Sashe 49
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yaya Ashe jikin nura haka yazama, ni yanzu yaran gari sukaje suna fad'amun cewa ai kunanan asibiti da nura ya zauce saboda b'atan matarsa"
"To kadai gani Ali, jarabawar da ALLAH yad'oro muna kenan! Ubangiji ALLAH yabamu ikon canyeta."
"Amin Yaya, Amma to ba wannan ba yakamata yaronnan yasawa ransa salama, idan ALLAH yatsaro za'aga yarinyarnan to za'a ganta, in Kuma ALLAH be nufa ba to yayi haquri basai yaje ya illata kns ba zai samu wata matar tunda ba ita kad'aice mace ba, mata ne gasunan ko ina sai yazab'a ya darje, nan kusa ba nesa ba ga 'yar uwarsa nan muneera sai tamaye masa gurbinta ai inaga shikenan ko?"
Cike da b'acin rai baffa ya nufosa had'e da shaqe wuyansa ya had'a da jikin bango. "Aliyu dama kai bakada hankali ban sani ba? Mekake nufi da idan ba'a ganeta ba? Wlh damuwata tafi yawa akan b'atar yarinyar nan fiye da halinda Nuraddeen ke ciki domin nasan cewa ganinta ne kad'ai zai kawo masa sassaucin wannan halin da yake ciki saboda itace farincikinsa, shine kake fatar kada aganeta saboda ita d'in ba 'yarka bace?, Yaqarasa maganar cikin d'aga murya tare da qara shaqesa tayanda ko lumfashi mai kyau baya iyayi, kakarin d'aya farayi ne yasa baffa da likita sukayo kansa suna rirriqesa amma suka kasa cire hannunsa daga wuyansa, cikin b'acin ran daya sauya masa kalar idanuwansa dake fari izuwa jajaye yace.
"Kaje ka muri sauran mintotan da suka rage maka kafin jami'an tsaro su iso gareka, Ina tabbatar maka da cewa dukkaninku sai nasa ansa kunfad'i inda kuka kai yarinyar mutane, idan ba haka ba zanyanke duk wata alaqa da Kuma 'yan uwantakar dake tsakanina dakai nasa akulleku har sai natabbatar da kunfad'i inda take tukuna."
Yana gama fad'ar haka ya sakesa tare da wullasa gefe sannan yabar d'akin da asibitin gaba d'aya, baffa Usman ne ya tsaya har saida akayiwa Nuraddeen allurar bacci wanda duk abunda ke faruwa idanuwansa kad'aine arufe amma yana saurarensu.
Take bacci ya d'aukesa bayan an laqa masa gorar ruwa guda. Juyowa yayi yana kallon baffa Ali da har lokacin ke zaune qasa yana lalubar wuyansa saboda azabar zafin riqon da baffa yayi masa a kuma lokaci guda yana fidda lumfashi d'aya bayan d'aya yace.
"Ga d'anka nan ka kula dashi idan kaga dama, idan kuma baka gani ba zaka iya tafiya." Yana kaiwa nan shima yabi bayan baffa, har yakusa fita ya juyo had'e da cewa. "Yawwa Ali namanta in fad'a maka cewa zaka iya qarasa rayuwarsa idan kana buqata tunda bakwason ganinsa cikin farinciki balle raye." Sannan yawuce.
