Sashe 14
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan yafita baffa ya kalli 'yan uwansa yace, "usman, Aliyu Ina son kunemawa d'anku Nuraddeen izinin neman auren Rashida 'yar gidan malan bashar a hannun iyayenta dake zaune agabanku idan har ba'a tsayar mata da miji ba kamar yanda d'annaku yabuqata cewa yana sonta"
Wani irin annurine da farinciki ya bayyana a fuskokinsu gaba d'aya jin kalaman dake fito daga bakin aminin nasu in banda baba da kuma aliyu qanen baffa, shidai baba tsantsar farincikine da kuma mamakin jin cewa wai malan idris nason 'yarsa Rashida, shikuma Aliyu tsananin bak'inciki da takaicin hakanne da yaji yasa yakasa b'oyewa saboda 'yarsa muneera yaso ya had'a aurensu da shi saboda yanda take tsananin sonshi. Sosai baffa yalura da sauyawar fuskar da d'an uwansa tayi Amma sai ya basar saboda jin Usman na fad'in "Masha Allah, alhamdulillah, agaskiya haka yayi kyau kuma shizai k'ara dank'on zumunci a tsakaninmu, don baka iyayen rashida kunji buqatar d'anku idan har yarinyar nan ba'a tsaida mata da miji ba, to muna nema masa izinin yafara zuwa wajenta donsu daidaita"
Gaba d'ayansu suka had'a baki wajen cewa, "to aimu da Nuraddeen da Kuma Rashida duk 'ya'yanmune, saboda haka indon ta tamu bamuqi jinin yau a d'aura masu aure ba, don haka mu tabakin malan bashar muke jira sai muyanke hukunci"
Murmushi baba yayi sannan yace "hak'ik'a nayi farinciki, farinciki kuma marar misaltuwa akan wannan al-amarin, narigaku azuciya ne sai kuma ALLAH yasa yaron ya rigani abaki, Amma ALLAH shine shedar azuciyata nayi niyar bawa Nuraddeen auren Rashida saboda yanda nayaba da halinsa da kuma nagartarsa, dad'in fad'awa da naji cewa shi d'an amininane kuma d'an wannan ahali masu d'inbin karamci da kyautatawa, saboda haka kamar yanda kukace ku iyayen duka biyunne to nima haka, gaba d'ayansu 'ya'yana ne don haka ga mahaifinta nan malan balarabe sai muji tabakinsa." Yaqarasa maganar yana nuna inda qanen nasa kezaune, murmushi malan balarabe yayi had'e da cewa, "to madallah tunda duk kunbar mani 'yar tawa nagode kuma ni balarabe Ina so ku sheda cewa ba izini kad'ai ba hatta auren 'yata Rashida nabawa d'ana Nuraddeen duniya da lahira, don haka duk sadda kuka so asa rana da kuma yanka maku sadaki sai ku nememu in sha ALLAH ko yaushene mu a shirye muke"
"Alhamdulillah" kowa yafad'a, baffa yace "Tunda hakane mezai hana ayanka sadakin kuma asa ranar yanzu sai ahuta ko me kukace?"
Cikin rawar murya anensa Aliyu yace, "A'a yaya abari har sai sunje sun tambayi yarinyar idan ta amince ina ga hakan zaifi."
"Indai ta b'angaren yarinyar mune babu wata matsala koda had'asu mukayi munyarda da tarbiyarta zata amince ballema shi yaron yaganta yace yana so, don haka ayi abunda yakamata babu damuwa in Sha ALLAH" malan balarabe yafad'a cike da nuna yarda akan 'yar tasu,ko kad'an ran Aliyu bi yimasa dad'i ba Amma babu yanda zaiyi dole ya haqura tunda duk 'yan uwan nasa sun nuna amincewarsu, kafin kace me aka yanka sadaki dubu hamsin , nan take abokanan iyayen nasu su hud'u suka had'a kud'in suka ba qannen mahaifin Nuraddeen a matsayin tasu gudun mawar ga d'an nasu,
Hakan ba k'aramin sake farantawa baffa zuciya yayi ba tare da yiwa ALLAH godiya daya basa nagartaccin abokanai irinsu,
Abunda ALLAH yaso kuma yariga ya had'a ko ana so ko ba'a so to sai ya tabbata, a ranar su baba basu baro garinba har saida aka dindince ranar d'aurin auren nan da sati biyu masu zuwa tare da sadakin Rashida a hannunsu zuciyoyinsu cike da farinciki, nisawa mahaifin Rashida yayi yace "ALLAH mai iko kuma mai yin yanda yaso, mu da mukaje gano marar lafiya sai gashi mun dawo da sadakin 'yarmu a hannu, tabbas komai nada sanadi arayuwa, ubangiji ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi kuma ya had'e hankulansu waje d'aya" kowanensu ya amsa da "Amin" suna masu jinjina al-amarin ubangiji.
