ko?."
Ahankali tad'ago kai tana kallon ammie hawaye nazubo mata afuska.
"I couldn't believe ammie, ammie ashe nima zan haihu ba juya bace ni kamar yanda ake fad'a, Ashe nima zan zama uwa am...?"
Kasa qarasawa tayi sakamakon kukan farinciki da yaci qarfinta, Bata tab'a kawowa kusa cewa zata haihuba, Bata tab'a sama ranta tana da ciki ba duka da dai Bata tab'a cire tsammani da rahamar ALLAH ba, ako yaushe cikin sa rai take komai daren dad'ewa zata haihu itama in ALLAH ya yarda.
Cike da tausayinta ammie tajawota ajiki ta rungume tana fad'in.
"Ya isa haka 'yatah, just blieve it, dama haka ALLAH yake, yakan lullub'e bayinsa da rahamarsa a lokacin da basu tab'a tsammani ba, kuma yakan dubi zukatan bayinsa da sukayi Imani dashi suka kyautata al'amurransu ya share masu hawayensu, wannan shine abunda nayita fad'a maki cewa idan lokaci yayi bazato ba tsammani zakiga abun kamar qyaftawar gira, Kuma nafad'a maki tunda dai har akece lafiyanki qalaw to kiyi haquri domin SANNU SANNU bata hana zuwa....gashi naki ALLAH yakawo ijaba har kin iso ko kuwa?"
Tafad'a tana d'an turo idanuwanta kad'an tana dariya alamar tana jiran amsa.
Jijjiga kai tashigayi alamar tabbatar mata da cewa hak ne ammie tace.
"To mugodewa ALLAH ba kuka zakiyi ba kinji ko?, Yanzu fad'amun me kike son ci?"
Rufe fuska tayi ammie nadariya tamiqe tana fad'in.
"Ko zakici wainar fulawa nayi maki?"
Ta girgiza kai had'e da cewa.
"A'a ammie eba dai zanci."
Turo idanuwa ammaie tayi had'e da cewa.
"Tofah, kice maigidan nawa d'an yarbawa ne?"
Duk sukasa dariya harda Dr nura da tun d'azu ke tsaye abakin qofa yace.
"Ai kuwa ammie da yaci sunan qudusu" yafad'a kamar yanda yarbawa ke kiran sunan suka sake sa dariya atare, can batare daya ankareba ammie takamo kunnensa had'e da murd'ewa tana fad'in.
"Son yanzu rashin kunyarka har yakai da kanka kake fad'an 'yata nada juna biyu kuma ka taso mani ita agaba, To Ida cikashe rashin kunyar taka ka fad'amun ko how many month ne?,"
Fatima na ganin haka ta tashi tashigewarta bedroom d'in mom tana murmushi, komai na surukar tata cike yake da burgewa da kuma ban sha'awa, ko kad'an batada wata matsala komai nata tanayinsa da cikakkiyar wayewar da babu qazanta acikinta.
"Awwwshhh..ammie da zafi fa."
"Nasani mana, bakai rashin kunya ba?"
"Kai mom, albishir nefa nayi maku, ALLAH badon baba ba sai kun cike mani check tukuna zan fad'a, Ashe laifine nayi bansani ba, amma ita data azawa mutane kuka Ina gani sai wani lallashinta akeyi ana murmushi." Yafad'a yana turo baki sai kace wani qaramin yaro.
Murmushi tayi had'e da sakinsa tace.
"Srry kaji ko son, tsantsar farincikinne har yayi mani over shiyasa nanemi regesa akanka, congrat soon zaka shiga next level arayuwa, wato mtakin zama uba bayan magidanci, ubangiji ALLAH yayi maku albarka yabamu rayayye."
"Amin ammien mu" yafad'a yana rungumeta.
Baba kuwa koda yakoma sashensa acan ya tarar da Dr nura suna gaisaw da umma da Rashida yana basu labarin jiya a asibiti suka kwana saboda zazzab'in daya tasowa Fatima har saida aka qara mata ruwa, baikai ga fad'a masu zancen cikin ba baba yashigo yamiqe zai fita baba ya tsayar dashi yake sanar dashi batun tafiyar da zaiyi kano, nan take Dr yaji tafiyar bata kwanta masa ba, yayi iya qoqarinsa naganin ya hana baba tafiyar har zuwa banda gobe idan zaije wajen aiki suwuce tare amma yakafe kai da fata shidai ya barshi ya tafi ai yau zai dawo, hakan yasa babu yanda ya iya dole sukayi sallama akan idan zai tafi ya aika Rashida yakirawosa zai koma wajen ammie sai ya ajiyeshi tasha sannan yabar sashen yanajin wani irin.