••• ••• •••
A gefen wani babban titi shed'anin da bargaji yaturo ya sace Rashida ya jefar da ita bayan yagama azabtar da ita lokacin qarfe hud'u da rabi na dare ko motsi batayi, abunda ke cikinta sai faman motsi yakeyi saboda azabar daya sha ga lumfashin uwa dake taimaka masa na neman yarabu da gangar jikinta, cikin iyawar ALLAH da nuna isarsa ga bayinsa da sukayi imani dashi kuma yake taimaka masu alokacin da suke neman taimako yasa sanyin asuba nafara sauka lumfashin Rashida ya daidaita ga gangar jikinta, wani dogon lumfashi taja had'e da qoqarin bud'e idanuwanta a hankali a hankali, ganinta agefen titi gashi duhu ya mamaye gari ko hasken mota bata gani saboda dogayen ciyawun da sukayi shamaki tsakaninta da titi balle ahangota yasa tafara qoqarin tashi, bataji wani dogon rauni ba a zahirance sai 'yar gugguljewar da ko ina ajikinta yayi da kuma azabar da takeji can cikin qashin bayanta da kuma mararta wanda in bata manta ba acikin wannan halin take kafin ta tsinci kanta acikin wannan yanayin da take kallo tamkar mafarki, jin an shureta cikin ciki ya tuna mata da d'an dake cikinta da sauri tasa hannu tana tattab'a cikin, duk inda taji alamun abunda ke ciki yayi motsi sai takai hannunta akai shi kuma sai ya janye yakoma wani gefen, haka ta dingayi tana murmushi kafin tafara qoqarin fitowa daga cikin ciyawun tana takawa da qyar saboda nauyin cikin. Hango wani haske da tayi acan tsallaken titi yasa tayi yunqurin tsallakawa don samawa kanta tsaro daga abun dakan iya cutar da ita awajen.
K'iiiiiiiii...kakeji da qarfi motar dake tafe gabanta da gudu matuqin yaja burki ganin mutum ya gitta masa, nan take tsananin tsoro daya gama zama abokin rayuwarta yasa tasaki wata irin qara tare da duqewa wajen, k'iris kad'an ya rage Mai motar yabugeta Amma ALLAH ya taimakesa kafin motar takai ga jikinta yayi nasarar tsaida ita, qara hasken fitillun motarsa yayi don gasgata idanuwansa dake gane masa mace da tsohon ciki agabansa, da sauri ya bud'e motar yafito jin wata irin qara da Rashida tayi tana fad'in,
"Wayyo ummata zan mutu." Saboda azabar naqudar da tataso mata lokaci guda,
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun., Baiwar ALLAH daga Ina? kike da asubancin nan haka?"
Kasa magana tayi sai yarfi da hannu takeyi tana cizon baki, kallo d'aya yayi mata ya fahimci haihuwace zatayi saboda ganin ruwan dake bin qafafuwanta Wanda bako shakka fawace tafashe.
Gabas da yamma, kudu da arewa yaduba Babu wani mahaluqi dake tahowa daga saman titin, shimad'in yayi sakkon fitowane saboda wani emergency operation da aka kirasa cewa zaiyi da safennan, shine dalilin fitowarsa cikin sauri zaije airport don ya hau jirgi sai gashi ya had'u da wannan tsotsayin, sake kallon Rashida yayi yaga she's too young da alama ma haihuwar farince duk rashin imaninsa bazai iya barinta awajen ba, gashi tana stage d'in da take matuqar buqatar taimako, bai tsaya saurarar zuciyarsa ba kawai ya runtse idanuwa yana karanto addu'a daga bakinsa ya tallabeta ya sakata cikin motar ya tayar ya nufi hanyar asibiti mafi kusa dasu acikin garin, kallon yanda take nishi da qarfi alamun haihuwar na kusa yakeyi had'e da qara gudun motarsa,
A wata qatotuwar asibiti yayi parking had'e da fitowa da sauri ya bud'e bayan motar ya sake d'aukota yanufi cikin asibitin da ita yana kiran "nurse, nurse.." da gudu suka fito suka karb'eta suka nufi cikin wani d'aki da ita, wata nurse ce tashiga da sauri cikin wani office tayowa dr dake on duty magana suka fito tare da ita, har zasu shiga d'akin da aka shiga da Rashida yayi saurin tsaishesu yana fad'in
"Dr. don ALLAH ka taimakawa yarinyarnan, haihuwa ce zatayi kuma inaga wannan itace tafari, ga dukkan alama yamatuqar Shan wahala don tadad'e tana labour, yanayinta ya nuna tayi riching final stage da zata iya haihuwa wato 10cm don ALLAH kayi iya qoqarinka wajen taimakonta ta haihu lafiya." Yaqare maganar yana had'a hannayensa waje d'aya, riqa hannunsa Dr yayi yana mai bashi k'warin guiwar cewa zai iya sannan ya wuce batare daya tanka ba.
Safa da marwa mutumen ya dingayi abakin d'akin yana mai addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya kafin yaciro wayarsa yakira matarsa. Bugu d'aya ta d'aga had'e da cewa.
