Sashe 145
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin rashin kulawa little dake amsa kiran da Rashida tayi masa daidai lokacin daya tsaya shima yamiqa masa hannu sukayi musabiha tare da cewa.
"Ah ba komai maigida, ahuta lafiya saida safe" tare da tada motar yanaci gaba da amsa kiran mahaifiyarsa.
"Little badai har yanzu baku Isa gida ba bayan kasan gobe akwai tafiya mai tsawo a gabanku?"
Rashida tafad'a ranta a d'an b'ace.
"Yanzun nan can muka nufa wani bawan ALLAH ne natsaya naragewa hanya, shine ma kikaji yana yimana godiya."
"To ba laifi, adai dinga kulawa ALLAH yasa ku Isa lafiya, kudaure don ALLAH ka riqamata kuyi duk shirin daya kamata kafin safe, yanda zakuji dad'in yin sakko kaji ko?"
"To gwaggo in sha ALLAH."
Sannan ya kashe wayar daidai lokacin da take fitowa daga cikin hotel d'in.
Dr kuwa yajima tsaye yana bin motarsu da kallo aransa yanajin kamar yasan bayin ALLAHn nan, koma dai meye yaron nada kirki sosai don ya kwanta masa arai fiye da tunani, Sam bayada rawar kai irinta samarin yanzu da rashin girmamawa, ya fahimci hakanne ganin tunda ya shigo motar baiga wani abun ya had'asa da iyalinsa koda kuwa magana ce balle sayesayen kide kiden da zakaga anayi a mota ankai volume qarshe anayi ana canza batare da andamu da wud'anda ke cikin motar ba, haka yanayin yanda yake magana dashi cikin girmamawa da martabawa shiyasa yaron yaqara burgeshi sosai aransa.
Murmushi yayi sannan yasa kai yanufi cikin hotel d'in bayan yaga fitarsu don har saida motar tasu ta b'ace masa da gani sannan yabar wajen.
Akan hanyarsu tazuwa gida batool ta kalli little tace.
"Wai kasan wani abu Abu sumayya?."
"A'a gimbiyata sai kin fad'a."
Ya bata amsa had'e da juyowa yana sakar Mata murmushi,
"Wlh muryar bawan ALLAHn nan yanda kasan taka, ni da farko ma da yayi magana saida natsorata bakaga sanda najuya baya Ina son naga fuskar saba?"
Mangareta yayi ga kai had'e da cewa.
"Yawwa ai kin tuna mani, wato don kinibibi mijin wata kike qoqarin kalla, to da izinin wa kikayi hakan?, Ai tun lokacin naso mangareki albarkacinsa kikaci don kar yaga rashin kunyata shiyasa na qyaleki."
Dariya ta dingayi sosai har tana kwantar da kanta saman kujerar kafin tace.
"Oh ni batoolun Abbana!, Ashe kace abun yayi maka zafi haka, to i hak'uri ranka ya dad'e Abu sumayya abban hasssana da hussaina, gimbiyarka natuba ka yafeta bazata sake ba, Amma maganar gaskiya muryarku na yanayi sosai."
"Ko?"
Yafad'a tare da danna hancin motarsa cikin gidansu da tuni mai gadi yana ganin isowarsu taso ya wangale masu gate d'in."
Saida ya kashe motar bayan yayi parking sannan ya juyo ya kalleta had'e da cewa.
"Kinsan yanda ikon ALLAH yake, qilan qasar muce guda, hakan zata iya kasancewa amma dai ni banji hakan ba, kawai dai naji kamar na tab'a jin muryar awani wajen ne"
Ya qarasa maganar yana dariya had'e da mintsilar mata kumatu.
Dariyar itama tayi kafin tace.
"Ahaf! Ai tara na tare da goma , wani wajen yafi muryarka da kakeji kullum."
"Bawani gimbiya kindai zama mayyata kamar yanda nake mayenki shiyasa kikejin muryar kowa na shige da tawa."
Yafice yana dariya don yasan yasan ya tsokalota tunda yafad'i hakan.
