Sashe 74
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Aunty da gaske su ummata sun tafiyarsu?, Da gaske ba'asan inda suka tafi ba?, Shikenan bazan sake ganinsu ba?" Rashida tafad'a had'e da riqe hannuwanta tana kuka, cikin dakewa Fatima da tuni zuciyarta tayi rauni hawaye sun soma kaida kawo a fuskarta tace.
"A'a maman boy, Zaki ga su ummanki komai daren dad'ewa, hakan bayana nufin kun rabu bane Rashida sai dai kawai ubangijinki na auna imaninkine ta hanyar yimaki jarabawa wata bayan wata Kuma dama haka rayuwar mumini take, idan anyi masa jarabawa ya canye ta sai asake yimasa wata jarabawar wacce tafi tafarkon da akayi masa don kawai a d'aukaka darajarsa da kuma imaninsa idan ya canyesu, kiyarda cewa zasu dawo agareki nan kusa bada jimawa ba in Sha ALLAH." Cikin kuka tace
"Yaushe? Awane lokaci kuma aunty? Bayan zukatansu sunriga sunyi imanin cewa sun rasani kenan har abada."
"Kisa aranki cewa kusa zasu dawo, haba maman boy karki manta ALLAH subhanahu wata'ala yana cewa."
_"Laa taqnad'u min rahmatllah (kada mu kuskura muyanke qauna ga rahamar ALLAH)_"
"Don haka kada kicire tsammanin cewa rahamar ALLAH zatasa iyayenki sudawo matuqar kika miqa dukanin al'amurranki agaresa kamar yanda kikayi abaya, haqiqa wawa, lusari, Wanda baisan kanshi kad'aine ke rabka hannuwa yana tsammanin cewa ALLAH bazai jarabcesa ba bayan kuma yace yayi Imani, walh Rashida ALLAH da kansa ke cewa matuqar kukace kunyi Imani to."
_"wala nabluwannakum bi shai'in minal haufi wal ju'i wa naqsin min amfusi wassamarat, wabasshirisubirin, allazina iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa Inna ilaihirrajiuun, ma'ana idan kunyi Imani dani to (zamu jarabceku da abubuwan tsoro, da yunwa da rashin rayuka daga kawunanku da kuma tsirrai, muna yima masu haquri bushara wud'anda idan musiba tasamesu sai suce ga ALLAH mukazo Kuma agareshi zamu koma)"_
"Saboda haka ki daure ki zamo cikin bayinsa masu haquri da yake yiwa bushara kinji ko!"
Cikin kuka dake cike da sauti Rashida tafad'a jikinta tana fad'in.
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, allahummah thabbit aqadami wa haqqiq Imani,.."
Qarar kukan nata yajanyo hankalin su baba balarabe dake waje da sauri suka shigo cikin d'akin har suna rige rigen qarasowa bakin gadonta, tana ganinsu taqara fashewa da wani kukan had'e da rungume aunty marwiyya tana fad'in.
"Wayyo ummana.."
Babu yanda suka iya domin rasa iyaye tako wace irin fuska ce yanada matuqar rad'ad'i arai wanda dole ko ana so ko ba'aso awannan gab'ar dole abarta tayi kukan domin ko anhanata yinsa rad'ad'in da takeji azuciyarta bazai barta tahanu ba, sai da tayi mai isarta tayi shiru sannan tajaye daga riqon da tayiwa aunty marwiyya takwanta akan gado tana ajiyar zuciya har lokacin hawayen basu dena fita daga idanuwanta ba, sannu suka dinga yimata d'aya bayan d'aya tana amsawa had'e da binsu da kallo hawayen naci gaba da zubo mata.
Rarrashinta suka taru sunayi had'e da ban magana da dad'ad'an kalamai Amma gaba d'aya ita ba abunda take gani sai hoton fuskokin iyayen nata da batasan ranar da zata koma had'uwa dasu ba.
