Sashe 122
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ba kunya little ya d'aga kai Rashida tayi murmushi had'e da d'auke kai tana qoqarin barin wajen tace.
"Wayaga god'ai god'ai, ALLAH yatsari jariri idan haka yake!,"
Yanda tayi yasa Dr sakinsa tare da bushewa da dariya yana fad'in.
"A'a maman little banda cin gira fa kusa ga ido, har yanzu takwarana jaririne, zo muje kafad'amun idan akwai sauran abubuwan da kake buqata kafin gobe." Yaja hannunsa tare da ficewa.
Rashida kuwa girgiza kai kawai tayi tana 'yar dariya taqarasa shigewarta batare da tabi takansu ba.
Gidan amare kam yasha kyau musamman na batool da gaba d'aya saida su uncle suka cika mata d'akunan da kayan d'aki masu kyau don duka kayan nawajene hatta kayan kitchens d'inta suma daga waje su Uncle h sukasa akayo odarsu, duk wata gata da suke tunanin mahaifinta nada niyar yimata sunyi mata fiye da hakan, babban falonta kad'ai saitin kujeru biyu aka zuba mata aciki, qarami kuma saiti d'aya, sai kayan gado d'aki biyu aka samata su tare da wata qatuwar katifa a d'an qaramin d'akin dake cikin gidan Wanda kamar an tanadesa ne saboda yara ko baqi da doguwar wadrobe had'e da cheat of drawer aciki, komai dai yaji Masha ALLAH, nera tasha kashi sosai don su uncle sun bud'e bakin aljifansu duk da ba itace 'ya tafarko da suka fara aurarwa agidan ba, amma amatsayinta na 'yar gaban goshin yayan nasu sun nunama duniya cewa tabbas itad'in 'yar gatace, duk wanda ya shiga gidan yafito sai kaji yana fad'in albarkacin bakinsa, wasuma har suna kiran little ya tako arziqi, hakama a b'angaren iman iyayenta sunyi qoqari matuqa sunsa mata komai daidai qarfinsu, inda Shakur ya sake zage damtse wajen ganin yasa duk abunda yaga batada shi saboda gudun 'yan gutsuri tsoma musamman da yaji mahaifiyarsa na zancen irin kayan da aka narkawa batool agidan little, har tana fad'in da yanzu suke dasu ankayi masu baqinciki saboda sonkai.
Kwanci tashi ba wuya awajen ALLAH haka ita SANNU SANNU bata hana zuwa saidai adad'e ba akai ba, abunda duk aka sawa rana kuma to tabbas qararrene, yau misalin qarfe 12:30 na rana dubban mutane suka sheda d'aurin auren NURADDEEN NURADDEEN IDRIS ALIYU (LITTLE) DA AMARYARSA FATIMA UMAR FARI, a nan anguwar sharad'a phase 1 dake cikin kano inda yasamu halartar manya manyan baqi ciki harda mataimakin gwamna jahar da ciyamoma da manyan 'yan kasuwa na cikin gida da waje don babu wanda su uncle h basu gayyato ba, kama daga kan abokanan yayan nasu(Abba) har zuwa nasu abokanan, 'yan uwa da abokan arziqi, mutanen anguwa, mutanen gari nakusa dana nesa hakan yasa anguwar tacika maqil ko masokar tsintsiya babu, duk inda ka duba manyan motocine sai huci sukeyi tamkar ana cidasu, abunka ga sanannen mutum wanda akasan dashi nan take 'yan gidan redio da television suka isa wajen suna d'aukar rahoton yanda ake gudanar da d'aurin auren, duban irin karamci da halaccin dasu dady suka yiwa jininsa yasa baffa yaroqi dady daya zamo wakilin ango ma'ana ya karb'ar masa auren batool a hannun iyayenta, shi kuma dady sai yace yabarwa baba balarabe, nan shima yace a'a yabar masa ya amsa kawai, ganin abun nasu yakoma jayayya yasa baffa Usman yace, Dr nura yaje yakarb'o masa auren sun nad'asa waliyin ango dama shiyafi dacewa don shine ubansa su duka karambanine zasuyi, ba tare da bata lokaciba kuwa nan take yaje aka gudanar da d'aurin auren dama tuni anbada sadaki don haka sai abun bai wani d'auki dogon lokaci ba.
