Sashe 71
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To mungode, Kai Nuraddeen kaji abunda tafad'a, me kace."
"Ni zan iya kulawa da mahaifiyata koma a inane, kawai ni bana buqatar zamanta ne a hannun wud'annan mutanen."
Shiru sukayi kafin sufice waje suna tattaunawa akan inda yakamata akaita daga qarshe suka yanke shawarar ajiyeta can gida a d'akinta, ciro waya baffa Usman yayi yakira maqwabcinsu dake jigilar motar haya,
Bayan mintuna sai gashi yazo da motarsa sukaje aka d'auko Yaya hawwa tana kucce kucce, aka sata baya sannan Nuraddeen shima ya shiga ya riqeta, kallon baffa Usman baffa yayi yace yashiga gaba, shi zai biyosu abaya ya shiga suka wuce,
Godiya ya sake yiwa inspector najida sannan ya nemi Mai mashin ya hau yabi bayansu.
Ba qaramar wahala Nuraddeen yasha ba kafin su isa gida don duk ta yakusheshi, haka ma da zasu shigar da ita daqyar da sud'in goshi yasamu yashigar da ita cikin gida har d'akinta don hana kowa ya tab'ata yayi ganin yanda sai ihu da dariya yaran shiya ke yimata.
Baffa na saman mashin ya kira baba balarabe yana tambayarsa jikinsu baba balarabe, nan ya sheda masa halin da ake ciki na b'atansu, baffa yashiga tashin hankali sosai marar misaltuwa yashiga sallallami har ya iso gidan, yana isowa ya tadda baffa Usman tsaye shida baffa Ali yana surfa masa masifa akan don me za'a kawo masu mahaukaciya acikin gida tahanasu bacci ta illata masu iyali, yana ganin baffa ya d'aure fuska had'e da zunduma ashar sannan yabar wajen, baffa dake cikin alhini da damuwan b'atan iyayen Rashida kota kansa bebiba balle yadamu da abunda yayi masa yashiga yima baffa Usman bayanin abunda ke faru.
"Astagfirullah, astagfirullah, astagfirullah ALLAH ka sassauta mana wannan jarabawar dake b'ullo mana d'aya bayan d'aya." Baffa Usman yafad'a yana zabga uban tagumi, ahaka Nuraddeen ya taraddasu baffa yayi masa bayani, awannan karon damuwa tayi masa nauyin da bayada kuzarin yin kuka balle ya zubar da hawaye, gefen baffa ya zauna ya d'ora kansa saman kafad'arsa ko zai samu sassaucin yanayin da yakejin kansa aciki, tabbas ubangiji baya zalunci kuma baya goyawa mai zalunci baya domin yayi hani da hakan, haqiqa halin da mahaifiyarsa ke ciki ta cancanci zama ciki fiye da hakan saboda haqqin wud'annan bayin ALLAH da tayi sanadiyar fad'awarsu cikin wani hali suda 'yarsu,
A hankali ya d'ago kansa yana kallon baffa yace.
"Baffana shin kana fushi da inna ne har yanzu?."
"A'a Nuraddeen bana fushi da ita Amma aduk lokacin dana tuna cewa ita wani sashece acikin rayuwata kuma mahaifiyar d'ana nakanji ba dad'i."
"Kayafe mata Baffa nasan hakan zaisa tasamu sassucin halin da take ciki."
"Ko kad'an Nuraddeen bani tunanin haqina na daga cikin dalilan da ALLAH ke hukuntata domin tun aranar da ALLAH ya wanzar da tsinkewar alaqar dake tsakaninmu nayafe mata dukkanin haqqina dake kanta kuma ALLAH shine sheda akan haka."
Sake maida kansa yayi saman kafad'ar tasa sannan yace.
"Kayi haquri baffana, haqiqa dukanin mumini baya kaucewa jarabawarsa, in Sha ALLAH da sannu quncinmu zai koma farinciki."
"ALLAH ya qaddara hakan Nuraddeen."
Cike da tausayi baffa Usman ke kallonsu, haqiqa ALLAH shi yake fidda farin tuwo acikin baqar tukunya kamar yanda ya fidda Nuraddeen acikin Yaya hawwa, Wanda gaba d'aya kyawawan halayensa na mahaifinsa ne ya gado, sunjima awajen kafin akira sallar la'asar suje suyo SALLAH sannan suka kama hanyar yarimawa.