Gaba d'aya takasa tsaida zubar hawayenta wanda hakan yasa Dr nura yaje yakira Dr daya dubata yazo ya sake yimata allurar bacci bayan aunty marwiyya ta aza mata little daya fara qananun kuka tabashi nono yasha,
Bacci mai nauyi sosai ya d'auketa sannan baba balarabe yace da aunty marwiyya taje gida tunda dare yayi sosai lokacin qarfe d'aya da rabi,
Atafau tabuga kai ga qasa akan babu inda zataje anan zata kwana, don gani take za'a iya sake d'auketa idan taje gida kafin tadawo gobe da safe. Adole aka qyaleta tunda ta nace akan haka, Kiran mijinta tayi tasanar dashi anan zata kwana Kuma cikin sa'a ya amince mata don mutumne da baida matsala kuma ko bayan hka su biyu suke ga mijin nata shiyasa Bata damu da sai takoma gida ba.
Yaya maryam ma daqyar baba balarabe ya samu tabi mijinta sannna yajuyo yana kallon Fatima dake riqe da little yace.
"Fatima dake da Dr. Yakamata ku koma gida saboda akwai gajiyar tafiyar da kukayo kuna buqatar hutawa sosai, inyaso nida qanwar mahaifiyar ta zamu kwana anan idan Babu damuwa koda za'a buqaci sawo wani abu kunga ni Ina nan babu matsala."
Ji Fatima tayi kamar ta k'walla ihu don har ga ALLAH bataso barin asibitin ba amma saboda dr.nura ya amsa yasa dole babu yanda zatayi ta haqura ta miqawa aunty marwiyya little kamar zatayi kuka ta karb'esa sannan sukayi saida safe suka tafi sai tunzurar baki takeyi, kallonta yayi yana tuqi yayi murmushi had'e da cewa.
"Fatima meye abun b'acin rai naga kina turar baki haka?" Saida ta kallesa sannan ta maida kanta gefe tace.
"Meyasa kaima bakace anan zamu kwana ba, ALLAH bana son rabuwa da maman boy ita da little hisby d'innan nawa, shine kai harda wani miqewa da sauri irin bakama damu ba." 'yar dariya yayi daidai lokacin suka iso inda 'yan sandan dake security akan titi suke yayi slow da motar had'e da ciro i.d card d'insa ya nuna masu suna yayyada bayan motar da wajen boot sannan suka basa izinin wucewa.
Bayan sun wuce wajen ya juyo ya kalleta tare da aza hannunsa saman nata yace.
"Kiyi haquri kinji matar?, Ba haka nake nufi ba amma yakamata kisn cewa yanzu bamuda wani sauran iko akanta, mu kawai masu taimako ne, munemi cikar ladar taimakon da mukayi, kada mu nemi shiga hurumin da iyayenta kad'ai suke da haqqi akansa, kada mutauye ladarmu tahanyar nuna ra'ayin zukatanmu bayan munsan ayanzu sunfimu tsananin buqatar kasantuwa da ita, koba haka bama ai dole murabu dasu ko bama so, don haka daga yanzu kifara koyawa zuciyarki yanda zata jurewa rashinsu akusa damu kinji ko?"
Batare data amsa masa ba ta d'ora kanta kawai saman kafad'arsa tana shafa hannunsa har suka iso gida.
Shima baba balarabe kiran iyalansa yayi yace surufe gida shi sai gobe zai dawo.
••• ••• •••
Su baffa nadawowa daga filin jirgi suka harhad'a kud'ad'en da zasuje kai yaya hawwa asibiti tare da wata 'yar qaramar jikka da kowanensu yasa kayansa kala d'aya da zasuyi amfani dasu don sai gobe zasu dawo kasancewar akwai nisa sosai tsakanin kano da kuma sokoto garin shehu, wanda koda sun isa dawuri bazasu kammala abunda ya kaisu ba har sai dare yayi, don haka dole suyi haqurin juyowa gobe idan ALLAH yakaimu bayan sun kammala abunda sukeyi.
Bankwana sukayi da Inna Bilkisu bayan baffa Usman ya jadda mata da kada abar Yaya hawwa da yunwa kafin sudawo, suyi qoqari kota tagane su dinga ajiye mata abinci har ALLAH yadawo dasu lafiya sannan suka tafi, akan hanya sukaci karo da Inna ruqayya ita da baffa Ali tafe suna magana qasa qasa, kallo d'aya baffa Ali yayi masu ya d'auke kai Inna ruqayya kuwa harara ta zabaga masu had'e dayin tsuki tawuce tana fad'in.
"Qarya dai fure take ba 'ya'ya, Kuma raminta qurarrene, sunyi abu yasha masu kai, gashinan garin neman gira anrasa ido, ba'a samu yabo ba ansamu wahala."
