Sashe 41
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Satinta d'aya cikin d'aki tunda aka salla mota bata fitowa ko bakin qofa tana jinyar jikinta don har yanzu bai koma daidai ba bata son cin komai sai fura da kwad'on zogale hakan yasa tadena girki don ko qamshinsa bata so, Inna Bilkisu kullum cikin sayen ganyen zogale take a b'oye tana aika mata dashi haka baffa duk yafita sai ya sawo mata damammiyar fura tasha nono, abunka da qaramar yarinyar dake taka matakin farko na cikar girmanta mace nan take suka karb'i jikinta ta murmuje tayi haske abunta, bata aikin komai saboda fadeela da aysha keyi mata share share da wanke wanke, shi Kuma Nuraddeen shike kula da gyara mata d'akinta da wankanta, sosai yake bata kulawar da baya barin kowa shigowa sai idan aikowa akayi ko kuma cikin matan gidanne sukazo dubata da jiki shima d'in sai ya tabbatar ya saka mata hijabi tukuna yake cewa su shigo.
Yaya hawwa kam ranar tunda safe ta shiga sashen daga tsakar gida tana qwalla masa kira da sauri yafito had'e da duqawa yana gaisheta, kallonsa tayi tun daga sama har qasa ta mere baki had'e da cewa.
"Sannu bawan mata, wai ita har yanzu bata warke bane?"
"A'a innar mu da sauqi dai."
"Mtssa to ni nagaji da d'ora sanwar nan Ina jiran aminci don yau zanyi baqi, sai ka sanar da ita don kada ab'ata mani lokaci."
"To innar mu."
Yafad'a jiki a sanyaye yana mamakin wannan hali na mahaifiyarsa, tun ranar da abunnan yafaru tsakaninsa da muneera har zuwa ciwon Rashida bataxo sashen ba balle tazo ta dubata, amma yanzu rashin kai mata abinci na sati d'aya yajawo tazo tana qorafi akai, muryarta ya tsinkayo daga tunanin daya tafi tana fad'in. "Kaji ko."
"E.eh innar mu."
Nuraddeen yabata amsa da sauri cikin i'ina, Jan tsaki tayi tare da kallon qofar d'akin Rashida ta cije baki had'e da girgiza kai sannan tabar wajen, jiki sanyaye yabar wajen shima yakoma cikin d'aki yana kallon Rashida dake baccinta hankali kwance batare da tasan ma wainar da ake toyawa ba,
K'arar wayarta dake ruri yasa ta motsawa had'e da bud'e idanuwanta suka sauka akan fuskarsa, murmushi yayi tare da mik'a mata hannu yariqota ta tashi zaune sannan ya d'auko wayar dake sake ruri akaro na biyu ya miqa mata, murmushi ne ya bayyana a fuskarta lokacin da idanuwanta suka sauka saman screen d'in wayar ta kalli Nuraddeen tace.
"Laaaa..Habibi baba ne."
"To kid'auka mana kada ta tsinke." yafad'a tare da miqewa yabar d'akin yana tunanin abunda yakamata ya dafawa Yaya hawwa tunda ko kad'an Rashida bata son qamshin girki shiyasa ta denayi, shi kansa saidai yanemi ruwan tea yasha ko kuma yaci abincin da Inna Bilkisu ke aiko mata dashi.
Cikin jin dad'i Rashida ta d'aga had'e da gaisheda mahaifin nata da tuni labarin tana da ciki ya isa kunnensu...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
_Hi fan's am so sorry akan yanda kuka matsu mukoma asalin labari, Karku manta ita SANNU SANNU bata hana zuwa..no matter how matuqar ALLAH yabani aron lumfashi da kuma rayuwa zan sadaku da farkon labarin da muka faro, karku manta *baku san ko waye Abu sumayya ba?, bakusan asalinsa ba? taya ya had'u da matarsa batool shima baku sani ba? meya jawo batooul tabar iyayenta har na tsawon shekaru bakwai? Shin Abu sumayya ya cancanci mutuwa adaidai lokacin da yakamata yasan ko waye mahaifinsa?, meyasa mahaifin batoul ya sheganta shi, Shin batool itama ta cancanci ta fuskanci jarabawar da take ciki adaidai lokacin da take d'okin sake had'uwa da iyayenta?* 😅Inada yaqini akan shima baku sani ba kuma bakuda duka amsoshin wud'annan tambayoyin, wannan waiwayen tushen labari da mukayi shi kad'ai zai amsa maku duka wud'annan tambayoyi kuma da sannu ya sadaku da farkon labarinku, saboda haka kujuri zuwa rafi na tabbatar ranar da tulun zai fashe na nan zuwa🤣Ina matuqar godiya bisa yanda kuke qaramun k'warin guiwa ta hanyar comment d'inku, nakanyi farinciki kuma na nishad'antu da hakan akoda yaushe, FILLAH INA SONKU OVER💋😍_
Page___31💎
Har Nuraddeen zai wuce yadawo yayi tsaye yana jin maganganun dake fitowa daga bakin muneera, tun daga farko har qarshe babu abunda baiji ba yafito ransa a'bace yana watsawa Inna ruqayya da tayi tsuru tsuru da idanuwa tana 'yan kame kame wani irin mugun kallo da yasa cikinta murd'awa, nunata da yatsa yayi yace.