Ana kammalawa motoci suka fara kwasar mutane zuwa d'akin taron da za'a gudanar da walima, sai dai shi baba balarabe da baffa Usman da bashar(abbaty) d'and'an Dr wanda shine babban abokin ango tunda bawani girme masa yayi ba dasu Hassan da Hussain 'ya'yan baba balarabe su suka tsaya wajen gudanar da walimar tare da ango, su kuma su dady, Dr, baffa, juyawa sukayi suka koma borno don misalin qarfe 2:30 na rana za'a d'aura auren Shakur da amaryarsa hafsat (iman) dama booking d'in jirgi sukayi ya kawosu Kuma shi zasubi su koma saboda yanayin lokaci mota bazata bari su isa dawuri ba, da da baba balarabe za'aje sai dady yace akwai buqatar ace iyayen ango sun halarci walimar, don haka sai ya tsaya akaje da baffa da mijin aunty marwiyya.
Suna Isa kai tsaye suka nufi wajen d'aurin auren Shakur don har lokaci yasoma qurewa dama dady yabar amininsa da faruk su tsaya tare da Shakur koda sunyi lattin dawowa, suna zuwa aka fara gudanar da d'aurin auren wanda anan ma Dr shiya karb'arwa qanensa shakur auren iman.
Bayan an kammala d'aurin auren mutane suka hallara zuwa qofar gidan Dr wanda sai alokacin Rashida takira Dr tafad'a masa akwai reception d'in data had'awa 'yan d'aurin aure anan gidansa idan an kammala, wanda ita ta shiryashi da kud'inta batare da sanin kowa ba si Fatima data fad'awa don komai odarsa tayo a restaurant, nan take Dr ya sanar da dady akayi sanarwa akwai reception a anguwarsu Dr. dama dakon mutane kenan kamar yanda abun yasoma zama al'ada yanzu don haka suka nufi gidan Dr wanda tuni ankafa qatuwar rumfa da kujeru awajen, wasu kuma mutanen suka tafiyarsu saboda wasu uzurukka nasu, bayan kowa yaci yasha ya qoshi shakur yashiga har cikin gida yayiwa Rashida godiya sannan shida abokanansa suka nufi gidansu iman don d'aukar hotuna.
••• ••• •••
A can kano kuwa saida aka gama kwashe kowa aka kai can inda za'ayi walima sannan su Uncle h suka zo suka d'auki amarya batool, matar uncle Hussain da amaryar Abba wato kishiyar hajia mama su suka riqota har zuwa cikin mota, sanye take da royal blue lace yasha fararen fulawowi masu fad'i ajikinsa anyi mata d'unkin riga da sket, sai wata qatuwar alkibba fara tas itama daga saman kai ayi mata aiki da royal blue d'in zare haka agaban rigar da bayanta an qawatashi shima, kallo d'aya zakayi mata ka hango tsantsar farincikin dake tattare da ita don takasa b'oye hakan, kasancewar ita d'in kyakkyawa ce ta ajin farko yasa bata wani bari aka cika mata fuska da irin kwalliyar nan da ake yayi ba sai dai 'yar kad'an data qara fiddo mata da kyanta na asali sai qamshi take zubawa tayi matuqar kyau tubarkallah masha ALLAH abunka ga farar macce da blue d'in abu ke matuqar amsa.
Batare da b'ata lokaci ba uncle Hussain yaja motar suka bar wajen, Abba kuwa dake can bayan corridor d'akinsa zaune bisa resting chair idanuwansa arufe miqewa yayi yakoma cikin d'aki yarufe yanajin wani irin rad'ad'i azuciyarsa, tabbas yau ya yarda da bahaushe dake cewa son zuciya b'acin zuciya..Wai yau 'yarsa da yafi so fiye da komai aduniya itace ke farinciki bayan baqin cikinsa, itace tazab'i bijire masa akan zab'inta, ta yarda tarasa gatar da yake bata taje ta zauna da wani marar asali matsiyaci da baisan darajarta ba, ta zauna da mutanen da basuda wata kima da daraja a idanuwan mutane, idan kuwa hakane dole a matsayin sa na mahaifi daya reneta cikin kulawa har takawo wannan girman yanuna mata kuskurenta na fifita wasu akansa.
A can wajen walima kuwa tunda aka shiga da ita idanuwan little ke kanta ko qyabtawa bayayi, ganin an nufo wajen da ita yasa little qoqarin miqewa da sauri abbaty yaja rigarsa yakoma ya zauna.