Gidan baba balarabe suka sauka suka jajanta masa akan abunda yafaru kafin sujuyo sudawo gida.
Da daddare suna zaune sunacin abinci sukaji sanarwar batun tafiyarsu Nuraddeen nan da kwana uku ana masu aqa gargad'insu dasu kasance cikin shiri, Nuraddeen na kallon yanda yanayin fuskar baffa takoma lokacin da aka fara sanarwar har aka gama yana saurare yayi ajiyar zuciya had'e da cewa Allah ya sawaqe.
Cikin kwanaki ukun da suka rage kullum Nuraddeen shike zuwa da kansa d'akin Yaya hawwa da aka kulleta ciki ya bata abincin safe rana da kuma dare, haka kuma yakanyi qoqarin gusar mata da duk wata najasa da tayi da dattin dake taruwa cikin d'akin, Bata barin qazanta ko kad'an atattare da ita koda kuwa tana dukan sane har sai yaga ya tsaftace ta.
Shi kuma baffa tuni suka gama yanke shawarar Kai Yaya hawwa asibitin mahaukata ta uduth dake jahar sokoto wanda tafiyar takama ranar dasu Nuraddeen zasu wuce, shire shire kawai baffa keyi nakai Yaya hawwa asibitin batare daya koma kula zancen maganar tafiyarsu Nuraddeen ba saboda yanda yaga yafita batun abun,
Da daddare awayi safiyar ranar baffa na zaune shida baffa Usman suna fira saiga Nuraddeen yadawo kayansa duk ajiqe sanadiyar ruwan saman da akayi suka yimasa duka, binsa da kallo sukayi har yaje yacire kayan jikinsa ya canzo wasu yazo ya zauna inda suke yana mai saqale hannuwansa waje d'aya ya d'ora akn qirji,
"A'a, Nuraddeen daga Ina kake haka ruwa sukayi maka duka?." Baffa Usman yafad'a yana kallonsa, saida ya kalli mahaifinsa dake qoqarin had'o tea a cup sannan yace.
"Daga wajen bankwana nake baffa Usman."
Miqo masa cup d'in tea daya had'a Mai zafi har yana tururi baffa yayi had'e da cewa.
"Bankwana fa kace Nuraddeen, Ina zaka jene?"
Saida ya kurb'i tea d'in yana sake motsasa da cokalin dake ciki saboda zafinsa sannan yace.
"Baffa kayi hak'uri bisa qin fahimtarka da nayi akan maganar tafiyata, a yanzu amince zanje saboda gujewa dana sanin rashin amfani da damar dake iya zowa mutum sau d'aya arayuwarsa, zanje nayi karatu, karatun da zansa kuyi alfahari dani har iya qarshen rayuwata, karka manta lokacin da kake jinya kaso ace d'aya daga cikin zuri'arku yayi karatu a fannin lafiya, to tabbas zan cika maka wannan burin da yardar ALLAH, al-amarin innar mu da Rashida kuwa, wa'ufawwidu amri ilallah, natabbata zai dafa maka wajen kula da komai, don haka shirin da nayi bazan warwaresa ba, da yardar ALLAH zantafi."
Kallo baffa Usman baffa yayi mumushi d'auke da fuskarsa yace.
"Kaji ko Usman, dama nafad'a maka bazan takura Nuraddeen ba, bazan tilasta saba amma ina da yaqinin bazai Bari wannan damar da ALLAH yabamu tawuce Saba."
"Alhamdulillah haqiqa naji dad'in sauya wannan hukuncin da kayiwa kanka da kayi, ubangiji ALLAH yayi maka albarka yasa kaje cikin sa'a, ALLAH yafaranta zuciyarka ybka kariya aduk inda kake kuma yayi maka jagora.."
Haka baffa yaci gaba da kwararo masa addu'o'i yana riqe da hannunsa baffa Usman na tayashi fuskokinsu d'auke da farinciki, murmushi Nuraddeen yayi ganin haka a fuskarsu had'e da cewa.
"Saidai baffa nakasa zuwa wajen baba balarabe inyi masa bankwana saboda rashin sanin da wace irin fuska zan kallesa in iya fad'a masa cewa zanje karatu waje a daidai lokacin da nine na zamo silar b'atan 'yarsa da kuma iyayenta.