Ita dai bata tankasa ba itama tasa qafa ta fito bayan ya zagayo ya bud'e mata gambun.
Kusan kwana sukayi suna shiri tare da imagining yanda tafiyar tasu zata kasance gobe zukatansu cike da farinciki.
••• ••• •••
A can qasar malesia kuwa tuni gidan labaransu na redio da talevision suka d'auki harmar labaran komawar shahararren likitannan da akafi sani da Dr N.I Aliyu qasarsa, wanda hakan baqaramin jawo hankulan manema labaran qasar yayi ba, gashi gaba d'aya bayada lambar wayar da za'a iya samunsa hannunsa balle su tuntub'esa da kanun labaran don suji dalilinsa nayin hakan bayan yafurta cewa bayada alaqa da qasar ashekarun da suka gabata, hakan kuwa ba qaramin cece kuce yajawo ba ga mutanen qasar da kuma su kansu 'yan jarida, Wanda daga qarshe har saida suka dangana da shugaban asibitin daya baro da kuma shugabar makarantar daya yayi wacce itace tazame masa tamkar uwa kuma uba aqasar, duk da dogon jawabai da bayanonan da suka samu hakan bai hanasu cigaba da yayata labaranba da kuma tofa albarkacin bakinsu ba akan hakan, aganinsu hakan da yayi tamkar butulcine yayi wa qasar tasu.
Kan kace me itama qasar tasa ta nageria sun fara qoqarin mauar masu da raddi tare da son ganin lallai sai sun gana dashi ta kowace hanya kafin isowarsa, haka wani jami'in labarai yaci gaba da bin diddigi har saida yasamu sanin ko wane jirgi ya shigo daga nan yatuntub'i jami'an jirgin suka yimasa bayanin cewa, sanadiyar hazo da gajimare da suka yima sama qawanya yasa Basu samu damar sauke pasinjojin nasu a jahar kano ba suka saukesu a jahar borno, kuma sun bashi tabbacin yana cikin jahar tunda isowar dare sukayi, idan har zai bar jahar to sai zuwa wayewar safiyar gobe idan ALLAH yakai mana rai,
Haka wannan d'an jaridar ya bawa abokanan aikinsa duk wani rahoton daya samu kafin safiyar gobe saboda shi d'an jahar adamawa ne.
Wannan daren ya zamo wani irin dare dake cike da ban al'ajabi domin kuwa a b'angaren su batool farinciki bai barsu suka runtsa idanuwa ba haka ma Rashida kwana tayi tana salloli akan ALLAH ya qaddara wannan tafiyar tasu little ta zamo alkhairi saboda yanda ta koma jin jikinta ba daidai ba, Dr Nuraddeen ma haka, d'oki da fargabar yanda zai riski iyayensa gobe basu bari ya runtsa ba, ga b'angaren' 'ya jaridu da 'yan gidan redio da talevision da sauran manema labarai suma kwana sukayi suna Shire shiren yanda zasu tarbi isowar wannan shahararren likita da labarinsa ya karad'e ko ina. Kowane b'an gare matse yake kuma qagare yake safiya tawaye don cimma cikar burin zukatansu.
••• ••• •••
A b'angaren Abba kuwa Yana gama waya da little yafad'a zaune saman katafaren gadon dake cikin d'akin tare dasa hannayensa ya dafe kai,
Kallonsa su uncle h d'aya tsayar tun d'azu sukayi had'e da tambayarsa ko lafiya.
Cikin raunin murya yace.
"Batool ce, ta dage lallai sai tazo, Kuma bana buqatar wani abun ya sameta, don haka dole nabar garin nan gobe."
"Ka natsu da kayi hakan a ranka?" Uncle Hassan yafad'a tare da zaunawa kusa dashi, jinjina masu kai kai yayi uncle Hussain dake qoqarin zama kusa dashi a d'ayan gefen yace.
"Shikenan ka kwantar da hankalinka, in Sha ALLAH gobe damu dakai duka zamu tafi, Amma Kuma kasa aranka cewa idan ALLAH yana nufin wanzuwar wani abunne akansu koda basu zoba to tabbas zai faru atawani sanadin daban saboda bawa bai isa ya kaucewa qaddararsa ba, Wanda muminin kwarai yazama dole yayi Imani da ita ya ALLAH mai kyau ko marar kyau."