"Wai ni za'a kai wajen wani malami ko boka don in so wannan abar?" Yaqare maganar yana nuna muneera sama da qasa da hannu, murmushin gefen baki ya saki cike da takaici kafin yaci gaba da cewa. "To wallahi Inna ruqayya koda matan duk duniya zasu qare bazan tab'a auren muneera ba Kuma badon bana sonta ba sai don kawai kinzamo mahaifiyarta, duk da 'yar uwata ce ita bazan iya aurenta ba har duniya ta nad'e don haka idanma mafarki kukeyi to wlh kufarka kunema mata mijin daya dace da ita, wannan Nuraddeen da kike gani in sha ALLAH mallakin Rashida ne ita kad'ai, zuciya da kuma ruhi gaba d'aya natane bana tunani ko a mafarki kwakwalwata zata aminta da shigowar wata azuciyata ko wacece ita ciki kuwa har da muneera d'in da kuke qaqabar 'yar uwata ce domin bare tagama mani komai aduniya.." wata irin qara muneera tayi had'e da ciyo kwalarsa tana kuka, "wallahi ya nura baka isa ba, don ka kawai aka halitto ni bazai yuyu na auri wani inba kaiba.." Bata qarasa maganar sanadiyar wani zazzafan mari daya d'auketa yana kallon wuyar rigarsa data riqo, qafa yakai zai hankad'ata tayi saurin duqewa wajen tare da riqe masa qafafuwa tana kuka, "don ALLAH ya nura karka damu da inna, kafita batunta da halayenta ni kai nake so, zan zauna da kai ko mata nawa zaka aura amma karka yimani hukunci akan halin Inna ita da baffa sune basa son matarka haka ranar naji suna fad'a wai Inna hawwa takaita wajen malan bakada imani za'a dinga turo mata aljanu suna tsoratata, yanzu haka ciwon da takeyi sune sukasa yaturo mata shi.." baya baya Nuraddeen yayi kamar zai fad'i saboda tsorata da kalaman dake fitowa daga bakin muneera, duk da dai ciwon da Rashidarsa keyi ba irin wanda take nufi bane amma maganarta akwai qamshin gaskiya aciki idan yayi la'akari da tsoron da Rashida kecewa ana bata da Kuma yawan firgitarta acikin barci, kasa cewa uffan yayi har saida Inna Bilkisu dake tsaye cikin rumfarta tana sauraronsu ta matso wajen ganin yanayin daya shiga ta dafashi tana fad'in. "Karka kuskura ka amince da wannan soki burutsun na muneera kasan halinta da shirme, idan kuma har gaskiya take fad'a to kada ka tsorata domin da wannan tsoron naka za'ayi amfani wajen cutar da kai da kuma matarka kayarda ba mai yimaka sai ALLAH kuma Babu wanda ya isa ya cutar da kai sai abunda alqalamin qaddara ya rubuto akanka, maza kawuce kaje wajen iyalinka ba abunda zai sameku in sha ALLAH tunda kun riqe ALLAH, sharri shi Kuma d'an aikene duk inda kaje zai dawo ya sanar maka."
Taqare maganar tana kallon Inna ruqayya da tsabar kunya tasa tayi wuri wuri da idanuwa tana faman susar wuyanta.
Wasu zafafan hawaye yaji son zubo masa wai ace qiyayyar da mahaifiyarsa keyima matarsa har takai ga za'a iya had'a baki da ita acutar mashi da ita don d'ai cikar burin wasu, cikin zafin rai ya dubi Inna Bilkisu yace. "Inna Bilkisu me yarinyar nan tayi masu da suke nema su cutar da ita, nine fa d'ansu duk wani abu na mataki daya kamata su d'auka akaina ya dace ba itaba." Girgiza kai Inna Bilkisu tayi had'e da cewa.