Baba kuwa zaunawa yayi suka sake d'an tab'a hira dasu umma yanata zolayarta wai yanzu idonta sun bud'e tadena kunyar Rashida amatsayinta na 'yarta tafari ashe b'oyewa takeyi tana sonta sosai sunata dariya.
Daga nan kuma yajuya akalar firar tasu izuwa yimasu nasiha akan rayuwar duniya sai kace wanda akace idan yatafi bazai dawo ba, bayan yagama umma tayi ajiyar zuciya had'e da cewa.
"Malan nifa duk jikina yamutu wlh, nidai don ALLAH kabar zancen tafiyarnan har zuwa wani lokacin."
Murmushi yayi had'e da cewa
"Karki manta sau da yawa bama son abu sai kiga ALLAH yasanya alkhairi sosai acikinsa, kika San alkhairan da wannan tafiyar zata jawo mana, qilama 'yar qanwa zan samomaki shiyasa duk kikabi kika tada hankalinki akanta." Yaqarasa maganar cikin sigar zolaya yana dariya had'e da miqewa yana d'auke da litte,
"Rana nayi bari na hanzarta yau nake son nadawo in sha ALLAH, Rashida jeki kikira Dr ni kam nad'au harma."
Gaban Rashida ne taji yafad'i da sauri tace.
"Baba kayi haquri kuwuce da uncle banda gobe."
"Ikon ALLAH, har dake Rashida? Bakyason sanin halin da mijinki da surukarki suke ciki halan?"
"A'a baba, ni kawai..."
Saurin dakatar da ita yayi tahanyar cewa "maza jeki kice Ina jiransa."
Har takusa fita yakira sunanta had'e da cewa.
"Dawo nayi maku albishir ni namanta, maman Rashida matar Dr fa tasamu qaruwa."
"Da gaske baba?" Rashida tafad'a cike da farinciki tare da ficewa da kad'an ma tafad'i garin sauri, umma kuwa Alhamdulillah tace tana fad'in "ALLAHU AKBAR, ALLAH maji roqon bayinsa, kai madalla bari naje nataya hajia murna."
Kusan tare da ita suka fita yana maijin wani sanyi aransa saboda yanayin farincikin da yaga ya bayyana a fuskarsu wanda hakn baqaramin tasiri yayi ba wajen qara masa natsuwa azuciya.....
_Godiya agareku masoya masu karamci da halacci bisa bibiyar lafiyata da kukayi, nagode sosai ALLAH yabar tare, maman ameera da ummu sauda ban manta daku ba, kunnuna kulawa agareni kuma jazakumullahu bikhair, fatan alkhairi aduk inda kuke👍🏻_
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___68💎
Saida 'yan uwan baba suka iso sannan akayimasa wanka aka sallaci gawarsa aka kaishi gidansa nagaskiya, a yanda mutane suka taru sukayi dandazo wajen sallar jana'izarsa kai ka dauka wani riqaqqen mai mulkine ko sarauta ko kuma wani hamshaqin malami, ALLAHU AKBAR, shiyasa akoda yaushe akeson mutum yazama mai sanyin hali da kyautata zamantakewa dtsakaninsa da mutane, duk da baba ba d'an asalin mazaunin cikin garin bane, kyakkyawan halayensa sun biyosa har zuwa qasarsa inda aka rufesa, bayada wani tarin arziqi kuma bai kasance wani sananne ba acikin garin da shekara d'aya kacal yayi acikinsa amma soyayyarsa ga ALLAH da kuma kyautata zaman takewarsa ga mutane yasa ubangijinsa ya soshi kuma yasa al'ummah ta soshi, babban abunda zaisa a kyautata masa zato shine yanda ruwa ke bulbulowa awajen haqar kabarinsa, har kusan sau biyu ana canza masa wani kabarin amma kowane aka haqo haka ake riskarsa, a dole aka d'aukesa akasashi hakanan acikinsu mutane namasu yabawa da ni'imarsa da ALLAH yayi masa tun akabari, duk inda kaduba cikin maqabartar cike yake da mutane ta ko ina da sukazo kawosa.