Saida sukaga yad'an rage damuwa sosai sannan suka bar wajen suma suna masu addu'ar ALLAH ya kauda fitinar zamowar mafarki gaskiya.
Ita kuwa hajia mama kwana tayi tana kuka tana addu'a da Abba ya sanar da ita yanda sukayi da batool, don ta tabbata yanda take da kafiya da tsattsauran ra'ayin irin nashi ALLAH kad'aine ya isa yahana zuwan nata gobe kamar yanda tafad'a don haka ta dage wajen roqon ALLAH daya sauqa masu duk wata jarabawa da zai yimasu yanda zasu iya canyeta, haka kuma tayiwa Abba tambihi sosai akan kuskuren da yayi nafad'ar mafarki marar kyau baiyi yanda annabi yace ayiba, sosai yasake shiga damu don ta fahimtar dashi cewa alqawarin ALLAH ne duk wanda ya sab'awa umurnin manzon ALLAH yabi son zuciyarsa to tabbas zaiga ba daidaiba, wanda hakan yasa tanace da addu'a tare da qasqantar da kai ga ubangiji akan idan zai jarabcesu to yayi masu wacce imaninsu ke iya d'auka don haka sai shima Abba yayi nadamar hakan daya aikata yaci gaba da roqon yafiyar ALLAH akan sab'awa karantarwar annabi da yayi cikin rashin sani da kuma neman saussauci acikin wud'annan al-amurran.
••• ••• •••
Tun da asubar fari batool ta tashi ko nauyin cikin jikinta bataji tayi dukkanin abunda ya kamata, sannan ta tadashi suka hau shirin tafiya, koda qarfe takwas da rabi tayi suna qifar gidan Dr sun rakkosu bakin mota, a tsarin tafiyar bada su hassana zasuyi ba duk da taso hakan aranta saboda Abba yaga jikokinsa Amma saboda kawaici da kara da kuma alkunya ta kasa magana, suna shigewa cikin motar da zimmar tafiya suka ga 'yan biyun sun rugo a gyare tsaf Rashida na biye dasu da akwatinsu, karb'a Dr yayi yana dariya had'e da cewa.
"Lalle kinyi dubara kuma kin kyauta, yanzu nake zancen araina nace to ita wannan 'yar tawa wayau zatayi masu ta gudu wajen abbanta bada suba bayan suma tagudar masu da nasu abban? Sai gashi Naga kin tasosu agaba, inaga maman little wannan kora da haline kike yimasu don kema kihuta da rigimarsu kwana biyu."
Saida tad'an dara sannan tace.
"Aikuwa kamar kasani uncle, suje can wajen sabon angon nasu muma muhuta da qiriniyarsu kwana biyu."
Duk akasa dariya wajen tare da yimasu ALLAH ya kiyaye, suna qoqarin tashi Dr yaga tayarsu ta baya tayi faci yace.
"Ashsha! Kai takwara ai tayar motar tayi faci."
Fitowa yayi yad'an dudduba had'e da shafa kansa yana fad'in.
"Ahaf, sauri ya haifi nawa, to malama uwar zumud'i sai kifito, Bari naje nakirawo mai faci asa mana iska had'e da juyawa.
Har ya kusa kai bakin qofa Dr yakirasa had'e da lalaba gaban aljihun rigarsa yaciro makullin mota sabo dashi ya miqa masa yana fad'in.
"Karki tsaya b'ata wannan lokaci, jeka kaciro waccan sabiwar motar da shekaranjiya ka kai aka yimata service, Ina komai dai daidai ko ina andubata ko."
"Eh Abba, ammafa cewa kayi sai shahida zata dawo za'a lonceta."
"Manta da wannan, Kai da zakaje wajen surukinka babbar gaisuwa ta musamman da wajen dangin mahaifinka ai kai yakamata ka lunche mana ita muga yaya lafiyarta ko kuwa matana."