"ALLAH dai ya kyauta, kawai kashiga ciki in sha ALLAH babu abunda zai sameta."
"Munafuka! aikin kenan ko yaushe sa ido, to Ina ruwanki tunda duk abunda akayi d'in da sanin mahaifiyarsa ita data haifesa, meye naki nasa baki, ke kuma shegiya mai baqin baki kamar aku da yaushe akayi haka? wato ke uwar soyayya zaki qaqaba mana sharri tsakar rana, tashi muje yau sai kin gane kurenki" irin borin kunyar nan Inna ruqayya tafara wud'annan suruttan had'e da rufe muneera da duka tana janta,
"Dakata Inna ruqayya! ku gaggauta zuwa kusa a kwance qullin da akayi maku akan matata idan ba haka ba duk abunda yafaru da ita to sai nayi shari'a daku.." kafin yarufe baki yaji saukar wasu zafafan marora har biyu a fuskarsa, Yaya hawwa ce da tun d'azu da taji muneera ta sako baki tana zuba tafito tayi tsaye tana qare masu kallo ta sakar masa wud'annan marora bazato ba tsammani, cikin d'aure fuska da rashin tsoron duk abunda zaije yadawo tace
"Don buhun ubanka dake kwance anyi qullin kuma baza'a kwance ba kayi duk abunda ka iya, inkaga dama kaje koton duniya ni hawwa bana tsoron uban kowa akan wannan tsigalalliyar yarinya bare daka auro mani, Kai nifa nagaya maka natsani matarnan tun wuri ka rabu da ita ko agaban idanuwanka insa ta walaqanta, shashashan banza da wofi har kace zakayi shari'a damu akan bare." tunda Nuraddeen ya soke kai qasa bai d'ago ba sai hawaye dake faman kwarara daga idanuwansa, yarasa wannan wace irin qiyayya ce mahaifiyarsa keyi ma Rashida da har Bata shakkun kowa akan zata iya illatata.
'Dago kansa yayi yana kallon Yaya hawwa yace. "Innar mu kiyi hak'uri, aurena da Rashida muqaddirine daga ALLAH, Ina sonta sosai shiyasa nakasa haqura da ita tun farko, don ALLAH ko donni ki daure kisawa zuciyarki soyayyarta, inada yaqini akan zakiyi alfaharin samunta a matsayin suruka, kigujewa wannan mummunar al'adar da kike tunanin daidace kada ta jefaki cikin fushin ALLAH."
"To saketa idan kana so kada nashiga cikin fushin ALLAH, idan bahaka ba nayi maka baki ka lalace." Taqarasa maganar tana gyara tsayuwarta da d'aurin zanenta,
Yaya hawwa kam ranar tunda safe ta shiga sashen daga tsakar gida tana qwalla masa kira da sauri yafito had'e da duqawa yana gaisheta, kallonsa tayi tun daga sama har qasa ta mere baki had'e da cewa.
"Sannu bawan mata, wai ita har yanzu bata warke bane?"
"A'a innar mu da sauqi dai."
"Mtssa to ni nagaji da d'ora sanwar nan Ina jiran aminci don yau zanyi baqi, sai ka sanar da ita don kada ab'ata mani lokaci."
"To innar mu."
Yafad'a jiki a sanyaye yana mamakin wannan hali na mahaifiyarsa, tun ranar da abunnan yafaru tsakaninsa da muneera har zuwa ciwon Rashida bataxo sashen ba balle tazo ta dubata, amma yanzu rashin kai mata abinci na sati d'aya yajawo tazo tana qorafi akai, muryarta ya tsinkayo daga tunanin daya tafi tana fad'in. "Kaji ko."
"E.eh innar mu."
Nuraddeen yabata amsa da sauri cikin i'ina, Jan tsaki tayi tare da kallon qofar d'akin Rashida ta cije baki had'e da girgiza kai sannan tabar wajen, jiki sanyaye yabar wajen shima yakoma cikin d'aki yana kallon Rashida dake baccinta hankali kwance batare da tasan ma wainar da ake toyawa ba,
K'arar wayarta dake ruri yasa ta motsawa had'e da bud'e idanuwanta suka sauka akan fuskarsa, murmushi yayi tare da mik'a mata hannu yariqota ta tashi zaune sannan ya d'auko wayar dake sake ruri akaro na biyu ya miqa mata, murmushi ne ya bayyana a fuskarta lokacin da idanuwanta suka sauka saman screen d'in wayar ta kalli Nuraddeen tace.