Kanta baffa Usman yanufo ransa ab'ace baffa yariqe hannunsa had'e da cewa.
"Haba Usman kada kataya mahaukaci hauka, ai kabarta tafad'i abunda ke ranta domin da kanta take, tafi muje ko nine a matsayinta zanfad'i abunda yafi hakan musamman idan akwai b'acewa atattare dani." Yaja hannunsa suka tafi.
Yanajin sadda suka kwashe da dariya baffa Ali nafad'in.
"ALLAH dai yaraka taki gona."
Inna Bilkisu kuwa da kanta taje tabud'e d'akin Yaya hawwa ta ajiye mata abinci had'e dayin tsaye abakin qofar d'akin tana kallonta, ganin tayi ana buga Yaya hawwa ajikin bangon d'akin kafin a d'agata sama ayar qasa batasha mamaki ba sai da taga anjuyar da kanta gefe yana kallon sama sannan an mammal qwashe mata hannuwa sun koma baya, qafafuwanta kuma anbud'esu kowace anjata gefe, ahaka taga tana jan ciki tazo inda abincin yake tasa kanta ta turesa ya zube qasa sannan tafaraci da baki kamar yanda dabbobobi keyi, kuka ne ya qwacewa Inna Bilkisu ganin yanda aka maida ita kamar wata muguwar dabba da sauri taja qofar d'akin tarufe tabar wajen tana kuka, kobata tambaya ba tasan wannan aikin shed'anun aljanune don haka taje ta d'auko redionta tasa karatun qur'ani tanufi d'akin, da sauri Yusuf yariqota had'e da cewa.
"Inna Bilkisu kada kiyi haka, bakisan wud'anne kala bane kada garin taimako kema su nemi cutar dake, kibari tunda su baffa sunje nemamata mafita anema mata."
Wata qara sukajiyo daga d'akin da tasa yusuf jawo hannun Inna Bilkisu yana fad'in "kinji ko inna Bilkisu, ALLAH kimaida kada kitafi, ALLAH zai baki ladar niyar da kikayi."
Inna ruqayya da baffa Ali nashigowa kuwa tsuki sukaja had'e da cewa.
"Bisimillah, 'yar mahaukatannan tafara, wlh mukam dai anzaluncemu da aka ajiye manaita anan tana neman kashe mana kunne da baqar qara sai kace dujjal."
Dariya baffa ya kwashe da ita had'e da zuwa ta tagar d'akin yana leqen Yaya hawwa yace.
"Ikon ALLAH, ke ruqayya zo kiga yanda matarnan mai shegen cin zarafi da iya walaqanci ta koma, wlh kyace wata qwaguwa ce," leqawa tayi tafashe da dariya tace.
"Ala gwai, wlh naji dad'i, dubi qafafuwan shegiya uwa na lala tacciyar mace, ke muneera.."
Ta kwalawa muneera kira dake d'aki kwance tana bacci. Cikin magagin bacci tafito tana susar kai tace,
"Matso nan kiga Yaya hawwa dake maki sherin gwalmammin qafafuwa kiga yanda ALLAH yamayar mata da nata."
Leqawa muneera tayi had'e da murza idanuwanta don ta tabbatar da abunda suka gane mata da sauri ta jid'o had'e da cewa.
"Tab.. ALLAH Inna hawwa takoma uwa banqararriyar kaza."
Suka kece da dariya, shidai Yusuf da Inna Bilkisu nagefe suna mamakin yanda baffa Ali da Inna ruqayya kefitar da munanna kalamansu ga Yaya hawwa cike da isgilanci, sai kace ada ba itace wacce suka d'auka shugaba kuma aminiyar duk wasu shawarwarinsu da al'amurransu na duniya ba.....