"Karka damu Nuraddeen nasan bayada matsala zai fahimceka, Amma yanzu lokaci yaqure saboda qarfe bakwai naji ance zaku had'u a babbar ma'aikatar jahar nan don qarfe takwas jirginku zai tashi, don haka ni zani magantu dashi da yardar ALLAH kaji ko?"
"Shikenan baffa babu damu." Yafad'a tare da shanye sauran tea n ya ajiye cup d'in agefe, hannu yasa aljihu ya fiddo kud'i ya miqawa baffa.
"Ga wannan baffa, Inna Bilkisu ce da sauran mutanen gida da naje yimasu bankwana suka bani, banso karb'a ba Amma sun tilasta adole na karb'a."
"ALLAH sarki, angode ALLAH yabada ladar zumunci,"
"Amin baffa."
"Yawwa Usman ka tayamu godiya idan kaje, ALLAH yasaka da alkhairi."
"Amin Yaya Babu komai ai yiwa kaine." Baffa usman yafad'a yana murmushi.
Nan suka shiga fira tare dayi masa nasihohi kala kala akan yariqe addininsa da al'adunsu nad'an bahaushe idan yaje kafin baffa yaje ya d'auko kud'ad'en da yake ajiya saboda tafiyar. Saida yasake qidanyasu dubu d'ari biyu da ashirin don ya tab'a wasu ma sannan ya miqawa Nuraddeen yace.
"Ga wannan ka qara dasu, banida cikakken qarfi ko arziqi da na yimaka fiye da hakan, to kayi haquri dasu su kad'ai ALLAH ya horemun." Qin karb'a yayi had'e da cewa
"A'a baffa kabarsu ai su zasu bamu duk abubuwan da muke buqata idan munje, muradinsu kawai muyi karatu sosai mudawo mutaimakawa qasarmu, don haka kabarsu akula da lafiyar innar mu dasu."
Daqyar baffa suka tilastasa ykarb'i dubu d'ari suka ajiye d'ari da ishirin d'in kamar yanda ya buqata.
Shirune yabiyo bayan wasu lokuta kafin Nuraddeen yace "baffa kuroqamun sa albarkar baffa Ali koda bayan natafine a matsayinsa na mahaifi agareni, naje nayi masa magana nafad'a masa zancen tafiyata amma ko juyowa beyi ya kalleni ba."
Murmushin takaici baffa yayi zuciyarsa cike da damuwar halin da d'an uwansa ke nunawa, baffa Usman ne yace.
"Kayi haquri Nuraddeen, in sha ALLAH komai zai wuce kaji?"
"To baffa Usman ALLAH ya yarda."
Miqewa baffa Usman yayi yace zai wuce baffa ya rakkosa har qofar gida suka yiwa juna seda safe sannan yatafi.
Aranar kam zaune baffa suka kwana shida Nuraddeen suna firar bankwana cike da shauqin rabuwa da junan da zasuyi.
Tunda asubar fari Nuraddeen ya ida shirya kayansa lokacin shima baffa yagyara tsaf suka nufi can gidan saboda Nuraddeen naso yayi bankwana da mahaifiyarsa, a kan hanya suka had'u da baffa Usman yanata sauri zaije can suka sake juyawa suka nufi gidan tare, a bakin qofar d'aki suka tsaya Nuraddeen yabud'e ya shiga Yaya hawwa na kwance tana bacci bisa tabarmar data rage kad'ai a cikin d'akin don gaba d'aya Nuraddeen ya kwashe kayan dake ciki saboda gudun kada tajima kanta ya mayar dasu acan d'ayan d'akinsa nada.
A hankali ya qarasa ciki yaduqa saiti fuskarta yakai hannu zai shafa sai kuma ya fasa, wasu irin hawaye suka zubo masa a fuska yayi saurin gogege yana fad'in.
"Innar mu ALLAH yabaki lafiya, ALLAH ya yaye maki wannan lalurar albarkacin haihuwa da tarbiyar da kka bani, ALLAH yasa kaffarar kankarar zunubbanki ne wannan hlin da kike ciki, Ina maibaqincikin barin qasarnan babu addu'arki da sanyawar abarkarki atttare dani, fatan alkhairi uwata kafin nadawo agareki."
Yana gama fad'ar haka yamiqe da sauri yana hawaye yabar d'akin, kamar an tsinkili Yaya hawwa ta tashi da qarfi tanufo wajen qofar tana fad'in.
"Nura, nura, kana Ina d'ana, Ina kake nura"
Jawo qofar baffa Usman yayi da sauri ya rufe had'e da murd'a key.