"Swthrt har ka isa airport d'in." Cike da damuwa yace
"A'a fatima banma je wajen ba, yanzu haka Ina asibiti.." miqewa tayi daga kwancen da take ta tashi zaune had'e da cewa "swhrt lafiya kuwa? meya same kane? Dama tunda zaka tafi Saida nafad'a maka hankalina bai kwanta da tafiyarnan ba qara kabari sai safiya tawaye ido naganin ido amma ka nace kai sai alokacin zaka tafi." Taqare maganar had'e da fashewa da kuka.
"Haba Fatima meye haka kikeyi? Kinaji na ki saurareni kiji me zanfad'a, Babu abunda ya sameni kawai ansamu matsalace akan hanyata ta zuwa filin jirgin..."
Nan yaciga da yimata bayani dalla dalla sannan takwantar da hankalinta, cike da damuwa yaci gaba da cewa.
"Idan zaki iya munanan _mom maternity clinic_ kiyi sauri kizo kinji ko."
"On my way Dr. In Sha ALLAH." Tafad'a tana goge hawayenta had'e da kashe wayar.
Daidai lokacin shima yasaki wata irin ajiyar zuciya tare da runtse idanuwa saiga likitan yafito da sauri ya nufo inda yake tsaye.
"Dr. Lafiya?." Mutumen yafad'a yana kallonsa cikin tashin hankali, shiru Dr. ya d'anyi kafin ya kallesa had'e da cewa.
"Am sorry ansamu matsala. Dole zaka samana hannu anan." Yajuya wajen nurse d'in dake biye dashi ya karb'i takarda a hannunta yana miqa masa. "Zaka saka hannu saboda dole sai anyi mata tiyata bazata iya haihuwa da kanta ba."
"Kamarya Dr.? Inada tabbaci akan takai adadin yanda ake buqatar ta haihu mezaisa kace Kuma bazata iya haihuwa ba yanzu."
"Saboda yaron baizo daidai ba, ma'ana amai makon yazo takai sai yazo ta qafafuwa aturance muna Kiran irin wannan haihuwa da "breech presentation" wato haihuwar da tazo a baibai ba normal haihuwa ba." Shafa kai mutumen yayi had'e da cewa.
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun." Kafin yafiddo wasu i.d card guda uku had'e da license d'insa nazama likita a aljihunsa ya miqa masa da sauri, karb'a Dr. Yayi ya shiga dubawa, d'aya national i.d card d'insa ce, d'aya kuma i.d card d'in dake nuna yana aiki a qarqashin asibitin aminu kano ce dake garin birnin kano, d'ayar kuma shedar cewa shi qwararren likitane a fannin matsalar mata wato (gynicolgy) inda yaga an rubuta Dr. Nura ahmad. 'Dauke da lambobin dake nuna cewa shi cikakken likitane babba a fannin wato (consultant).
'Dago kai Dr yayi yana kallonsa ya jinjina masa kai alamar bashi tabbaci akan abunda yagani, cike da girmamawa Dr. Yasake bashi hannu suka gaisa saboda ganin shi babban sane.
"Don Allah Dr zan iya shiga na taimaka mata?. Nasan insha ALLAH zata iya haihuwa da kanta basai anyi mata tiyata ba." Shiru Dr yayi kafin ya bashi hanya yana nuna masa qofar shiga d'akin, da sauri ya shiga ya tarar da Rashida kwance ta matuqar jigata, nan take yasa handglove batare daya cire kayan dake jikinsa ba ya nufi inda take kwance, Saida yafara zuwa saiti fuskarta yace.
"Kiyi fad'a da kowace irin qadadara ce data fiddoki cikin dare awannan yanayin, ki qoqarta wajen ceto abunda kecikinki inada tabbaci akan komeye zai zamo sanyin idaniyarki, kada kibari qaddararki ta rinjayi nasararki wajen rasa abunda ke cikinki ta hanyar gazawarki, kiyi addu'a kuma ki jajirce kibamu had'in kai in sha ALLAH zamuyi nasarar wannan aikin da zamuyi." Binsa kawai Rashida tayi da kallo batare data iya tanka masa ba hawaye na tsiyaya tagefen idanuwanta, tabbas ba k'aramin tasiri kalamansa suka yimata ba hakan yasa taquduri bayar da rayuwarta ga abunda ke cikinta.