"Little meye haka?, Duk idanuwan taron nan fa na akanka, ina zakaje idan katashi?"
Sai alokacinma little yafahimci ko meyake son yayi yayi saurin duba gefe da gefensa yana murmushi tare da sunkuyar da kansa qasa yana sosa qeyar kansa, qasa yayi da muryarsa had'e da cewa.
"Old man." Don haka yake kiransa saboda sunan marigayi baba dake garesa.
"Ya akayi?, in baka waje zaka tafine?"
"Haba! Bahaka nake nufi ba, bakaga yanda gimbiya tayi kyau bane!, Sak tafito a gimbiyarta wanda kamata yayi ace awannan lokacin nazama srki, ya kake tunanin abun zai kasance."
Saida abbaty yaui dariya sannan yakai bakinsa wajen kunnensa had'e da cewa.
"Abun zai matuqar burgewa, Amma kayi qoqarin farkawo daga mafarkin da kakeyi inba haka ba ko yanzu kazamo sarkin marasa kunyoyi awajen nan!"
Da sauri ya juyo suka had'a ido dashi ya kad'a masa kai alamun tabbatar masa da abunda yafad'a had'e da d'an turo masa idanuwansa.
Hakan yasa yayi saurin tattaro natsuwarsa zuwa ga sauraren wa'azin, bini bini yake juyawa ya kalli batool dake can kan kujera saiti dashi a gefen da mata suke, malamai sunyi wa'azi sosai akan zamantakewar aure da kuma neman aljannah, mutuntaka da kuma girmama rayuwar d'an Adam, muhimmancin riqo da addinin da kuma kariyar da take bayarwa acikin aure, tausayi tsakanin ma'aurata da taimakekeniyar juna, yiwa juna uzuri tare da fahimtar juna, kyakkyawar zamantakewa da iyaye da kuma 'yan uwa had'i da mutanen gari, haquri, juriya da Kuma yiwa juna uzuri acikin rayuwar aure, duk da ba awaje d'aya suke zaune ba alokaci d'aya zukatansu sun quduri riqe junansu amana bisa wud'annan kyawawan nasihu da suka fito daga bakin manyan malamai tare dayin alwashin aiki da duka nasihohin da suka saurara.
"Wayaga god'ai god'ai, ALLAH yatsari jariri idan haka yake!,"
Yanda tayi yasa Dr sakinsa tare da bushewa da dariya yana fad'in.
"A'a maman little banda cin gira fa kusa ga ido, har yanzu takwarana jaririne, zo muje kafad'amun idan akwai sauran abubuwan da kake buqata kafin gobe." Yaja hannunsa tare da ficewa.
Rashida kuwa girgiza kai kawai tayi tana 'yar dariya taqarasa shigewarta batare da tabi takansu ba.
Gidan amare kam yasha kyau musamman na batool da gaba d'aya saida su uncle suka cika mata d'akunan da kayan d'aki masu kyau don duka kayan nawajene hatta kayan kitchens d'inta suma daga waje su Uncle h sukasa akayo odarsu, duk wata gata da suke tunanin mahaifinta nada niyar yimata sunyi mata fiye da hakan, babban falonta kad'ai saitin kujeru biyu aka zuba mata aciki, qarami kuma saiti d'aya, sai kayan gado d'aki biyu aka samata su tare da wata qatuwar katifa a d'an qaramin d'akin dake cikin gidan Wanda kamar an tanadesa ne saboda yara ko baqi da doguwar wadrobe had'e da cheat of drawer aciki, komai dai yaji Masha ALLAH, nera tasha kashi sosai don su uncle sun bud'e bakin aljifansu duk da ba itace 'ya tafarko da suka fara aurarwa agidan ba, amma amatsayinta na 'yar gaban goshin yayan nasu sun nunama duniya cewa tabbas itad'in 'yar gatace, duk wanda ya shiga gidan yafito sai kaji yana fad'in albarkacin bakinsa, wasuma har suna kiran little ya tako arziqi, hakama a b'angaren iman iyayenta sunyi qoqari matuqa sunsa mata komai daidai qarfinsu, inda Shakur ya sake zage damtse wajen ganin yasa duk abunda yaga batada shi saboda gudun 'yan gutsuri tsoma musamman da yaji mahaifiyarsa na zancen irin kayan da aka narkawa batool agidan little, har tana fad'in da yanzu suke dasu ankayi masu baqinciki saboda sonkai.