"Laaaa..Habibi baba ne."
"To kid'auka mana kada ta tsinke." yafad'a tare da miqewa yabar d'akin yana tunanin abunda yakamata ya dafawa Yaya hawwa tunda ko kad'an Rashida bata son qamshin girki shiyasa ta denayi, shi kansa saidai yanemi ruwan tea yasha ko kuma yaci abincin da Inna Bilkisu ke aiko mata dashi.
Cikin jin dad'i Rashida ta d'aga had'e da gaisheda mahaifin nata da tuni labarin tana da ciki ya isa kunnensu...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
_Hi fan's am so sorry akan yanda kuka matsu mukoma asalin labari, Karku manta ita SANNU SANNU bata hana zuwa..no matter how matuqar ALLAH yabani aron lumfashi da kuma rayuwa zan sadaku da farkon labarin da muka faro, karku manta *baku san ko waye Abu sumayya ba?, bakusan asalinsa ba? taya ya had'u da matarsa batool shima baku sani ba? meya jawo batooul tabar iyayenta har na tsawon shekaru bakwai? Shin Abu sumayya ya cancanci mutuwa adaidai lokacin da yakamata yasan ko waye mahaifinsa?, meyasa mahaifin batoul ya sheganta shi, Shin batool itama ta cancanci ta fuskanci jarabawar da take ciki adaidai lokacin da take d'okin sake had'uwa da iyayenta?* 😅Inada yaqini akan shima baku sani ba kuma bakuda duka amsoshin wud'annan tambayoyin, wannan waiwayen tushen labari da mukayi shi kad'ai zai amsa maku duka wud'annan tambayoyi kuma da sannu ya sadaku da farkon labarinku, saboda haka kujuri zuwa rafi na tabbatar ranar da tulun zai fashe na nan zuwa🤣Ina matuqar godiya bisa yanda kuke qaramun k'warin guiwa ta hanyar comment d'inku, nakanyi farinciki kuma na nishad'antu da hakan akoda yaushe, FILLAH INA SONKU OVER💋😍_
Page___31💎
Har Nuraddeen zai wuce yadawo yayi tsaye yana jin maganganun dake fitowa daga bakin muneera, tun daga farko har qarshe babu abunda baiji ba yafito ransa a'bace yana watsawa Inna ruqayya da tayi tsuru tsuru da idanuwa tana 'yan kame kame wani irin mugun kallo da yasa cikinta murd'awa, nunata da yatsa yayi yace.
"Wai ni za'a kai wajen wani malami ko boka don in so wannan abar?" Yaqare maganar yana nuna muneera sama da qasa da hannu, murmushin gefen baki ya saki cike da takaici kafin yaci gaba da cewa. "To wallahi Inna ruqayya koda matan duk duniya zasu qare bazan tab'a auren muneera ba Kuma badon bana sonta ba sai don kawai kinzamo mahaifiyarta, duk da 'yar uwata ce ita bazan iya aurenta ba har duniya ta nad'e don haka idanma mafarki kukeyi to wlh kufarka kunema mata mijin daya dace da ita, wannan Nuraddeen da kike gani in sha ALLAH mallakin Rashida ne ita kad'ai, zuciya da kuma ruhi gaba d'aya natane bana tunani ko a mafarki kwakwalwata zata aminta da shigowar wata azuciyata ko wacece ita ciki kuwa har da muneera d'in da kuke qaqabar 'yar uwata ce domin bare tagama mani komai aduniya.." wata irin qara muneera tayi had'e da ciyo kwalarsa tana kuka, "wallahi ya nura baka isa ba, don ka kawai aka halitto ni bazai yuyu na auri wani inba kaiba.." Bata qarasa maganar sanadiyar wani zazzafan mari daya d'auketa yana kallon wuyar rigarsa data riqo, qafa yakai zai hankad'ata tayi saurin duqewa wajen tare da riqe masa qafafuwa tana kuka, "don ALLAH ya nura karka damu da inna, kafita batunta da halayenta ni kai nake so, zan zauna da kai ko mata nawa zaka aura amma karka yimani hukunci akan halin Inna ita da baffa sune basa son matarka haka ranar naji suna fad'a wai Inna hawwa takaita wajen malan bakada imani za'a dinga turo mata aljanu suna tsoratata, yanzu haka ciwon da takeyi sune sukasa yaturo mata shi.." baya baya Nuraddeen yayi kamar zai fad'i saboda tsorata da kalaman dake fitowa daga bakin muneera, duk da dai ciwon da Rashidarsa keyi ba irin wanda take nufi bane amma maganarta akwai qamshin gaskiya aciki idan yayi la'akari da tsoron da Rashida kecewa ana bata da Kuma yawan firgitarta acikin barci, kasa cewa uffan yayi har saida Inna Bilkisu dake tsaye cikin rumfarta tana sauraronsu ta matso wajen ganin yanayin daya shiga ta dafashi tana fad'in. "Karka kuskura ka amince da wannan soki burutsun na muneera kasan halinta da shirme, idan kuma har gaskiya take fad'a to kada ka tsorata domin da wannan tsoron naka za'ayi amfani wajen cutar da kai da kuma matarka kayarda ba mai yimaka sai ALLAH kuma Babu wanda ya isa ya cutar da kai sai abunda alqalamin qaddara ya rubuto akanka, maza kawuce kaje wajen iyalinka ba abunda zai sameku in sha ALLAH tunda kun riqe ALLAH, sharri shi Kuma d'an aikene duk inda kaje zai dawo ya sanar maka."