Aliyu kuwa suna tafiy bai zame ko Ina ba sai d'akin mahaifiyar Nuraddeen wato matar yayan nasa yay hawwa kmar yanda suke kiranta yana cika yana batsewa, nan ta taso tana tambayarsa ko lafiya ai kamar jira yakeyi ya zayyane mata qarya da gaskiya, ashar ta lailayo ta dire tna fad'in "ai wlh ba'a isa ba, yaushe har shi nuran yayi girman da ya isa yace ga wadda yake so da har za'aje ayo masa qulle qulle a aura masa wata can bare, to wlh bazan tab'a lamuntar wannan abun gori acikin dangi ba, haka kurum ajawo mani abun kunya da fad'a acikin gari, kowa yasan awannan garin namu auren zumunci akeyi, bamuda bare kuma ba'a tab'a kawo mana ita acikin gida ba, shikenan sai yanzu ace akan d'ana za'a fara?to wlh haka bazata sab'uba wai bindiga aruwa" wani farincikine ya rufe Aliyu yaci gaba da ingizata yana zugata haddasu cewa "Nima haka nagani yaya hawwa, Ina laifin ace ko muneera ce an had'asa da ita tunda tana sonsa amma wai antashi an had'asa da wacce batasan kimarmu da darajarmu ba, ga yaran cikin garin basuda mutunci da girmama na gabansu"
"Kai rufamun baki, muneera ko shashasha, tun yaushe nake cemata tadinga oqarin jawo hankalinsa amma takasa, shegiya mai gwalmad'ad'd'in qafafuwa ai koma meye laifin tane"
"Amma yaya hawwa kemafa kinsan yaronnan da baqin rai yake, har yaushe tag fuska balle taje tayi masa karairayar da zata jawo hankalinsa, yanzu dai ya kamata kisan abunyi kafin yarinyar nan tazo tarabamu da d'anmu ta tsigemu gaba d'aya"
"Kai Aliyu tofar da mugun yawun bakinan naka, wannan baqar fata har Ina, Bari naje wajen malan dole a ajiye wannan maganar" fiiiii...tanufi shigifar da baffa ke kwance ta iskosa yana jan carbi, masifa tafara zuba masa yana kallonta har ta gama sannan ya ajiye carbin agefe yace "yanzu ke hawwa awannan yanayin da nake ciki har kinada k'warin guiwar zuwa kiyi tsaye agabana kina wud'annan maganganun, to bari infad'a maki ko kina so ko bakya so sai anyi wannan auren tunda yana son yarinyar"
"Ni kuma bana son yarinyar, don haka bazai aureta ba"
"Saboda meye?"
"Saboda ita d'in barece"
"A'ina aka fad'i hakan, qur'ani yafad'a ne ko a'a?"
"A al'adar garinmu dai ce ba'a tab'a yin hakan ba kuma baza'a fara akan d'ana ba"
"Kaji shirmen banza, al'adar tafi alqur'anin ne? To Bari kiji wannan aure kamar anyi angama ne da yardar ALLAH"
"Amma malan inkayi mani haka bakayi mani adalci ba sabo..." Bata qarasa rufe baki ba yace
"Eh jeki naji d'in ni yanzu barci nakeji bana son wannan hayaniyar!"