Kwanci tashi ba wuya awajen ALLAH haka ita SANNU SANNU bata hana zuwa saidai adad'e ba akai ba, abunda duk aka sawa rana kuma to tabbas qararrene, yau misalin qarfe 12:30 na rana dubban mutane suka sheda d'aurin auren NURADDEEN NURADDEEN IDRIS ALIYU (LITTLE) DA AMARYARSA FATIMA UMAR FARI, a nan anguwar sharad'a phase 1 dake cikin kano inda yasamu halartar manya manyan baqi ciki harda mataimakin gwamna jahar da ciyamoma da manyan 'yan kasuwa na cikin gida da waje don babu wanda su uncle h basu gayyato ba, kama daga kan abokanan yayan nasu(Abba) har zuwa nasu abokanan, 'yan uwa da abokan arziqi, mutanen anguwa, mutanen gari nakusa dana nesa hakan yasa anguwar tacika maqil ko masokar tsintsiya babu, duk inda ka duba manyan motocine sai huci sukeyi tamkar ana cidasu, abunka ga sanannen mutum wanda akasan dashi nan take 'yan gidan redio da television suka isa wajen suna d'aukar rahoton yanda ake gudanar da d'aurin auren, duban irin karamci da halaccin dasu dady suka yiwa jininsa yasa baffa yaroqi dady daya zamo wakilin ango ma'ana ya karb'ar masa auren batool a hannun iyayenta, shi kuma dady sai yace yabarwa baba balarabe, nan shima yace a'a yabar masa ya amsa kawai, ganin abun nasu yakoma jayayya yasa baffa Usman yace, Dr nura yaje yakarb'o masa auren sun nad'asa waliyin ango dama shiyafi dacewa don shine ubansa su duka karambanine zasuyi, ba tare da bata lokaciba kuwa nan take yaje aka gudanar da d'aurin auren dama tuni anbada sadaki don haka sai abun bai wani d'auki dogon lokaci ba.
Ana kammalawa motoci suka fara kwasar mutane zuwa d'akin taron da za'a gudanar da walima, sai dai shi baba balarabe da baffa Usman da bashar(abbaty) d'and'an Dr wanda shine babban abokin ango tunda bawani girme masa yayi ba dasu Hassan da Hussain 'ya'yan baba balarabe su suka tsaya wajen gudanar da walimar tare da ango, su kuma su dady, Dr, baffa, juyawa sukayi suka koma borno don misalin qarfe 2:30 na rana za'a d'aura auren Shakur da amaryarsa hafsat (iman) dama booking d'in jirgi sukayi ya kawosu Kuma shi zasubi su koma saboda yanayin lokaci mota bazata bari su isa dawuri ba, da da baba balarabe za'aje sai dady yace akwai buqatar ace iyayen ango sun halarci walimar, don haka sai ya tsaya akaje da baffa da mijin aunty marwiyya.
Suna Isa kai tsaye suka nufi wajen d'aurin auren Shakur don har lokaci yasoma qurewa dama dady yabar amininsa da faruk su tsaya tare da Shakur koda sunyi lattin dawowa, suna zuwa aka fara gudanar da d'aurin auren wanda anan ma Dr shiya karb'arwa qanensa shakur auren iman.
Bayan an kammala d'aurin auren mutane suka hallara zuwa qofar gidan Dr wanda sai alokacin Rashida takira Dr tafad'a masa akwai reception d'in data had'awa 'yan d'aurin aure anan gidansa idan an kammala, wanda ita ta shiryashi da kud'inta batare da sanin kowa ba si Fatima data fad'awa don komai odarsa tayo a restaurant, nan take Dr ya sanar da dady akayi sanarwa akwai reception a anguwarsu Dr. dama dakon mutane kenan kamar yanda abun yasoma zama al'ada yanzu don haka suka nufi gidan Dr wanda tuni ankafa qatuwar rumfa da kujeru awajen, wasu kuma mutanen suka tafiyarsu saboda wasu uzurukka nasu, bayan kowa yaci yasha ya qoshi shakur yashiga har cikin gida yayiwa Rashida godiya sannan shida abokanansa suka nufi gidansu iman don d'aukar hotuna.