Dr yaqarasa maganar yana kallon 'yan biyu da sukayi cirko cirko da alama sun matsu atafi yana dariya.
"Ah ba komai maigida, ahuta lafiya saida safe" tare da tada motar yanaci gaba da amsa kiran mahaifiyarsa.
"Little badai har yanzu baku Isa gida ba bayan kasan gobe akwai tafiya mai tsawo a gabanku?"
Rashida tafad'a ranta a d'an b'ace.
"Yanzun nan can muka nufa wani bawan ALLAH ne natsaya naragewa hanya, shine ma kikaji yana yimana godiya."
"To ba laifi, adai dinga kulawa ALLAH yasa ku Isa lafiya, kudaure don ALLAH ka riqamata kuyi duk shirin daya kamata kafin safe, yanda zakuji dad'in yin sakko kaji ko?"
"To gwaggo in sha ALLAH."
Sannan ya kashe wayar daidai lokacin da take fitowa daga cikin hotel d'in.
Dr kuwa yajima tsaye yana bin motarsu da kallo aransa yanajin kamar yasan bayin ALLAHn nan, koma dai meye yaron nada kirki sosai don ya kwanta masa arai fiye da tunani, Sam bayada rawar kai irinta samarin yanzu da rashin girmamawa, ya fahimci hakanne ganin tunda ya shigo motar baiga wani abun ya had'asa da iyalinsa koda kuwa magana ce balle sayesayen kide kiden da zakaga anayi a mota ankai volume qarshe anayi ana canza batare da andamu da wud'anda ke cikin motar ba, haka yanayin yanda yake magana dashi cikin girmamawa da martabawa shiyasa yaron yaqara burgeshi sosai aransa.
Murmushi yayi sannan yasa kai yanufi cikin hotel d'in bayan yaga fitarsu don har saida motar tasu ta b'ace masa da gani sannan yabar wajen.
Akan hanyarsu tazuwa gida batool ta kalli little tace.
"Wai kasan wani abu Abu sumayya?."
"A'a gimbiyata sai kin fad'a."
Ya bata amsa had'e da juyowa yana sakar Mata murmushi,
"Wlh muryar bawan ALLAHn nan yanda kasan taka, ni da farko ma da yayi magana saida natsorata bakaga sanda najuya baya Ina son naga fuskar saba?"
Mangareta yayi ga kai had'e da cewa.
"Yawwa ai kin tuna mani, wato don kinibibi mijin wata kike qoqarin kalla, to da izinin wa kikayi hakan?, Ai tun lokacin naso mangareki albarkacinsa kikaci don kar yaga rashin kunyata shiyasa na qyaleki."
Dariya ta dingayi sosai har tana kwantar da kanta saman kujerar kafin tace.
"Oh ni batoolun Abbana!, Ashe kace abun yayi maka zafi haka, to i hak'uri ranka ya dad'e Abu sumayya abban hasssana da hussaina, gimbiyarka natuba ka yafeta bazata sake ba, Amma maganar gaskiya muryarku na yanayi sosai."
"Ko?"
Yafad'a tare da danna hancin motarsa cikin gidansu da tuni mai gadi yana ganin isowarsu taso ya wangale masu gate d'in."
Saida ya kashe motar bayan yayi parking sannan ya juyo ya kalleta had'e da cewa.
"Kinsan yanda ikon ALLAH yake, qilan qasar muce guda, hakan zata iya kasancewa amma dai ni banji hakan ba, kawai dai naji kamar na tab'a jin muryar awani wajen ne"
Ya qarasa maganar yana dariya had'e da mintsilar mata kumatu.
Dariyar itama tayi kafin tace.
"Ahaf! Ai tara na tare da goma , wani wajen yafi muryarka da kakeji kullum."
"Bawani gimbiya kindai zama mayyata kamar yanda nake mayenki shiyasa kikejin muryar kowa na shige da tawa."
Yafice yana dariya don yasan yasan ya tsokalota tunda yafad'i hakan.
Ita dai bata tankasa ba itama tasa qafa ta fito bayan ya zagayo ya bud'e mata gambun.