"Ni zan iya kulawa da mahaifiyata koma a inane, kawai ni bana buqatar zamanta ne a hannun wud'annan mutanen."
Shiru sukayi kafin sufice waje suna tattaunawa akan inda yakamata akaita daga qarshe suka yanke shawarar ajiyeta can gida a d'akinta, ciro waya baffa Usman yayi yakira maqwabcinsu dake jigilar motar haya,
Bayan mintuna sai gashi yazo da motarsa sukaje aka d'auko Yaya hawwa tana kucce kucce, aka sata baya sannan Nuraddeen shima ya shiga ya riqeta, kallon baffa Usman baffa yayi yace yashiga gaba, shi zai biyosu abaya ya shiga suka wuce,
Godiya ya sake yiwa inspector najida sannan ya nemi Mai mashin ya hau yabi bayansu.
Ba qaramar wahala Nuraddeen yasha ba kafin su isa gida don duk ta yakusheshi, haka ma da zasu shigar da ita daqyar da sud'in goshi yasamu yashigar da ita cikin gida har d'akinta don hana kowa ya tab'ata yayi ganin yanda sai ihu da dariya yaran shiya ke yimata.
Baffa na saman mashin ya kira baba balarabe yana tambayarsa jikinsu baba balarabe, nan ya sheda masa halin da ake ciki na b'atansu, baffa yashiga tashin hankali sosai marar misaltuwa yashiga sallallami har ya iso gidan, yana isowa ya tadda baffa Usman tsaye shida baffa Ali yana surfa masa masifa akan don me za'a kawo masu mahaukaciya acikin gida tahanasu bacci ta illata masu iyali, yana ganin baffa ya d'aure fuska had'e da zunduma ashar sannan yabar wajen, baffa dake cikin alhini da damuwan b'atan iyayen Rashida kota kansa bebiba balle yadamu da abunda yayi masa yashiga yima baffa Usman bayanin abunda ke faru.
"Astagfirullah, astagfirullah, astagfirullah ALLAH ka sassauta mana wannan jarabawar dake b'ullo mana d'aya bayan d'aya." Baffa Usman yafad'a yana zabga uban tagumi, ahaka Nuraddeen ya taraddasu baffa yayi masa bayani, awannan karon damuwa tayi masa nauyin da bayada kuzarin yin kuka balle ya zubar da hawaye, gefen baffa ya zauna ya d'ora kansa saman kafad'arsa ko zai samu sassaucin yanayin da yakejin kansa aciki, tabbas ubangiji baya zalunci kuma baya goyawa mai zalunci baya domin yayi hani da hakan, haqiqa halin da mahaifiyarsa ke ciki ta cancanci zama ciki fiye da hakan saboda haqqin wud'annan bayin ALLAH da tayi sanadiyar fad'awarsu cikin wani hali suda 'yarsu,
A hankali ya d'ago kansa yana kallon baffa yace.
"Baffana shin kana fushi da inna ne har yanzu?."
"A'a Nuraddeen bana fushi da ita Amma aduk lokacin dana tuna cewa ita wani sashece acikin rayuwata kuma mahaifiyar d'ana nakanji ba dad'i."
"Kayafe mata Baffa nasan hakan zaisa tasamu sassucin halin da take ciki."
"Ko kad'an Nuraddeen bani tunanin haqina na daga cikin dalilan da ALLAH ke hukuntata domin tun aranar da ALLAH ya wanzar da tsinkewar alaqar dake tsakaninmu nayafe mata dukkanin haqqina dake kanta kuma ALLAH shine sheda akan haka."
Sake maida kansa yayi saman kafad'ar tasa sannan yace.
"Kayi haquri baffana, haqiqa dukanin mumini baya kaucewa jarabawarsa, in Sha ALLAH da sannu quncinmu zai koma farinciki."
"ALLAH ya qaddara hakan Nuraddeen."
Cike da tausayi baffa Usman ke kallonsu, haqiqa ALLAH shi yake fidda farin tuwo acikin baqar tukunya kamar yanda ya fidda Nuraddeen acikin Yaya hawwa, Wanda gaba d'aya kyawawan halayensa na mahaifinsa ne ya gado, sunjima awajen kafin akira sallar la'asar suje suyo SALLAH sannan suka kama hanyar yarimawa.
Gidan baba balarabe suka sauka suka jajanta masa akan abunda yafaru kafin sujuyo sudawo gida.
