Sashe 107
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hmm malan balarabe kenan!, Karabu da d'an yau kawai, ada zuciyata na kokonton cewa Nuraddeen zai iya d'aukar dogon lokaci da ransa da lafiyarsa da kuma hankalinsa ba tare damu ba, amma tunda aka d'auki tsawon wud'annan shekarun bai waiwayo muba bayan nakirasa kuma yaji muryata har ya ambaci sunana yaji irin tashin hankalin da nake ciki na rashin dawowarsa amma ya kashe wayarsa saboda baya buqatarmu ya kuma toshe duk wata hanya da zamu iya samunshi nacire wannan kokonto da kuma tabbacin da nake dashi akai, wanda yayi hakan tawace hanya kuma kake tunanin zamu iya sake samunsa balle har mu sanar dashi?,"
Kallon baffa Usman yayi da tun d'azu yazuba masa idanuwa shima yana kallo saboda mamakin kalamn dake fita daga bakinsa, yatabbata idan shine bazai tab'a yafe masu ba akan wannan abun da suka yimasa amma shi alokaci d'aya ya yafe masu har yana qoqarin b'oye laifinsu ya bayyana na d'ansa, a gaskiya qarfin imanin yayan nan nasa yayi yawa, yana wannan tunanin ne yaji yace.
"Kaga d'an uwana nan, Babu wahalar da bamuyi ba wajen ganin munsamu hanyar da zata sadamu dashi Amma hakan ta faskara, haka nakoma tamkar wani mahaukaci kullum riqe da waya a hannuna Ina qoqarin kiransa ko ALLAH zaisa in samesa amma hakan ya cutara kuma ina tsammanin shine yaqi bada damar da hakan zata yuyu saboda yasamu duniya da wasu mutanen da yake tunanin sun fimu."
"Haba Yaya kadena fad'ar hakan?, Wlh nasan ba haka kurum yaqi dawowa ba, wannan abun akwai sharrin shed'anu aciki."
"Hmm Usman kenan, sharrin shed'anu ko kuma sharrin zuciya?, ALLAH dai ya yaye masa abunda kedamunsa amma mudena azawa shed'an da shed'anu laifukanmu akoda yaushe muma kanmu muna aikatasu da kanmu da kuma saninmu sai mufake da cewa shed'anne ko kuma akasin haka, nayi imani akan cewa innamal a'amalu binniyat."
Wud'annan kalamai na baffa su suka fahimtar da baffa Usman cewa izuwa yanzu ran d'an uwan nasa yafara b'aci game da rashin dawowar d'an nasa wanda alamu sun nuna bai yarda cewa wani yayiwa Nuraddeen wani abuba daya shafi magani ko sammu, amma shi zuciyarsa d'ari bisa d'ari tayarda baya bisa hankalinsa kuma ba kowa yake zargi ba sai d'an uwansu, don haka dole yaqara tashi tsaye akan matsalar ko ALLAH zaisa adace awannan karon duk da dama ko yaushe cikin addu'a suke kuma yanada yaqinin tana karb'uwa ijaba kawai ce bata sauka ba....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___79💎
Saida little yagama zagaye kasuwar sannan yasamu daqyar yagano hanyar da zai komawa shagon nasu, lokacin har qarfe sha biyun rana tagamayi, a wahalce ya dawo tare da fad'awa akan kujerar rubar dake ciki yana fitar da nishi a hankali, kallonsa baba balarabe yayi had'e da cewa.
"Ina katsaya ne tun d'azu naketa faman jiran dawowarka kazo ka zauna ka karya najika shiru, ga abincin nan dana anso maka har ruwan tean sun huce gaba d'ai"
"Bari kawai d'an tsohona, gaba d'aya nan agajiye nake ga yunwar cikina ta isheni, gaskiya kasuwarnan da girma take, ai kad'an yarage in b'ace ALLAH ya taimaka nadawo kan hanya."
"Kace ashe ka kuru?, Ai nazata kanacan wajen malan idris d'in ne?"
"A'a, ai tund'azu nabaro wajensa ina zazzagayawa cikin kasuwar saboda na d'ebe qeyar idanuwana, Amma dattijon nan gaskiya yakamata ace yazauna gida ya huta saboda ya manyanta sosai, halama bashida manyan 'ya'ya mazane suka barshi haka yana faman shan wahalar rayuwa?."
Saurin kauda zancen baba balarabe yayi had'e da d'auko masa biredi da wainar qwai yamiqa masa yana fad'in.
"Ungo nan nidai kaci abinci kar qwalsa(ulcer) ta kamamin kai, ga ruwan tea nan saika had'a dasu haka nan ka kora"
Yafad'a yana miqo masa cup d'in.
Karb'a yayi had'e da cewa.
"Bari naci biredin kawai ya isheni."