Taqare maganar tana kallon Inna ruqayya da tsabar kunya tasa tayi wuri wuri da idanuwa tana faman susar wuyanta.
Wasu zafafan hawaye yaji son zubo masa wai ace qiyayyar da mahaifiyarsa keyima matarsa har takai ga za'a iya had'a baki da ita acutar mashi da ita don d'ai cikar burin wasu, cikin zafin rai ya dubi Inna Bilkisu yace. "Inna Bilkisu me yarinyar nan tayi masu da suke nema su cutar da ita, nine fa d'ansu duk wani abu na mataki daya kamata su d'auka akaina ya dace ba itaba." Girgiza kai Inna Bilkisu tayi had'e da cewa.
"ALLAH dai ya kyauta, kawai kashiga ciki in sha ALLAH babu abunda zai sameta."
"Munafuka! aikin kenan ko yaushe sa ido, to Ina ruwanki tunda duk abunda akayi d'in da sanin mahaifiyarsa ita data haifesa, meye naki nasa baki, ke kuma shegiya mai baqin baki kamar aku da yaushe akayi haka? wato ke uwar soyayya zaki qaqaba mana sharri tsakar rana, tashi muje yau sai kin gane kurenki" irin borin kunyar nan Inna ruqayya tafara wud'annan suruttan had'e da rufe muneera da duka tana janta,
"Dakata Inna ruqayya! ku gaggauta zuwa kusa a kwance qullin da akayi maku akan matata idan ba haka ba duk abunda yafaru da ita to sai nayi shari'a daku.." kafin yarufe baki yaji saukar wasu zafafan marora har biyu a fuskarsa, Yaya hawwa ce da tun d'azu da taji muneera ta sako baki tana zuba tafito tayi tsaye tana qare masu kallo ta sakar masa wud'annan marora bazato ba tsammani, cikin d'aure fuska da rashin tsoron duk abunda zaije yadawo tace
"Don buhun ubanka dake kwance anyi qullin kuma baza'a kwance ba kayi duk abunda ka iya, inkaga dama kaje koton duniya ni hawwa bana tsoron uban kowa akan wannan tsigalalliyar yarinya bare daka auro mani, Kai nifa nagaya maka natsani matarnan tun wuri ka rabu da ita ko agaban idanuwanka insa ta walaqanta, shashashan banza da wofi har kace zakayi shari'a damu akan bare." tunda Nuraddeen ya soke kai qasa bai d'ago ba sai hawaye dake faman kwarara daga idanuwansa, yarasa wannan wace irin qiyayya ce mahaifiyarsa keyi ma Rashida da har Bata shakkun kowa akan zata iya illatata.
'Dago kansa yayi yana kallon Yaya hawwa yace. "Innar mu kiyi hak'uri, aurena da Rashida muqaddirine daga ALLAH, Ina sonta sosai shiyasa nakasa haqura da ita tun farko, don ALLAH ko donni ki daure kisawa zuciyarki soyayyarta, inada yaqini akan zakiyi alfaharin samunta a matsayin suruka, kigujewa wannan mummunar al'adar da kike tunanin daidace kada ta jefaki cikin fushin ALLAH."
"To saketa idan kana so kada nashiga cikin fushin ALLAH, idan bahaka ba nayi maka baki ka lalace." Taqarasa maganar tana gyara tsayuwarta da d'aurin zanenta,