Kusan kwana sukayi suna shiri tare da imagining yanda tafiyar tasu zata kasance gobe zukatansu cike da farinciki.
••• ••• •••
A can qasar malesia kuwa tuni gidan labaransu na redio da talevision suka d'auki harmar labaran komawar shahararren likitannan da akafi sani da Dr N.I Aliyu qasarsa, wanda hakan baqaramin jawo hankulan manema labaran qasar yayi ba, gashi gaba d'aya bayada lambar wayar da za'a iya samunsa hannunsa balle su tuntub'esa da kanun labaran don suji dalilinsa nayin hakan bayan yafurta cewa bayada alaqa da qasar ashekarun da suka gabata, hakan kuwa ba qaramin cece kuce yajawo ba ga mutanen qasar da kuma su kansu 'yan jarida, Wanda daga qarshe har saida suka dangana da shugaban asibitin daya baro da kuma shugabar makarantar daya yayi wacce itace tazame masa tamkar uwa kuma uba aqasar, duk da dogon jawabai da bayanonan da suka samu hakan bai hanasu cigaba da yayata labaranba da kuma tofa albarkacin bakinsu ba akan hakan, aganinsu hakan da yayi tamkar butulcine yayi wa qasar tasu.
Kan kace me itama qasar tasa ta nageria sun fara qoqarin mauar masu da raddi tare da son ganin lallai sai sun gana dashi ta kowace hanya kafin isowarsa, haka wani jami'in labarai yaci gaba da bin diddigi har saida yasamu sanin ko wane jirgi ya shigo daga nan yatuntub'i jami'an jirgin suka yimasa bayanin cewa, sanadiyar hazo da gajimare da suka yima sama qawanya yasa Basu samu damar sauke pasinjojin nasu a jahar kano ba suka saukesu a jahar borno, kuma sun bashi tabbacin yana cikin jahar tunda isowar dare sukayi, idan har zai bar jahar to sai zuwa wayewar safiyar gobe idan ALLAH yakai mana rai,
Haka wannan d'an jaridar ya bawa abokanan aikinsa duk wani rahoton daya samu kafin safiyar gobe saboda shi d'an jahar adamawa ne.
Wannan daren ya zamo wani irin dare dake cike da ban al'ajabi domin kuwa a b'angaren su batool farinciki bai barsu suka runtsa idanuwa ba haka ma Rashida kwana tayi tana salloli akan ALLAH ya qaddara wannan tafiyar tasu little ta zamo alkhairi saboda yanda ta koma jin jikinta ba daidai ba, Dr Nuraddeen ma haka, d'oki da fargabar yanda zai riski iyayensa gobe basu bari ya runtsa ba, ga b'angaren' 'ya jaridu da 'yan gidan redio da talevision da sauran manema labarai suma kwana sukayi suna Shire shiren yanda zasu tarbi isowar wannan shahararren likita da labarinsa ya karad'e ko ina. Kowane b'an gare matse yake kuma qagare yake safiya tawaye don cimma cikar burin zukatansu.
••• ••• •••
A b'angaren Abba kuwa Yana gama waya da little yafad'a zaune saman katafaren gadon dake cikin d'akin tare dasa hannayensa ya dafe kai,
Kallonsa su uncle h d'aya tsayar tun d'azu sukayi had'e da tambayarsa ko lafiya.
Cikin raunin murya yace.
"Batool ce, ta dage lallai sai tazo, Kuma bana buqatar wani abun ya sameta, don haka dole nabar garin nan gobe."
"Ka natsu da kayi hakan a ranka?" Uncle Hassan yafad'a tare da zaunawa kusa dashi, jinjina masu kai kai yayi uncle Hussain dake qoqarin zama kusa dashi a d'ayan gefen yace.
"Shikenan ka kwantar da hankalinka, in Sha ALLAH gobe damu dakai duka zamu tafi, Amma Kuma kasa aranka cewa idan ALLAH yana nufin wanzuwar wani abunne akansu koda basu zoba to tabbas zai faru atawani sanadin daban saboda bawa bai isa ya kaucewa qaddararsa ba, Wanda muminin kwarai yazama dole yayi Imani da ita ya ALLAH mai kyau ko marar kyau."