Duk inda ran hawwa yake inyayi dubu yab'aci, tafice buuuu.kamar zata tashi sama tana maseefa, karo tayi da Usman akan hanyar tsakar gidan da yake family ne duk anan suke zune tafara yimasa qorafi, murmushi yayi sannan yace, "ikon ALLAH, to aike yaya hawwa banda addu'a babu abunda yakamata kiyi tunda shi yaganta kuma yace yana sonta, don ALLAH don annabi ki kwantar da hankalinki, mai k'aya ya daure kuma sai ace mai cira na kuka!?"
Aifa nan shima tayi masa tatas har tana k'arawa da cewa ai duk munafuccin da akayi dashi akayisa, shidai murmushi kawai yayi yawuce abunsa batare daya sake tankata ba, Aliyu ne ya iso wajen yana kallon irin hararar data raka d'an uwansa da ita yace,
"Ahaf! Ai infad'a maki yaya hawwa duk munafuccin agindinsa yake, shine nan ya qulla komai." Tsaki taja had'e da barin wajen tana fad'in, "sakarci, to kai meya hanaka kwancewa daya qulla, ai wlh duk sai nayi maganinku ga baki d'aya."
😨 _TIRQASHI! RASHIDA KINA CIKIN MATSALA, GASHI KEBA ILIMIN ZAMANI BALLE KI KWACI KANKI🤔🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️_
*_ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU👏😭_*
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___12💎
Kallo Aliyu yabi yaya hawwa dashi kafin yace "Kai wannan mata anyi fitinanniyar halitta anan, duk girmanka baza katab'a gwaninta awajenta ba, jarababbiya da ganinta kasan ba qaramin haquri yaya keyi da ita ba."
Kasa zaune da tsaye yaya hawwa tayi saboda tunanin hanyar da zatabi ta hana auren, in tayi nan tayi can kamar mai jiran sauraren wani sak'on, cije baki tayi aranta tana mai ayyana kalar uqubobin data tanadawa yarinyar matuqar bata samu nasarar ruguje auren ba,
Baba kuwa yana isa gida bakinsa ko rufuwa bayayi saboda tsananin farinciki yafara k'walawa Rashida kira alokacin ita kuma tana bayi tana wanka,
"A'a sannu da zuwa malan,lafiya naji kana k'wallawa 'yar taka kira tundaga zaure" tak'are zancen had'e da jawo tabarmar dake gefen d'aki ta shimfid'a masa sannan takoma d'aki ta d'auko ruwa masu sanyi takawo masa, fuskarsa cike da annuri ya nemi waje ya zauna sannan yace,
"Yawwa maman Rashida lafiya klw muka dawo, Ina ita Rashidar take, ko tayi islamiya ne?"
"A'a yanzunnan tashiga wanka, inaji yauma tayi latti ALLAH yakareta daga dukan malamai."
"Amin ya ALLAH" Yafad'a had'e da d'aukar ruwan data ajiye masa agabansa yasha,
"Malan shin ko abun sirrine tsakanin uba da 'yarsa naji kayi shiru, kai da naga kashigo da azamarka kamar Wanda akaba saqo yakawo mani." Murmushi yayi mata sannan yace
"To kusan dai kamar hakanne amma sak'on Kuma bake aka bawa ba 'yarmu aka ba."
"Tooo...! Kace dai harkar tason kaice, to bari nakama bakina, inbar uba da 'yarsa susha sha'aninsu"
"A'a ranki shidad'e ai abun bai kai can ba, ungo wannan riqe inyi maki bayani" ya ciro kud'i a aljihunsa ya mik'a mata, ansa tayi tana bin kud'in cike da mamaki kafin tace, "malan a ina kasamo wud'annan? Ina wajen ganin marar lafiya kuka tafi ko?"
"Eh a can mukaje?"
"To wud'annan kud'infa a ina aka samosu?"
"Kai maman Rashida wud'annan tambayoyin sunyi yawa, sai kace wanda yasato"
"To ai dole na tambaya saboda abun da mamaki!."