"To kadai gani Ali, jarabawar da ALLAH yad'oro muna kenan! Ubangiji ALLAH yabamu ikon canyeta."
"Amin Yaya, Amma to ba wannan ba yakamata yaronnan yasawa ransa salama, idan ALLAH yatsaro za'aga yarinyarnan to za'a ganta, in Kuma ALLAH be nufa ba to yayi haquri basai yaje ya illata kns ba zai samu wata matar tunda ba ita kad'aice mace ba, mata ne gasunan ko ina sai yazab'a ya darje, nan kusa ba nesa ba ga 'yar uwarsa nan muneera sai tamaye masa gurbinta ai inaga shikenan ko?"
Cike da b'acin rai baffa ya nufosa had'e da shaqe wuyansa ya had'a da jikin bango. "Aliyu dama kai bakada hankali ban sani ba? Mekake nufi da idan ba'a ganeta ba? Wlh damuwata tafi yawa akan b'atar yarinyar nan fiye da halinda Nuraddeen ke ciki domin nasan cewa ganinta ne kad'ai zai kawo masa sassaucin wannan halin da yake ciki saboda itace farincikinsa, shine kake fatar kada aganeta saboda ita d'in ba 'yarka bace?, Yaqarasa maganar cikin d'aga murya tare da qara shaqesa tayanda ko lumfashi mai kyau baya iyayi, kakarin d'aya farayi ne yasa baffa da likita sukayo kansa suna rirriqesa amma suka kasa cire hannunsa daga wuyansa, cikin b'acin ran daya sauya masa kalar idanuwansa dake fari izuwa jajaye yace.
"Kaje ka muri sauran mintotan da suka rage maka kafin jami'an tsaro su iso gareka, Ina tabbatar maka da cewa dukkaninku sai nasa ansa kunfad'i inda kuka kai yarinyar mutane, idan ba haka ba zanyanke duk wata alaqa da Kuma 'yan uwantakar dake tsakanina dakai nasa akulleku har sai natabbatar da kunfad'i inda take tukuna."
Yana gama fad'ar haka ya sakesa tare da wullasa gefe sannan yabar d'akin da asibitin gaba d'aya, baffa Usman ne ya tsaya har saida akayiwa Nuraddeen allurar bacci wanda duk abunda ke faruwa idanuwansa kad'aine arufe amma yana saurarensu.
Take bacci ya d'aukesa bayan an laqa masa gorar ruwa guda. Juyowa yayi yana kallon baffa Ali da har lokacin ke zaune qasa yana lalubar wuyansa saboda azabar zafin riqon da baffa yayi masa a kuma lokaci guda yana fidda lumfashi d'aya bayan d'aya yace.
"Ga d'anka nan ka kula dashi idan kaga dama, idan kuma baka gani ba zaka iya tafiya." Yana kaiwa nan shima yabi bayan baffa, har yakusa fita ya juyo had'e da cewa. "Yawwa Ali namanta in fad'a maka cewa zaka iya qarasa rayuwarsa idan kana buqata tunda bakwason ganinsa cikin farinciki balle raye." Sannan yawuce.
••• ••• •••
A gefen wani babban titi shed'anin da bargaji yaturo ya sace Rashida ya jefar da ita bayan yagama azabtar da ita lokacin qarfe hud'u da rabi na dare ko motsi batayi, abunda ke cikinta sai faman motsi yakeyi saboda azabar daya sha ga lumfashin uwa dake taimaka masa na neman yarabu da gangar jikinta, cikin iyawar ALLAH da nuna isarsa ga bayinsa da sukayi imani dashi kuma yake taimaka masu alokacin da suke neman taimako yasa sanyin asuba nafara sauka lumfashin Rashida ya daidaita ga gangar jikinta, wani dogon lumfashi taja had'e da qoqarin bud'e idanuwanta a hankali a hankali, ganinta agefen titi gashi duhu ya mamaye gari ko hasken mota bata gani saboda dogayen ciyawun da sukayi shamaki tsakaninta da titi balle ahangota yasa tafara qoqarin tashi, bataji wani dogon rauni ba a zahirance sai 'yar gugguljewar da ko ina ajikinta yayi da kuma azabar da takeji can cikin qashin bayanta da kuma mararta wanda in bata manta ba acikin wannan halin take kafin ta tsinci kanta acikin wannan yanayin da take kallo tamkar mafarki, jin an shureta cikin ciki ya tuna mata da d'an dake cikinta da sauri tasa hannu tana tattab'a cikin, duk inda taji alamun abunda ke ciki yayi motsi sai takai hannunta akai shi kuma sai ya janye yakoma wani gefen, haka ta dingayi tana murmushi kafin tafara qoqarin fitowa daga cikin ciyawun tana takawa da qyar saboda nauyin cikin. Hango wani haske da tayi acan tsallaken titi yasa tayi yunqurin tsallakawa don samawa kanta tsaro daga abun dakan iya cutar da ita awajen.