_"'yar uwa shin ko kinsan da wud'anne kalar mutane kike rayuwa dasu acikin duniya?, shin kina iya banbancewa wud'anda ke sonki da kuma maqiyanki acikin mutanen dake zagaye dake?,sanin hakan nabuqatar natsuwa da kuma nazari, tabbas ni nakoyi darasin sanin cewa mutum mugune kuma bayada tabbas awajensu baffa Ali haka kuma na d'auki darasin zaunawa nagano banbancin masoyin gaskiya da kuma naqarya awajen Inna Bilkisu, nayarda cewa mutum bayada alqibla wajen rashin gano ainahin kalarsa. Don haka kema yiqoqari ki tsinci naki darasin acikin wannan littafin mai suna SANNU SANNU Bata hana zuwa.._🥰
"A'a maman boy, Zaki ga su ummanki komai daren dad'ewa, hakan bayana nufin kun rabu bane Rashida sai dai kawai ubangijinki na auna imaninkine ta hanyar yimaki jarabawa wata bayan wata Kuma dama haka rayuwar mumini take, idan anyi masa jarabawa ya canye ta sai asake yimasa wata jarabawar wacce tafi tafarkon da akayi masa don kawai a d'aukaka darajarsa da kuma imaninsa idan ya canyesu, kiyarda cewa zasu dawo agareki nan kusa bada jimawa ba in Sha ALLAH." Cikin kuka tace
"Yaushe? Awane lokaci kuma aunty? Bayan zukatansu sunriga sunyi imanin cewa sun rasani kenan har abada."
"Kisa aranki cewa kusa zasu dawo, haba maman boy karki manta ALLAH subhanahu wata'ala yana cewa."
_"Laa taqnad'u min rahmatllah (kada mu kuskura muyanke qauna ga rahamar ALLAH)_"
"Don haka kada kicire tsammanin cewa rahamar ALLAH zatasa iyayenki sudawo matuqar kika miqa dukanin al'amurranki agaresa kamar yanda kikayi abaya, haqiqa wawa, lusari, Wanda baisan kanshi kad'aine ke rabka hannuwa yana tsammanin cewa ALLAH bazai jarabcesa ba bayan kuma yace yayi Imani, walh Rashida ALLAH da kansa ke cewa matuqar kukace kunyi Imani to."
_"wala nabluwannakum bi shai'in minal haufi wal ju'i wa naqsin min amfusi wassamarat, wabasshirisubirin, allazina iza asabathum musibatun qalu innalillahi wa Inna ilaihirrajiuun, ma'ana idan kunyi Imani dani to (zamu jarabceku da abubuwan tsoro, da yunwa da rashin rayuka daga kawunanku da kuma tsirrai, muna yima masu haquri bushara wud'anda idan musiba tasamesu sai suce ga ALLAH mukazo Kuma agareshi zamu koma)"_
"Saboda haka ki daure ki zamo cikin bayinsa masu haquri da yake yiwa bushara kinji ko!"
Cikin kuka dake cike da sauti Rashida tafad'a jikinta tana fad'in.
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, allahummah thabbit aqadami wa haqqiq Imani,.."
Qarar kukan nata yajanyo hankalin su baba balarabe dake waje da sauri suka shigo cikin d'akin har suna rige rigen qarasowa bakin gadonta, tana ganinsu taqara fashewa da wani kukan had'e da rungume aunty marwiyya tana fad'in.
"Wayyo ummana.."
Babu yanda suka iya domin rasa iyaye tako wace irin fuska ce yanada matuqar rad'ad'i arai wanda dole ko ana so ko ba'aso awannan gab'ar dole abarta tayi kukan domin ko anhanata yinsa rad'ad'in da takeji azuciyarta bazai barta tahanu ba, sai da tayi mai isarta tayi shiru sannan tajaye daga riqon da tayiwa aunty marwiyya takwanta akan gado tana ajiyar zuciya har lokacin hawayen basu dena fita daga idanuwanta ba, sannu suka dinga yimata d'aya bayan d'aya tana amsawa had'e da binsu da kallo hawayen naci gaba da zubo mata.
Rarrashinta suka taru sunayi had'e da ban magana da dad'ad'an kalamai Amma gaba d'aya ita ba abunda take gani sai hoton fuskokin iyayen nata da batasan ranar da zata koma had'uwa dasu ba.
Gaba d'aya takasa tsaida zubar hawayenta wanda hakan yasa Dr nura yaje yakira Dr daya dubata yazo ya sake yimata allurar bacci bayan aunty marwiyya ta aza mata little daya fara qananun kuka tabashi nono yasha,
Bacci mai nauyi sosai ya d'auketa sannan baba balarabe yace da aunty marwiyya taje gida tunda dare yayi sosai lokacin qarfe d'aya da rabi,
Atafau tabuga kai ga qasa akan babu inda zataje anan zata kwana, don gani take za'a iya sake d'auketa idan taje gida kafin tadawo gobe da safe. Adole aka qyaleta tunda ta nace akan haka, Kiran mijinta tayi tasanar dashi anan zata kwana Kuma cikin sa'a ya amince mata don mutumne da baida matsala kuma ko bayan hka su biyu suke ga mijin nata shiyasa Bata damu da sai takoma gida ba.