••• ••• •••
A can kano kuwa saida aka gama kwashe kowa aka kai can inda za'ayi walima sannan su Uncle h suka zo suka d'auki amarya batool, matar uncle Hussain da amaryar Abba wato kishiyar hajia mama su suka riqota har zuwa cikin mota, sanye take da royal blue lace yasha fararen fulawowi masu fad'i ajikinsa anyi mata d'unkin riga da sket, sai wata qatuwar alkibba fara tas itama daga saman kai ayi mata aiki da royal blue d'in zare haka agaban rigar da bayanta an qawatashi shima, kallo d'aya zakayi mata ka hango tsantsar farincikin dake tattare da ita don takasa b'oye hakan, kasancewar ita d'in kyakkyawa ce ta ajin farko yasa bata wani bari aka cika mata fuska da irin kwalliyar nan da ake yayi ba sai dai 'yar kad'an data qara fiddo mata da kyanta na asali sai qamshi take zubawa tayi matuqar kyau tubarkallah masha ALLAH abunka ga farar macce da blue d'in abu ke matuqar amsa.
Batare da b'ata lokaci ba uncle Hussain yaja motar suka bar wajen, Abba kuwa dake can bayan corridor d'akinsa zaune bisa resting chair idanuwansa arufe miqewa yayi yakoma cikin d'aki yarufe yanajin wani irin rad'ad'i azuciyarsa, tabbas yau ya yarda da bahaushe dake cewa son zuciya b'acin zuciya..Wai yau 'yarsa da yafi so fiye da komai aduniya itace ke farinciki bayan baqin cikinsa, itace tazab'i bijire masa akan zab'inta, ta yarda tarasa gatar da yake bata taje ta zauna da wani marar asali matsiyaci da baisan darajarta ba, ta zauna da mutanen da basuda wata kima da daraja a idanuwan mutane, idan kuwa hakane dole a matsayin sa na mahaifi daya reneta cikin kulawa har takawo wannan girman yanuna mata kuskurenta na fifita wasu akansa.
A can wajen walima kuwa tunda aka shiga da ita idanuwan little ke kanta ko qyabtawa bayayi, ganin an nufo wajen da ita yasa little qoqarin miqewa da sauri abbaty yaja rigarsa yakoma ya zauna.
"Little meye haka?, Duk idanuwan taron nan fa na akanka, ina zakaje idan katashi?"
Sai alokacinma little yafahimci ko meyake son yayi yayi saurin duba gefe da gefensa yana murmushi tare da sunkuyar da kansa qasa yana sosa qeyar kansa, qasa yayi da muryarsa had'e da cewa.
"Old man." Don haka yake kiransa saboda sunan marigayi baba dake garesa.
"Ya akayi?, in baka waje zaka tafine?"
"Haba! Bahaka nake nufi ba, bakaga yanda gimbiya tayi kyau bane!, Sak tafito a gimbiyarta wanda kamata yayi ace awannan lokacin nazama srki, ya kake tunanin abun zai kasance."
Saida abbaty yaui dariya sannan yakai bakinsa wajen kunnensa had'e da cewa.
"Abun zai matuqar burgewa, Amma kayi qoqarin farkawo daga mafarkin da kakeyi inba haka ba ko yanzu kazamo sarkin marasa kunyoyi awajen nan!"
Da sauri ya juyo suka had'a ido dashi ya kad'a masa kai alamun tabbatar masa da abunda yafad'a had'e da d'an turo masa idanuwansa.
Hakan yasa yayi saurin tattaro natsuwarsa zuwa ga sauraren wa'azin, bini bini yake juyawa ya kalli batool dake can kan kujera saiti dashi a gefen da mata suke, malamai sunyi wa'azi sosai akan zamantakewar aure da kuma neman aljannah, mutuntaka da kuma girmama rayuwar d'an Adam, muhimmancin riqo da addinin da kuma kariyar da take bayarwa acikin aure, tausayi tsakanin ma'aurata da taimakekeniyar juna, yiwa juna uzuri tare da fahimtar juna, kyakkyawar zamantakewa da iyaye da kuma 'yan uwa had'i da mutanen gari, haquri, juriya da Kuma yiwa juna uzuri acikin rayuwar aure, duk da ba awaje d'aya suke zaune ba alokaci d'aya zukatansu sun quduri riqe junansu amana bisa wud'annan kyawawan nasihu da suka fito daga bakin manyan malamai tare dayin alwashin aiki da duka nasihohin da suka saurara.