K'iiiiiiiii...kakeji da qarfi motar dake tafe gabanta da gudu matuqin yaja burki ganin mutum ya gitta masa, nan take tsananin tsoro daya gama zama abokin rayuwarta yasa tasaki wata irin qara tare da duqewa wajen, k'iris kad'an ya rage Mai motar yabugeta Amma ALLAH ya taimakesa kafin motar takai ga jikinta yayi nasarar tsaida ita, qara hasken fitillun motarsa yayi don gasgata idanuwansa dake gane masa mace da tsohon ciki agabansa, da sauri ya bud'e motar yafito jin wata irin qara da Rashida tayi tana fad'in,
"Wayyo ummata zan mutu." Saboda azabar naqudar da tataso mata lokaci guda,
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun., Baiwar ALLAH daga Ina? kike da asubancin nan haka?"
Kasa magana tayi sai yarfi da hannu takeyi tana cizon baki, kallo d'aya yayi mata ya fahimci haihuwace zatayi saboda ganin ruwan dake bin qafafuwanta Wanda bako shakka fawace tafashe.
Gabas da yamma, kudu da arewa yaduba Babu wani mahaluqi dake tahowa daga saman titin, shimad'in yayi sakkon fitowane saboda wani emergency operation da aka kirasa cewa zaiyi da safennan, shine dalilin fitowarsa cikin sauri zaije airport don ya hau jirgi sai gashi ya had'u da wannan tsotsayin, sake kallon Rashida yayi yaga she's too young da alama ma haihuwar farince duk rashin imaninsa bazai iya barinta awajen ba, gashi tana stage d'in da take matuqar buqatar taimako, bai tsaya saurarar zuciyarsa ba kawai ya runtse idanuwa yana karanto addu'a daga bakinsa ya tallabeta ya sakata cikin motar ya tayar ya nufi hanyar asibiti mafi kusa dasu acikin garin, kallon yanda take nishi da qarfi alamun haihuwar na kusa yakeyi had'e da qara gudun motarsa,
A wata qatotuwar asibiti yayi parking had'e da fitowa da sauri ya bud'e bayan motar ya sake d'aukota yanufi cikin asibitin da ita yana kiran "nurse, nurse.." da gudu suka fito suka karb'eta suka nufi cikin wani d'aki da ita, wata nurse ce tashiga da sauri cikin wani office tayowa dr dake on duty magana suka fito tare da ita, har zasu shiga d'akin da aka shiga da Rashida yayi saurin tsaishesu yana fad'in
"Dr. don ALLAH ka taimakawa yarinyarnan, haihuwa ce zatayi kuma inaga wannan itace tafari, ga dukkan alama yamatuqar Shan wahala don tadad'e tana labour, yanayinta ya nuna tayi riching final stage da zata iya haihuwa wato 10cm don ALLAH kayi iya qoqarinka wajen taimakonta ta haihu lafiya." Yaqare maganar yana had'a hannayensa waje d'aya, riqa hannunsa Dr yayi yana mai bashi k'warin guiwar cewa zai iya sannan ya wuce batare daya tanka ba.
Safa da marwa mutumen ya dingayi abakin d'akin yana mai addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya kafin yaciro wayarsa yakira matarsa. Bugu d'aya ta d'aga had'e da cewa.