Da daddare suna zaune sunacin abinci sukaji sanarwar batun tafiyarsu Nuraddeen nan da kwana uku ana masu aqa gargad'insu dasu kasance cikin shiri, Nuraddeen na kallon yanda yanayin fuskar baffa takoma lokacin da aka fara sanarwar har aka gama yana saurare yayi ajiyar zuciya had'e da cewa Allah ya sawaqe.
Cikin kwanaki ukun da suka rage kullum Nuraddeen shike zuwa da kansa d'akin Yaya hawwa da aka kulleta ciki ya bata abincin safe rana da kuma dare, haka kuma yakanyi qoqarin gusar mata da duk wata najasa da tayi da dattin dake taruwa cikin d'akin, Bata barin qazanta ko kad'an atattare da ita koda kuwa tana dukan sane har sai yaga ya tsaftace ta.
Shi kuma baffa tuni suka gama yanke shawarar Kai Yaya hawwa asibitin mahaukata ta uduth dake jahar sokoto wanda tafiyar takama ranar dasu Nuraddeen zasu wuce, shire shire kawai baffa keyi nakai Yaya hawwa asibitin batare daya koma kula zancen maganar tafiyarsu Nuraddeen ba saboda yanda yaga yafita batun abun,
Da daddare awayi safiyar ranar baffa na zaune shida baffa Usman suna fira saiga Nuraddeen yadawo kayansa duk ajiqe sanadiyar ruwan saman da akayi suka yimasa duka, binsa da kallo sukayi har yaje yacire kayan jikinsa ya canzo wasu yazo ya zauna inda suke yana mai saqale hannuwansa waje d'aya ya d'ora akn qirji,
"A'a, Nuraddeen daga Ina kake haka ruwa sukayi maka duka?." Baffa Usman yafad'a yana kallonsa, saida ya kalli mahaifinsa dake qoqarin had'o tea a cup sannan yace.
"Daga wajen bankwana nake baffa Usman."
Miqo masa cup d'in tea daya had'a Mai zafi har yana tururi baffa yayi had'e da cewa.
"Bankwana fa kace Nuraddeen, Ina zaka jene?"
Saida ya kurb'i tea d'in yana sake motsasa da cokalin dake ciki saboda zafinsa sannan yace.
"Baffa kayi hak'uri bisa qin fahimtarka da nayi akan maganar tafiyata, a yanzu amince zanje saboda gujewa dana sanin rashin amfani da damar dake iya zowa mutum sau d'aya arayuwarsa, zanje nayi karatu, karatun da zansa kuyi alfahari dani har iya qarshen rayuwata, karka manta lokacin da kake jinya kaso ace d'aya daga cikin zuri'arku yayi karatu a fannin lafiya, to tabbas zan cika maka wannan burin da yardar ALLAH, al-amarin innar mu da Rashida kuwa, wa'ufawwidu amri ilallah, natabbata zai dafa maka wajen kula da komai, don haka shirin da nayi bazan warwaresa ba, da yardar ALLAH zantafi."
Kallo baffa Usman baffa yayi mumushi d'auke da fuskarsa yace.
"Kaji ko Usman, dama nafad'a maka bazan takura Nuraddeen ba, bazan tilasta saba amma ina da yaqinin bazai Bari wannan damar da ALLAH yabamu tawuce Saba."
"Alhamdulillah haqiqa naji dad'in sauya wannan hukuncin da kayiwa kanka da kayi, ubangiji ALLAH yayi maka albarka yasa kaje cikin sa'a, ALLAH yafaranta zuciyarka ybka kariya aduk inda kake kuma yayi maka jagora.."
Haka baffa yaci gaba da kwararo masa addu'o'i yana riqe da hannunsa baffa Usman na tayashi fuskokinsu d'auke da farinciki, murmushi Nuraddeen yayi ganin haka a fuskarsu had'e da cewa.
"Saidai baffa nakasa zuwa wajen baba balarabe inyi masa bankwana saboda rashin sanin da wace irin fuska zan kallesa in iya fad'a masa cewa zanje karatu waje a daidai lokacin da nine na zamo silar b'atan 'yarsa da kuma iyayenta.
"Karka damu Nuraddeen nasan bayada matsala zai fahimceka, Amma yanzu lokaci yaqure saboda qarfe bakwai naji ance zaku had'u a babbar ma'aikatar jahar nan don qarfe takwas jirginku zai tashi, don haka ni zani magantu dashi da yardar ALLAH kaji ko?"