Bayan andawo su baba balarabe sukaje sukaa yimasu umma nasiha akan sud'au haquri da tsarin qaddarar da ALLAH yayi masu akan d'an uwan nasu domin yanda yasamu jama'a suna kyautata masa zato had'e da yima junansu gaisuwa.
Kwanan su baba balarabe uku sannan suka fara maganar komawarsu tunda anyi masa addu'ar uku, lokacin da sukaje wajen dady yimasa sallama akan zasu tafi kuma suna son suwuce da iyalan marigayin tunda dama shine jigonsu nazama garin kuma ALLAH yakarb'i abunsa sai dady yayi gyaran murya had'e da sake yimasu gaisuwar rashin d'an uwan nasu akaro na ba adadi sannan yace.
"Malan balarabe Ina son in roqeki wata alfarma awajenku idan zaku iya"
"Munaji alhaji ALLAH yasa batafi qarfinmu ba."
"Eh to! Banace haka ba amma Ina son ne idan har kun amince kubar iyalan marigayi anan har zuwa lokacin da zata gama takaba, nayi maku alqawarin cewa zan kula maku dasu bisa amana har zuwa lokacin idan ALLAH yabamu aron rayuwa."
Miqewa dady yayi shima had'e da cewa.
"Dota congrat, ALLAH yakawo mana rayayyi masu albarka." Sannn shima yajuya yafice, ammie na dariya tasa hannu ta d'ago fuskar Fatima da tayi sharkaf da hawaye tana fad'in.
"Kai 'yata wannan duk kukan farincikine ko kuma na shagwab'a ne akeyiwa ammie ankusa zama mama." Kasa tanka mata tayi saima faman share qwallar da takeyi tana wasa da gefen hijab d'inta had'e da sissinne kai qasa, karo nafarko kenan arayuwarta data fara jin kunyar ammie irin haka, arayuwa babu abunda take b'oyewa ammie, ta d'auketa tamkar uwar data haifeta da cikinta, hatta wani abun cikin rayuwr aure idan Bata sani ba ita take tambaya tafad'a mata, haka ab'angaren kayan jiki na gyaran mata duka ammie nahad'a mata tabata kuma tayi mata bayani batare da taji kunyarta ba, sai gashi yau gaba d'aya takasa d'aga kai takalli ammie su had'a ido.
Murmushi irin na manya ammie tayi had'e da cewa, "ikon ALLAH, karmuyi haka dake 'yata, kisaki jikinki ni mahaifiyarkice don haka dena wani jin kunya akan wannan abun farinciki daya kamata muyi sharing happiness d'inmu atare, let celebrate together my dota bawani abubane, show me how much appy you feel about this, i will support you and make you enjoy it better kinji ko?."
Ahankali tad'ago kai tana kallon ammie hawaye nazubo mata afuska.
"I couldn't believe ammie, ammie ashe nima zan haihu ba juya bace ni kamar yanda ake fad'a, Ashe nima zan zama uwa am...?"
Kasa qarasawa tayi sakamakon kukan farinciki da yaci qarfinta, Bata tab'a kawowa kusa cewa zata haihuba, Bata tab'a sama ranta tana da ciki ba duka da dai Bata tab'a cire tsammani da rahamar ALLAH ba, ako yaushe cikin sa rai take komai daren dad'ewa zata haihu itama in ALLAH ya yarda.
Cike da tausayinta ammie tajawota ajiki ta rungume tana fad'in.
"Ya isa haka 'yatah, just blieve it, dama haka ALLAH yake, yakan lullub'e bayinsa da rahamarsa a lokacin da basu tab'a tsammani ba, kuma yakan dubi zukatan bayinsa da sukayi Imani dashi suka kyautata al'amurransu ya share masu hawayensu, wannan shine abunda nayita fad'a maki cewa idan lokaci yayi bazato ba tsammani zakiga abun kamar qyaftawar gira, Kuma nafad'a maki tunda dai har akece lafiyanki qalaw to kiyi haquri domin SANNU SANNU bata hana zuwa....gashi naki ALLAH yakawo ijaba har kin iso ko kuwa?"