"kwantar da hankalinki to wannan sadakin Rashida ne kuma nan da sati biyu za'a d'aura auren in sha ALLAH..." bai qarasa zancen ba sukaji qarar fad'uwar bokiti daga toilet Rashida ta saki jin abunda kefitowa daga bakin mahaifin nata, atare umma da baba sukace,
"Ke lafiya?"
Wani irin annurine da farinciki ya bayyana a fuskokinsu gaba d'aya jin kalaman dake fito daga bakin aminin nasu in banda baba da kuma aliyu qanen baffa, shidai baba tsantsar farincikine da kuma mamakin jin cewa wai malan idris nason 'yarsa Rashida, shikuma Aliyu tsananin bak'inciki da takaicin hakanne da yaji yasa yakasa b'oyewa saboda 'yarsa muneera yaso ya had'a aurensu da shi saboda yanda take tsananin sonshi. Sosai baffa yalura da sauyawar fuskar da d'an uwansa tayi Amma sai ya basar saboda jin Usman na fad'in "Masha Allah, alhamdulillah, agaskiya haka yayi kyau kuma shizai k'ara dank'on zumunci a tsakaninmu, don baka iyayen rashida kunji buqatar d'anku idan har yarinyar nan ba'a tsaida mata da miji ba, to muna nema masa izinin yafara zuwa wajenta donsu daidaita"
Gaba d'ayansu suka had'a baki wajen cewa, "to aimu da Nuraddeen da Kuma Rashida duk 'ya'yanmune, saboda haka indon ta tamu bamuqi jinin yau a d'aura masu aure ba, don haka mu tabakin malan bashar muke jira sai muyanke hukunci"
Murmushi baba yayi sannan yace "hak'ik'a nayi farinciki, farinciki kuma marar misaltuwa akan wannan al-amarin, narigaku azuciya ne sai kuma ALLAH yasa yaron ya rigani abaki, Amma ALLAH shine shedar azuciyata nayi niyar bawa Nuraddeen auren Rashida saboda yanda nayaba da halinsa da kuma nagartarsa, dad'in fad'awa da naji cewa shi d'an amininane kuma d'an wannan ahali masu d'inbin karamci da kyautatawa, saboda haka kamar yanda kukace ku iyayen duka biyunne to nima haka, gaba d'ayansu 'ya'yana ne don haka ga mahaifinta nan malan balarabe sai muji tabakinsa." Yaqarasa maganar yana nuna inda qanen nasa kezaune, murmushi malan balarabe yayi had'e da cewa, "to madallah tunda duk kunbar mani 'yar tawa nagode kuma ni balarabe Ina so ku sheda cewa ba izini kad'ai ba hatta auren 'yata Rashida nabawa d'ana Nuraddeen duniya da lahira, don haka duk sadda kuka so asa rana da kuma yanka maku sadaki sai ku nememu in sha ALLAH ko yaushene mu a shirye muke"
"Alhamdulillah" kowa yafad'a, baffa yace "Tunda hakane mezai hana ayanka sadakin kuma asa ranar yanzu sai ahuta ko me kukace?"
Cikin rawar murya anensa Aliyu yace, "A'a yaya abari har sai sunje sun tambayi yarinyar idan ta amince ina ga hakan zaifi."
"Indai ta b'angaren yarinyar mune babu wata matsala koda had'asu mukayi munyarda da tarbiyarta zata amince ballema shi yaron yaganta yace yana so, don haka ayi abunda yakamata babu damuwa in Sha ALLAH" malan balarabe yafad'a cike da nuna yarda akan 'yar tasu,ko kad'an ran Aliyu bi yimasa dad'i ba Amma babu yanda zaiyi dole ya haqura tunda duk 'yan uwan nasa sun nuna amincewarsu, kafin kace me aka yanka sadaki dubu hamsin , nan take abokanan iyayen nasu su hud'u suka had'a kud'in suka ba qannen mahaifin Nuraddeen a matsayin tasu gudun mawar ga d'an nasu,
Hakan ba k'aramin sake farantawa baffa zuciya yayi ba tare da yiwa ALLAH godiya daya basa nagartaccin abokanai irinsu,
Abunda ALLAH yaso kuma yariga ya had'a ko ana so ko ba'a so to sai ya tabbata, a ranar su baba basu baro garinba har saida aka dindince ranar d'aurin auren nan da sati biyu masu zuwa tare da sadakin Rashida a hannunsu zuciyoyinsu cike da farinciki, nisawa mahaifin Rashida yayi yace "ALLAH mai iko kuma mai yin yanda yaso, mu da mukaje gano marar lafiya sai gashi mun dawo da sadakin 'yarmu a hannu, tabbas komai nada sanadi arayuwa, ubangiji ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi kuma ya had'e hankulansu waje d'aya" kowanensu ya amsa da "Amin" suna masu jinjina al-amarin ubangiji.