Miqewa baba balaraben yayi tare da d'aukar sauran kayan had'in tean daya sawo ya mayarwa mai tiredar shayin yace yabashi lemu mai sanyi da ruwa a maimakonsu da yake mai tiredar na sai dasu duka saboda masu buqata idan masu sayayyar kaya sunzo masu sannan yadawo ya kawo masa ya had'a dasu yaci abinshi ya qoshi.
Baba balarabe na ganin qarfe d'aya har da mintuna tayi yaciro d'ari biyar yamiqawa little had'e da cewa ya tashi yawuce makaranta tunda yace sunada lectures, sallama sukayi dashi sannan yamiqe zai tafi yana fad'in.
"Zan dawo tanan idan mun tashi zuwa qarfe shida na marece."
"A'a kabarshi sai kuma wani jiqon saboda daqyar mukai k'arfe shidan?"
"Kashh!...gashi kuma nacewa dattijon can ya aiko akirani idan zai tafi sai nariqa masa kayan,?"
"To saidai kayi haqura har zuwa wani lokacin don suna ma riganmu tashi saboda ba'a gari d'aya bane su samu su isa gida dawuri."
"Shikenan bari naje!"
Har yayi nisa sai kuma yadawo had'e da cemasa,
"Bari dai naje nafad'a masa kada ya aiko kuma asamu bana nan, kasan bakyau karya alqawari ko kuwa?"
Ya wuce batare da yajirayi jin amsar da zata fitowa daga bakinsa ba,
Yana zuwa ya iskosa tare da wasu manyan mutane da sukazo sayen kajin har angama cinaki sun bashi kud'in yana qirgawa, sallamar da yayi tasa baffa juyowa yana kallonsa kafin yayi qoqarin qarasa qidaye kud'd'in ya sallamesu sannan yamaido hankalinsa ga little d'in daya nemi waje ya zauna.
"A'a lele kadawo?" Baffa yafad'a yana kallonsa had'e da tura kud'in cikin aljihu, Saida little yayi murmushi sannan yace
"Eh kaka, dama zanwuce makaranta me yanzu saina tuna nayi maka alqawarin cewa ka aika akirawoni idan zaku tashi zanriqa maki kaya, shine nace bara nazo na sanar dakai kada ka aika saboda tafiya zanyi, Ina fatar hakan ba damuwa ko kaka."
"Ikon ALLAH, to nikam meye abun damuwa anan, ai nasaba karaka wani damar da kanka kaji."
"A'a nidai kam bana son yanda ka manyanta haka kana d'aukar wud'annan abubuwan, don ALLAH kasamu wud'anda zasu dinga riqa maka zuwa titi ko biyansu ne sai kadinga yi?"
Shiru baffa yayi yana kallonsa irin yanda yanuna damuwa qarara a fuskarsa tabbas yasan dole akwai wani abu b'oyayye tsakaninsa da wannan yaron, haka kurum baza'a samu irin wannan tausayin ba har sai in akwai alaqa mai qarfi tsakani,
"Shikenan jikana in Sha ALLAH bazan d'auka ba, zan riqasa akaimun duka abakin titi Ina biya."
"Yawwa kaka, hakan yafi gaskiya, bari intafi lokaci na qulewa ALLAH yaqaro kasuwa."
"Amin ya rabbi."
Har zai tafi baffa yakirasa had'e da cewa,
"Yarona yau kafara ganina amma kana matuqar tausayina da kuma girmamani, ko meyasa haka?"
"Nima ban sani ba kaka, Amma nasan shi tsoho na kowane, yanada kyau ace duk inda yake angirmamasa ko badon wani dalili ba?"
"Hakane, to shikenan nagode sosai, amma zaka tafi baka fad'amun sunan kaba?"
Shiru yayi na tsawon wasu daqiqu tare dayin murmushi da alama wani abun ya tuna sannan yace
"Kaka sunana Abu sumayya."
"Abu sumayya.? Kanada aure ne?" Ya maimaita sunan cike da mamaki.
"A'a kaka, Ina dai son akirani da sunanne saboda wani dalilin amma sunana na gaskiya..."
Bai qarasa ba sakamakon wayar baffa da tayi qara yayi saurin cirota daga cikin aljihunsa had'e da d'aga masa hannu alamun ya tsaya don yasamu ya amsa kiran, kasancewar kiran daga gidane wajen iyalinsa nusaiba yasa yabar wajen zuwa can gefe inda babu hayaniya sosai ya d'aga kiran, shi kuwa little naganin haka ya shiga duba agogon hannunsa yaga lokaci na neman qurewa gashi akwai tazara sosai kafin yasamu yakoma gida har yayi zancen shiryawa ya wuce makarantar, wani saurayi dake nan gefe zaune da alama yaron baffane dake taimaka masa ya kalla tare da cemasa"
"Dan ALLAH idan kaka yadawo kace masa nawuce saboda nakusa makara."
Gyad'a masa kai saurayin yayi sannan shi kuma yawuce yana d'an d'aga qafa saboda yasamu yayi saurin isa da wuri.