Tafad'a tana d'an turo idanuwanta kad'an tana dariya alamar tana jiran amsa.
Jijjiga kai tashigayi alamar tabbatar mata da cewa hak ne ammie tace.
"To mugodewa ALLAH ba kuka zakiyi ba kinji ko?, Yanzu fad'amun me kike son ci?"
Rufe fuska tayi ammie nadariya tamiqe tana fad'in.
"Ko zakici wainar fulawa nayi maki?"
Ta girgiza kai had'e da cewa.
"A'a ammie eba dai zanci."
Turo idanuwa ammaie tayi had'e da cewa.
"Tofah, kice maigidan nawa d'an yarbawa ne?"
Duk sukasa dariya harda Dr nura da tun d'azu ke tsaye abakin qofa yace.
"Ai kuwa ammie da yaci sunan qudusu" yafad'a kamar yanda yarbawa ke kiran sunan suka sake sa dariya atare, can batare daya ankareba ammie takamo kunnensa had'e da murd'ewa tana fad'in.
"Son yanzu rashin kunyarka har yakai da kanka kake fad'an 'yata nada juna biyu kuma ka taso mani ita agaba, To Ida cikashe rashin kunyar taka ka fad'amun ko how many month ne?,"
Fatima na ganin haka ta tashi tashigewarta bedroom d'in mom tana murmushi, komai na surukar tata cike yake da burgewa da kuma ban sha'awa, ko kad'an batada wata matsala komai nata tanayinsa da cikakkiyar wayewar da babu qazanta acikinta.
"Awwwshhh..ammie da zafi fa."
"Nasani mana, bakai rashin kunya ba?"
"Kai mom, albishir nefa nayi maku, ALLAH badon baba ba sai kun cike mani check tukuna zan fad'a, Ashe laifine nayi bansani ba, amma ita data azawa mutane kuka Ina gani sai wani lallashinta akeyi ana murmushi." Yafad'a yana turo baki sai kace wani qaramin yaro.
Murmushi tayi had'e da sakinsa tace.
"Srry kaji ko son, tsantsar farincikinne har yayi mani over shiyasa nanemi regesa akanka, congrat soon zaka shiga next level arayuwa, wato mtakin zama uba bayan magidanci, ubangiji ALLAH yayi maku albarka yabamu rayayye."
"Amin ammien mu" yafad'a yana rungumeta.
Baba kuwa koda yakoma sashensa acan ya tarar da Dr nura suna gaisaw da umma da Rashida yana basu labarin jiya a asibiti suka kwana saboda zazzab'in daya tasowa Fatima har saida aka qara mata ruwa, baikai ga fad'a masu zancen cikin ba baba yashigo yamiqe zai fita baba ya tsayar dashi yake sanar dashi batun tafiyar da zaiyi kano, nan take Dr yaji tafiyar bata kwanta masa ba, yayi iya qoqarinsa naganin ya hana baba tafiyar har zuwa banda gobe idan zaije wajen aiki suwuce tare amma yakafe kai da fata shidai ya barshi ya tafi ai yau zai dawo, hakan yasa babu yanda ya iya dole sukayi sallama akan idan zai tafi ya aika Rashida yakirawosa zai koma wajen ammie sai ya ajiyeshi tasha sannan yabar sashen yanajin wani irin.
Baba kuwa zaunawa yayi suka sake d'an tab'a hira dasu umma yanata zolayarta wai yanzu idonta sun bud'e tadena kunyar Rashida amatsayinta na 'yarta tafari ashe b'oyewa takeyi tana sonta sosai sunata dariya.
Daga nan kuma yajuya akalar firar tasu izuwa yimasu nasiha akan rayuwar duniya sai kace wanda akace idan yatafi bazai dawo ba, bayan yagama umma tayi ajiyar zuciya had'e da cewa.
"Malan nifa duk jikina yamutu wlh, nidai don ALLAH kabar zancen tafiyarnan har zuwa wani lokacin."
Murmushi yayi had'e da cewa
"Karki manta sau da yawa bama son abu sai kiga ALLAH yasanya alkhairi sosai acikinsa, kika San alkhairan da wannan tafiyar zata jawo mana, qilama 'yar qanwa zan samomaki shiyasa duk kikabi kika tada hankalinki akanta." Yaqarasa maganar cikin sigar zolaya yana dariya had'e da miqewa yana d'auke da litte,
"Rana nayi bari na hanzarta yau nake son nadawo in sha ALLAH, Rashida jeki kikira Dr ni kam nad'au harma."