Aliyu kuwa suna tafiy bai zame ko Ina ba sai d'akin mahaifiyar Nuraddeen wato matar yayan nasa yay hawwa kmar yanda suke kiranta yana cika yana batsewa, nan ta taso tana tambayarsa ko lafiya ai kamar jira yakeyi ya zayyane mata qarya da gaskiya, ashar ta lailayo ta dire tna fad'in "ai wlh ba'a isa ba, yaushe har shi nuran yayi girman da ya isa yace ga wadda yake so da har za'aje ayo masa qulle qulle a aura masa wata can bare, to wlh bazan tab'a lamuntar wannan abun gori acikin dangi ba, haka kurum ajawo mani abun kunya da fad'a acikin gari, kowa yasan awannan garin namu auren zumunci akeyi, bamuda bare kuma ba'a tab'a kawo mana ita acikin gida ba, shikenan sai yanzu ace akan d'ana za'a fara?to wlh haka bazata sab'uba wai bindiga aruwa" wani farincikine ya rufe Aliyu yaci gaba da ingizata yana zugata haddasu cewa "Nima haka nagani yaya hawwa, Ina laifin ace ko muneera ce an had'asa da ita tunda tana sonsa amma wai antashi an had'asa da wacce batasan kimarmu da darajarmu ba, ga yaran cikin garin basuda mutunci da girmama na gabansu"
"Kai rufamun baki, muneera ko shashasha, tun yaushe nake cemata tadinga oqarin jawo hankalinsa amma takasa, shegiya mai gwalmad'ad'd'in qafafuwa ai koma meye laifin tane"
"Amma yaya hawwa kemafa kinsan yaronnan da baqin rai yake, har yaushe tag fuska balle taje tayi masa karairayar da zata jawo hankalinsa, yanzu dai ya kamata kisan abunyi kafin yarinyar nan tazo tarabamu da d'anmu ta tsigemu gaba d'aya"
"Kai Aliyu tofar da mugun yawun bakinan naka, wannan baqar fata har Ina, Bari naje wajen malan dole a ajiye wannan maganar" fiiiii...tanufi shigifar da baffa ke kwance ta iskosa yana jan carbi, masifa tafara zuba masa yana kallonta har ta gama sannan ya ajiye carbin agefe yace "yanzu ke hawwa awannan yanayin da nake ciki har kinada k'warin guiwar zuwa kiyi tsaye agabana kina wud'annan maganganun, to bari infad'a maki ko kina so ko bakya so sai anyi wannan auren tunda yana son yarinyar"
"Ni kuma bana son yarinyar, don haka bazai aureta ba"
"Saboda meye?"
"Saboda ita d'in barece"
"A'ina aka fad'i hakan, qur'ani yafad'a ne ko a'a?"
"A al'adar garinmu dai ce ba'a tab'a yin hakan ba kuma baza'a fara akan d'ana ba"
"Kaji shirmen banza, al'adar tafi alqur'anin ne? To Bari kiji wannan aure kamar anyi angama ne da yardar ALLAH"
"Amma malan inkayi mani haka bakayi mani adalci ba sabo..." Bata qarasa rufe baki ba yace
"Eh jeki naji d'in ni yanzu barci nakeji bana son wannan hayaniyar!"