Yaya maryam ma daqyar baba balarabe ya samu tabi mijinta sannna yajuyo yana kallon Fatima dake riqe da little yace.
"Fatima dake da Dr. Yakamata ku koma gida saboda akwai gajiyar tafiyar da kukayo kuna buqatar hutawa sosai, inyaso nida qanwar mahaifiyar ta zamu kwana anan idan Babu damuwa koda za'a buqaci sawo wani abu kunga ni Ina nan babu matsala."
Ji Fatima tayi kamar ta k'walla ihu don har ga ALLAH bataso barin asibitin ba amma saboda dr.nura ya amsa yasa dole babu yanda zatayi ta haqura ta miqawa aunty marwiyya little kamar zatayi kuka ta karb'esa sannan sukayi saida safe suka tafi sai tunzurar baki takeyi, kallonta yayi yana tuqi yayi murmushi had'e da cewa.
"Fatima meye abun b'acin rai naga kina turar baki haka?" Saida ta kallesa sannan ta maida kanta gefe tace.
"Meyasa kaima bakace anan zamu kwana ba, ALLAH bana son rabuwa da maman boy ita da little hisby d'innan nawa, shine kai harda wani miqewa da sauri irin bakama damu ba." 'yar dariya yayi daidai lokacin suka iso inda 'yan sandan dake security akan titi suke yayi slow da motar had'e da ciro i.d card d'insa ya nuna masu suna yayyada bayan motar da wajen boot sannan suka basa izinin wucewa.
Bayan sun wuce wajen ya juyo ya kalleta tare da aza hannunsa saman nata yace.
"Kiyi haquri kinji matar?, Ba haka nake nufi ba amma yakamata kisn cewa yanzu bamuda wani sauran iko akanta, mu kawai masu taimako ne, munemi cikar ladar taimakon da mukayi, kada mu nemi shiga hurumin da iyayenta kad'ai suke da haqqi akansa, kada mutauye ladarmu tahanyar nuna ra'ayin zukatanmu bayan munsan ayanzu sunfimu tsananin buqatar kasantuwa da ita, koba haka bama ai dole murabu dasu ko bama so, don haka daga yanzu kifara koyawa zuciyarki yanda zata jurewa rashinsu akusa damu kinji ko?"
Batare data amsa masa ba ta d'ora kanta kawai saman kafad'arsa tana shafa hannunsa har suka iso gida.
Shima baba balarabe kiran iyalansa yayi yace surufe gida shi sai gobe zai dawo.
••• ••• •••
Su baffa nadawowa daga filin jirgi suka harhad'a kud'ad'en da zasuje kai yaya hawwa asibiti tare da wata 'yar qaramar jikka da kowanensu yasa kayansa kala d'aya da zasuyi amfani dasu don sai gobe zasu dawo kasancewar akwai nisa sosai tsakanin kano da kuma sokoto garin shehu, wanda koda sun isa dawuri bazasu kammala abunda ya kaisu ba har sai dare yayi, don haka dole suyi haqurin juyowa gobe idan ALLAH yakaimu bayan sun kammala abunda sukeyi.
Bankwana sukayi da Inna Bilkisu bayan baffa Usman ya jadda mata da kada abar Yaya hawwa da yunwa kafin sudawo, suyi qoqari kota tagane su dinga ajiye mata abinci har ALLAH yadawo dasu lafiya sannan suka tafi, akan hanya sukaci karo da Inna ruqayya ita da baffa Ali tafe suna magana qasa qasa, kallo d'aya baffa Ali yayi masu ya d'auke kai Inna ruqayya kuwa harara ta zabaga masu had'e dayin tsuki tawuce tana fad'in.
"Qarya dai fure take ba 'ya'ya, Kuma raminta qurarrene, sunyi abu yasha masu kai, gashinan garin neman gira anrasa ido, ba'a samu yabo ba ansamu wahala."
Kanta baffa Usman yanufo ransa ab'ace baffa yariqe hannunsa had'e da cewa.