"Shikenan baffa babu damu." Yafad'a tare da shanye sauran tea n ya ajiye cup d'in agefe, hannu yasa aljihu ya fiddo kud'i ya miqawa baffa.
"Ga wannan baffa, Inna Bilkisu ce da sauran mutanen gida da naje yimasu bankwana suka bani, banso karb'a ba Amma sun tilasta adole na karb'a."
"ALLAH sarki, angode ALLAH yabada ladar zumunci,"
"Amin baffa."
"Yawwa Usman ka tayamu godiya idan kaje, ALLAH yasaka da alkhairi."
"Amin Yaya Babu komai ai yiwa kaine." Baffa usman yafad'a yana murmushi.
Nan suka shiga fira tare dayi masa nasihohi kala kala akan yariqe addininsa da al'adunsu nad'an bahaushe idan yaje kafin baffa yaje ya d'auko kud'ad'en da yake ajiya saboda tafiyar. Saida yasake qidanyasu dubu d'ari biyu da ashirin don ya tab'a wasu ma sannan ya miqawa Nuraddeen yace.
"Ga wannan ka qara dasu, banida cikakken qarfi ko arziqi da na yimaka fiye da hakan, to kayi haquri dasu su kad'ai ALLAH ya horemun." Qin karb'a yayi had'e da cewa
"A'a baffa kabarsu ai su zasu bamu duk abubuwan da muke buqata idan munje, muradinsu kawai muyi karatu sosai mudawo mutaimakawa qasarmu, don haka kabarsu akula da lafiyar innar mu dasu."
Daqyar baffa suka tilastasa ykarb'i dubu d'ari suka ajiye d'ari da ishirin d'in kamar yanda ya buqata.
Shirune yabiyo bayan wasu lokuta kafin Nuraddeen yace "baffa kuroqamun sa albarkar baffa Ali koda bayan natafine a matsayinsa na mahaifi agareni, naje nayi masa magana nafad'a masa zancen tafiyata amma ko juyowa beyi ya kalleni ba."
Murmushin takaici baffa yayi zuciyarsa cike da damuwar halin da d'an uwansa ke nunawa, baffa Usman ne yace.
"Kayi haquri Nuraddeen, in sha ALLAH komai zai wuce kaji?"
"To baffa Usman ALLAH ya yarda."
Miqewa baffa Usman yayi yace zai wuce baffa ya rakkosa har qofar gida suka yiwa juna seda safe sannan yatafi.
Aranar kam zaune baffa suka kwana shida Nuraddeen suna firar bankwana cike da shauqin rabuwa da junan da zasuyi.
Tunda asubar fari Nuraddeen ya ida shirya kayansa lokacin shima baffa yagyara tsaf suka nufi can gidan saboda Nuraddeen naso yayi bankwana da mahaifiyarsa, a kan hanya suka had'u da baffa Usman yanata sauri zaije can suka sake juyawa suka nufi gidan tare, a bakin qofar d'aki suka tsaya Nuraddeen yabud'e ya shiga Yaya hawwa na kwance tana bacci bisa tabarmar data rage kad'ai a cikin d'akin don gaba d'aya Nuraddeen ya kwashe kayan dake ciki saboda gudun kada tajima kanta ya mayar dasu acan d'ayan d'akinsa nada.
A hankali ya qarasa ciki yaduqa saiti fuskarta yakai hannu zai shafa sai kuma ya fasa, wasu irin hawaye suka zubo masa a fuska yayi saurin gogege yana fad'in.
"Innar mu ALLAH yabaki lafiya, ALLAH ya yaye maki wannan lalurar albarkacin haihuwa da tarbiyar da kka bani, ALLAH yasa kaffarar kankarar zunubbanki ne wannan hlin da kike ciki, Ina maibaqincikin barin qasarnan babu addu'arki da sanyawar abarkarki atttare dani, fatan alkhairi uwata kafin nadawo agareki."
Yana gama fad'ar haka yamiqe da sauri yana hawaye yabar d'akin, kamar an tsinkili Yaya hawwa ta tashi da qarfi tanufo wajen qofar tana fad'in.
"Nura, nura, kana Ina d'ana, Ina kake nura"
Jawo qofar baffa Usman yayi da sauri ya rufe had'e da murd'a key.