Duk inda ran hawwa yake inyayi dubu yab'aci, tafice buuuu.kamar zata tashi sama tana maseefa, karo tayi da Usman akan hanyar tsakar gidan da yake family ne duk anan suke zune tafara yimasa qorafi, murmushi yayi sannan yace, "ikon ALLAH, to aike yaya hawwa banda addu'a babu abunda yakamata kiyi tunda shi yaganta kuma yace yana sonta, don ALLAH don annabi ki kwantar da hankalinki, mai k'aya ya daure kuma sai ace mai cira na kuka!?"
Aifa nan shima tayi masa tatas har tana k'arawa da cewa ai duk munafuccin da akayi dashi akayisa, shidai murmushi kawai yayi yawuce abunsa batare daya sake tankata ba, Aliyu ne ya iso wajen yana kallon irin hararar data raka d'an uwansa da ita yace,
"Ahaf! Ai infad'a maki yaya hawwa duk munafuccin agindinsa yake, shine nan ya qulla komai." Tsaki taja had'e da barin wajen tana fad'in, "sakarci, to kai meya hanaka kwancewa daya qulla, ai wlh duk sai nayi maganinku ga baki d'aya."
😨 _TIRQASHI! RASHIDA KINA CIKIN MATSALA, GASHI KEBA ILIMIN ZAMANI BALLE KI KWACI KANKI🤔🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️_
*_ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU👏😭_*
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___12💎
Kallo Aliyu yabi yaya hawwa dashi kafin yace "Kai wannan mata anyi fitinanniyar halitta anan, duk girmanka baza katab'a gwaninta awajenta ba, jarababbiya da ganinta kasan ba qaramin haquri yaya keyi da ita ba."
Kasa zaune da tsaye yaya hawwa tayi saboda tunanin hanyar da zatabi ta hana auren, in tayi nan tayi can kamar mai jiran sauraren wani sak'on, cije baki tayi aranta tana mai ayyana kalar uqubobin data tanadawa yarinyar matuqar bata samu nasarar ruguje auren ba,
Baba kuwa yana isa gida bakinsa ko rufuwa bayayi saboda tsananin farinciki yafara k'walawa Rashida kira alokacin ita kuma tana bayi tana wanka,
"A'a sannu da zuwa malan,lafiya naji kana k'wallawa 'yar taka kira tundaga zaure" tak'are zancen had'e da jawo tabarmar dake gefen d'aki ta shimfid'a masa sannan takoma d'aki ta d'auko ruwa masu sanyi takawo masa, fuskarsa cike da annuri ya nemi waje ya zauna sannan yace,
"Yawwa maman Rashida lafiya klw muka dawo, Ina ita Rashidar take, ko tayi islamiya ne?"
"A'a yanzunnan tashiga wanka, inaji yauma tayi latti ALLAH yakareta daga dukan malamai."
"Amin ya ALLAH" Yafad'a had'e da d'aukar ruwan data ajiye masa agabansa yasha,
"Malan shin ko abun sirrine tsakanin uba da 'yarsa naji kayi shiru, kai da naga kashigo da azamarka kamar Wanda akaba saqo yakawo mani." Murmushi yayi mata sannan yace
"To kusan dai kamar hakanne amma sak'on Kuma bake aka bawa ba 'yarmu aka ba."
"Tooo...! Kace dai harkar tason kaice, to bari nakama bakina, inbar uba da 'yarsa susha sha'aninsu"
"A'a ranki shidad'e ai abun bai kai can ba, ungo wannan riqe inyi maki bayani" ya ciro kud'i a aljihunsa ya mik'a mata, ansa tayi tana bin kud'in cike da mamaki kafin tace, "malan a ina kasamo wud'annan? Ina wajen ganin marar lafiya kuka tafi ko?"
"Eh a can mukaje?"
"To wud'annan kud'infa a ina aka samosu?"
"Kai maman Rashida wud'annan tambayoyin sunyi yawa, sai kace wanda yasato"
"To ai dole na tambaya saboda abun da mamaki!."
"kwantar da hankalinki to wannan sadakin Rashida ne kuma nan da sati biyu za'a d'aura auren in sha ALLAH..." bai qarasa zancen ba sukaji qarar fad'uwar bokiti daga toilet Rashida ta saki jin abunda kefitowa daga bakin mahaifin nata, atare umma da baba sukace,
"Ke lafiya?"