"Swthrt har ka isa airport d'in." Cike da damuwa yace
"A'a fatima banma je wajen ba, yanzu haka Ina asibiti.." miqewa tayi daga kwancen da take ta tashi zaune had'e da cewa "swhrt lafiya kuwa? meya same kane? Dama tunda zaka tafi Saida nafad'a maka hankalina bai kwanta da tafiyarnan ba qara kabari sai safiya tawaye ido naganin ido amma ka nace kai sai alokacin zaka tafi." Taqare maganar had'e da fashewa da kuka.
"Haba Fatima meye haka kikeyi? Kinaji na ki saurareni kiji me zanfad'a, Babu abunda ya sameni kawai ansamu matsalace akan hanyata ta zuwa filin jirgin..."
Nan yaciga da yimata bayani dalla dalla sannan takwantar da hankalinta, cike da damuwa yaci gaba da cewa.
"Idan zaki iya munanan _mom maternity clinic_ kiyi sauri kizo kinji ko."
"On my way Dr. In Sha ALLAH." Tafad'a tana goge hawayenta had'e da kashe wayar.
Daidai lokacin shima yasaki wata irin ajiyar zuciya tare da runtse idanuwa saiga likitan yafito da sauri ya nufo inda yake tsaye.
"Dr. Lafiya?." Mutumen yafad'a yana kallonsa cikin tashin hankali, shiru Dr. ya d'anyi kafin ya kallesa had'e da cewa.
"Am sorry ansamu matsala. Dole zaka samana hannu anan." Yajuya wajen nurse d'in dake biye dashi ya karb'i takarda a hannunta yana miqa masa. "Zaka saka hannu saboda dole sai anyi mata tiyata bazata iya haihuwa da kanta ba."
"Kamarya Dr.? Inada tabbaci akan takai adadin yanda ake buqatar ta haihu mezaisa kace Kuma bazata iya haihuwa ba yanzu."
"Saboda yaron baizo daidai ba, ma'ana amai makon yazo takai sai yazo ta qafafuwa aturance muna Kiran irin wannan haihuwa da "breech presentation" wato haihuwar da tazo a baibai ba normal haihuwa ba." Shafa kai mutumen yayi had'e da cewa.
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun." Kafin yafiddo wasu i.d card guda uku had'e da license d'insa nazama likita a aljihunsa ya miqa masa da sauri, karb'a Dr. Yayi ya shiga dubawa, d'aya national i.d card d'insa ce, d'aya kuma i.d card d'in dake nuna yana aiki a qarqashin asibitin aminu kano ce dake garin birnin kano, d'ayar kuma shedar cewa shi qwararren likitane a fannin matsalar mata wato (gynicolgy) inda yaga an rubuta Dr. Nura ahmad. 'Dauke da lambobin dake nuna cewa shi cikakken likitane babba a fannin wato (consultant).
'Dago kai Dr yayi yana kallonsa ya jinjina masa kai alamar bashi tabbaci akan abunda yagani, cike da girmamawa Dr. Yasake bashi hannu suka gaisa saboda ganin shi babban sane.
"Don Allah Dr zan iya shiga na taimaka mata?. Nasan insha ALLAH zata iya haihuwa da kanta basai anyi mata tiyata ba." Shiru Dr yayi kafin ya bashi hanya yana nuna masa qofar shiga d'akin, da sauri ya shiga ya tarar da Rashida kwance ta matuqar jigata, nan take yasa handglove batare daya cire kayan dake jikinsa ba ya nufi inda take kwance, Saida yafara zuwa saiti fuskarta yace.
"Kiyi fad'a da kowace irin qadadara ce data fiddoki cikin dare awannan yanayin, ki qoqarta wajen ceto abunda kecikinki inada tabbaci akan komeye zai zamo sanyin idaniyarki, kada kibari qaddararki ta rinjayi nasararki wajen rasa abunda ke cikinki ta hanyar gazawarki, kiyi addu'a kuma ki jajirce kibamu had'in kai in sha ALLAH zamuyi nasarar wannan aikin da zamuyi." Binsa kawai Rashida tayi da kallo batare data iya tanka masa ba hawaye na tsiyaya tagefen idanuwanta, tabbas ba k'aramin tasiri kalamansa suka yimata ba hakan yasa taquduri bayar da rayuwarta ga abunda ke cikinta.