"Haba Usman kada kataya mahaukaci hauka, ai kabarta tafad'i abunda ke ranta domin da kanta take, tafi muje ko nine a matsayinta zanfad'i abunda yafi hakan musamman idan akwai b'acewa atattare dani." Yaja hannunsa suka tafi.
Yanajin sadda suka kwashe da dariya baffa Ali nafad'in.
"ALLAH dai yaraka taki gona."
Inna Bilkisu kuwa da kanta taje tabud'e d'akin Yaya hawwa ta ajiye mata abinci had'e dayin tsaye abakin qofar d'akin tana kallonta, ganin tayi ana buga Yaya hawwa ajikin bangon d'akin kafin a d'agata sama ayar qasa batasha mamaki ba sai da taga anjuyar da kanta gefe yana kallon sama sannan an mammal qwashe mata hannuwa sun koma baya, qafafuwanta kuma anbud'esu kowace anjata gefe, ahaka taga tana jan ciki tazo inda abincin yake tasa kanta ta turesa ya zube qasa sannan tafaraci da baki kamar yanda dabbobobi keyi, kuka ne ya qwacewa Inna Bilkisu ganin yanda aka maida ita kamar wata muguwar dabba da sauri taja qofar d'akin tarufe tabar wajen tana kuka, kobata tambaya ba tasan wannan aikin shed'anun aljanune don haka taje ta d'auko redionta tasa karatun qur'ani tanufi d'akin, da sauri Yusuf yariqota had'e da cewa.
"Inna Bilkisu kada kiyi haka, bakisan wud'anne kala bane kada garin taimako kema su nemi cutar dake, kibari tunda su baffa sunje nemamata mafita anema mata."
Wata qara sukajiyo daga d'akin da tasa yusuf jawo hannun Inna Bilkisu yana fad'in "kinji ko inna Bilkisu, ALLAH kimaida kada kitafi, ALLAH zai baki ladar niyar da kikayi."
Inna ruqayya da baffa Ali nashigowa kuwa tsuki sukaja had'e da cewa.
"Bisimillah, 'yar mahaukatannan tafara, wlh mukam dai anzaluncemu da aka ajiye manaita anan tana neman kashe mana kunne da baqar qara sai kace dujjal."
Dariya baffa ya kwashe da ita had'e da zuwa ta tagar d'akin yana leqen Yaya hawwa yace.
"Ikon ALLAH, ke ruqayya zo kiga yanda matarnan mai shegen cin zarafi da iya walaqanci ta koma, wlh kyace wata qwaguwa ce," leqawa tayi tafashe da dariya tace.
"Ala gwai, wlh naji dad'i, dubi qafafuwan shegiya uwa na lala tacciyar mace, ke muneera.."
Ta kwalawa muneera kira dake d'aki kwance tana bacci. Cikin magagin bacci tafito tana susar kai tace,
"Matso nan kiga Yaya hawwa dake maki sherin gwalmammin qafafuwa kiga yanda ALLAH yamayar mata da nata."
Leqawa muneera tayi had'e da murza idanuwanta don ta tabbatar da abunda suka gane mata da sauri ta jid'o had'e da cewa.
"Tab.. ALLAH Inna hawwa takoma uwa banqararriyar kaza."
Suka kece da dariya, shidai Yusuf da Inna Bilkisu nagefe suna mamakin yanda baffa Ali da Inna ruqayya kefitar da munanna kalamansu ga Yaya hawwa cike da isgilanci, sai kace ada ba itace wacce suka d'auka shugaba kuma aminiyar duk wasu shawarwarinsu da al'amurransu na duniya ba.....
_"'yar uwa shin ko kinsan da wud'anne kalar mutane kike rayuwa dasu acikin duniya?, shin kina iya banbancewa wud'anda ke sonki da kuma maqiyanki acikin mutanen dake zagaye dake?,sanin hakan nabuqatar natsuwa da kuma nazari, tabbas ni nakoyi darasin sanin cewa mutum mugune kuma bayada tabbas awajensu baffa Ali haka kuma na d'auki darasin zaunawa nagano banbancin masoyin gaskiya da kuma naqarya awajen Inna Bilkisu, nayarda cewa mutum bayada alqibla wajen rashin gano ainahin kalarsa. Don haka kema yiqoqari ki tsinci naki darasin acikin wannan littafin mai suna SANNU SANNU Bata hana zuwa.._🥰