Gaban Rashida ne taji yafad'i da sauri tace.
"Baba kayi haquri kuwuce da uncle banda gobe."
"Ikon ALLAH, har dake Rashida? Bakyason sanin halin da mijinki da surukarki suke ciki halan?"
"A'a baba, ni kawai..."
Saurin dakatar da ita yayi tahanyar cewa "maza jeki kice Ina jiransa."
Har takusa fita yakira sunanta had'e da cewa.
"Dawo nayi maku albishir ni namanta, maman Rashida matar Dr fa tasamu qaruwa."
"Da gaske baba?" Rashida tafad'a cike da farinciki tare da ficewa da kad'an ma tafad'i garin sauri, umma kuwa Alhamdulillah tace tana fad'in "ALLAHU AKBAR, ALLAH maji roqon bayinsa, kai madalla bari naje nataya hajia murna."
Kusan tare da ita suka fita yana maijin wani sanyi aransa saboda yanayin farincikin da yaga ya bayyana a fuskarsu wanda hakn baqaramin tasiri yayi ba wajen qara masa natsuwa azuciya.....
_Godiya agareku masoya masu karamci da halacci bisa bibiyar lafiyata da kukayi, nagode sosai ALLAH yabar tare, maman ameera da ummu sauda ban manta daku ba, kunnuna kulawa agareni kuma jazakumullahu bikhair, fatan alkhairi aduk inda kuke👍🏻_
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___68💎
Saida 'yan uwan baba suka iso sannan akayimasa wanka aka sallaci gawarsa aka kaishi gidansa nagaskiya, a yanda mutane suka taru sukayi dandazo wajen sallar jana'izarsa kai ka dauka wani riqaqqen mai mulkine ko sarauta ko kuma wani hamshaqin malami, ALLAHU AKBAR, shiyasa akoda yaushe akeson mutum yazama mai sanyin hali da kyautata zamantakewa dtsakaninsa da mutane, duk da baba ba d'an asalin mazaunin cikin garin bane, kyakkyawan halayensa sun biyosa har zuwa qasarsa inda aka rufesa, bayada wani tarin arziqi kuma bai kasance wani sananne ba acikin garin da shekara d'aya kacal yayi acikinsa amma soyayyarsa ga ALLAH da kuma kyautata zaman takewarsa ga mutane yasa ubangijinsa ya soshi kuma yasa al'ummah ta soshi, babban abunda zaisa a kyautata masa zato shine yanda ruwa ke bulbulowa awajen haqar kabarinsa, har kusan sau biyu ana canza masa wani kabarin amma kowane aka haqo haka ake riskarsa, a dole aka d'aukesa akasashi hakanan acikinsu mutane namasu yabawa da ni'imarsa da ALLAH yayi masa tun akabari, duk inda kaduba cikin maqabartar cike yake da mutane ta ko ina da sukazo kawosa.
Bayan andawo su baba balarabe sukaje sukaa yimasu umma nasiha akan sud'au haquri da tsarin qaddarar da ALLAH yayi masu akan d'an uwan nasu domin yanda yasamu jama'a suna kyautata masa zato had'e da yima junansu gaisuwa.
Kwanan su baba balarabe uku sannan suka fara maganar komawarsu tunda anyi masa addu'ar uku, lokacin da sukaje wajen dady yimasa sallama akan zasu tafi kuma suna son suwuce da iyalan marigayin tunda dama shine jigonsu nazama garin kuma ALLAH yakarb'i abunsa sai dady yayi gyaran murya had'e da sake yimasu gaisuwar rashin d'an uwan nasu akaro na ba adadi sannan yace.
"Malan balarabe Ina son in roqeki wata alfarma awajenku idan zaku iya"
"Munaji alhaji ALLAH yasa batafi qarfinmu ba."
"Eh to! Banace haka ba amma Ina son ne idan har kun amince kubar iyalan marigayi anan har zuwa lokacin da zata gama takaba, nayi maku alqawarin cewa zan kula maku dasu bisa amana har zuwa lokacin idan ALLAH yabamu aron rayuwa."