Saida sukaga yad'an rage damuwa sosai sannan suka bar wajen suma suna masu addu'ar ALLAH ya kauda fitinar zamowar mafarki gaskiya.
Ita kuwa hajia mama kwana tayi tana kuka tana addu'a da Abba ya sanar da ita yanda sukayi da batool, don ta tabbata yanda take da kafiya da tsattsauran ra'ayin irin nashi ALLAH kad'aine ya isa yahana zuwan nata gobe kamar yanda tafad'a don haka ta dage wajen roqon ALLAH daya sauqa masu duk wata jarabawa da zai yimasu yanda zasu iya canyeta, haka kuma tayiwa Abba tambihi sosai akan kuskuren da yayi nafad'ar mafarki marar kyau baiyi yanda annabi yace ayiba, sosai yasake shiga damu don ta fahimtar dashi cewa alqawarin ALLAH ne duk wanda ya sab'awa umurnin manzon ALLAH yabi son zuciyarsa to tabbas zaiga ba daidaiba, wanda hakan yasa tanace da addu'a tare da qasqantar da kai ga ubangiji akan idan zai jarabcesu to yayi masu wacce imaninsu ke iya d'auka don haka sai shima Abba yayi nadamar hakan daya aikata yaci gaba da roqon yafiyar ALLAH akan sab'awa karantarwar annabi da yayi cikin rashin sani da kuma neman saussauci acikin wud'annan al-amurran.
••• ••• •••
Tun da asubar fari batool ta tashi ko nauyin cikin jikinta bataji tayi dukkanin abunda ya kamata, sannan ta tadashi suka hau shirin tafiya, koda qarfe takwas da rabi tayi suna qifar gidan Dr sun rakkosu bakin mota, a tsarin tafiyar bada su hassana zasuyi ba duk da taso hakan aranta saboda Abba yaga jikokinsa Amma saboda kawaici da kara da kuma alkunya ta kasa magana, suna shigewa cikin motar da zimmar tafiya suka ga 'yan biyun sun rugo a gyare tsaf Rashida na biye dasu da akwatinsu, karb'a Dr yayi yana dariya had'e da cewa.
"Lalle kinyi dubara kuma kin kyauta, yanzu nake zancen araina nace to ita wannan 'yar tawa wayau zatayi masu ta gudu wajen abbanta bada suba bayan suma tagudar masu da nasu abban? Sai gashi Naga kin tasosu agaba, inaga maman little wannan kora da haline kike yimasu don kema kihuta da rigimarsu kwana biyu."
Saida tad'an dara sannan tace.
"Aikuwa kamar kasani uncle, suje can wajen sabon angon nasu muma muhuta da qiriniyarsu kwana biyu."
Duk akasa dariya wajen tare da yimasu ALLAH ya kiyaye, suna qoqarin tashi Dr yaga tayarsu ta baya tayi faci yace.
"Ashsha! Kai takwara ai tayar motar tayi faci."
Fitowa yayi yad'an dudduba had'e da shafa kansa yana fad'in.
"Ahaf, sauri ya haifi nawa, to malama uwar zumud'i sai kifito, Bari naje nakirawo mai faci asa mana iska had'e da juyawa.
Har ya kusa kai bakin qofa Dr yakirasa had'e da lalaba gaban aljihun rigarsa yaciro makullin mota sabo dashi ya miqa masa yana fad'in.
"Karki tsaya b'ata wannan lokaci, jeka kaciro waccan sabiwar motar da shekaranjiya ka kai aka yimata service, Ina komai dai daidai ko ina andubata ko."
"Eh Abba, ammafa cewa kayi sai shahida zata dawo za'a lonceta."
"Manta da wannan, Kai da zakaje wajen surukinka babbar gaisuwa ta musamman da wajen dangin mahaifinka ai kai yakamata ka lunche mana ita muga yaya lafiyarta ko kuwa matana."
Dr yaqarasa maganar yana kallon 'yan biyu da sukayi cirko cirko da alama sun matsu atafi yana dariya.