Baiyi mintuna biyar da barin wajenba baffa yadawo yana tambayar saurayin ko ina yake? ya bashi amsa da cewa ai yawuce yace afad'a masa cewa sauri yakeyi yakusa makara shiyasa.
Ba haka baffa yaso ba don yaso ace yasan ainahin sunansa ko don mutuncinsa tare da kulawar daya bashi, amma duk da haka in sha ALLAH zai tambayi baba balarabe yafad'a masa tunda shi kullum suna tare a kasuwar.
Da lokacin tashinsu baffa yayi yasa masu yin dako suka d'aukar masa kwandunansa suka kaimasa bakin titi inda zai samu mota ya biyasu kamar yanda yayiwa little alqawari sannan ya d'auki kaji uku cikin sauran kajin da suka rage masa yanufi shagon baba balarabe dasu da niyar yabashi aba little amma ga mamakinsa sai ya isko shagon arufe da alama har ya rigashi tashi, Bai kawo komai aransa ba yawuce abunsa duk da aransa ba hakan yaso ba saboda dama wasu lokutan akwai lalurar da zata iya tasowa ya rigashi tashi ko shi yarigashi tashi, duk da dai su sunfi rigansu tashi saboda yanayin sana'ar tasu da kuma gari daba d'aya ba.
Baffa na isa gida bayan yawatsa ruwa yaci abinci yashiga labartawa matarsa nusaiba zancen saurayin daya gani d'an gidansu baba balarabe muryarsa da tafiyarsa sak ta Nuraddeen d'insa, kallo d'ayazakayi masa kaga banbancin farincikin daya samu yau fiye dana kullum, yaqare zancen yana fad'a mata cewa tabbas duk yanda akayi wannan yaron jininsa ne, amma zai tuntub'i balaraben yaji gaskiyar maganar don shidai jikinsa yabashi hakan.
Murmushi tayi itama fuskarta d'auke da farinciki saboda ganinsa cikin yanayin da tadad'e tana son ganinsa aciki tace.
"To kodai jita jitar da Yusuf yafad'a maku ashekarun baya gaskiyane cewa sunga yarinyarsu?"
"To banida tabbaci akan haka sai naje natuntub'esa tukuna, ada na musanta zancen na Yusuf saboda atunanina bazai yuyu ace anga yarinyarnan kuma akasa sanar damuba a matsayinmu na iyayen mijinta, koba komai muma munada haqqi musan halinda take ciki duk da mungaza wajen nemota, amma yanzu ganin yaron nan jikina yabani kamar akwai wani b'oyayyen al-amari da fushin zuciyar da nayi yasa nakasa saninsa."
"To koma dai meye ALLAH yasa hasashenmu yazamo gaskiya."
"Amin, maman Rashida, Ina suka shigane suda aminina."
Kallon baffa Usman yayi da tun d'azu yazuba masa idanuwa shima yana kallo saboda mamakin kalamn dake fita daga bakinsa, yatabbata idan shine bazai tab'a yafe masu ba akan wannan abun da suka yimasa amma shi alokaci d'aya ya yafe masu har yana qoqarin b'oye laifinsu ya bayyana na d'ansa, a gaskiya qarfin imanin yayan nan nasa yayi yawa, yana wannan tunanin ne yaji yace.
"Kaga d'an uwana nan, Babu wahalar da bamuyi ba wajen ganin munsamu hanyar da zata sadamu dashi Amma hakan ta faskara, haka nakoma tamkar wani mahaukaci kullum riqe da waya a hannuna Ina qoqarin kiransa ko ALLAH zaisa in samesa amma hakan ya cutara kuma ina tsammanin shine yaqi bada damar da hakan zata yuyu saboda yasamu duniya da wasu mutanen da yake tunanin sun fimu."
"Haba Yaya kadena fad'ar hakan?, Wlh nasan ba haka kurum yaqi dawowa ba, wannan abun akwai sharrin shed'anu aciki."
"Hmm Usman kenan, sharrin shed'anu ko kuma sharrin zuciya?, ALLAH dai ya yaye masa abunda kedamunsa amma mudena azawa shed'an da shed'anu laifukanmu akoda yaushe muma kanmu muna aikatasu da kanmu da kuma saninmu sai mufake da cewa shed'anne ko kuma akasin haka, nayi imani akan cewa innamal a'amalu binniyat."
Wud'annan kalamai na baffa su suka fahimtar da baffa Usman cewa izuwa yanzu ran d'an uwan nasa yafara b'aci game da rashin dawowar d'an nasa wanda alamu sun nuna bai yarda cewa wani yayiwa Nuraddeen wani abuba daya shafi magani ko sammu, amma shi zuciyarsa d'ari bisa d'ari tayarda baya bisa hankalinsa kuma ba kowa yake zargi ba sai d'an uwansu, don haka dole yaqara tashi tsaye akan matsalar ko ALLAH zaisa adace awannan karon duk da dama ko yaushe cikin addu'a suke kuma yanada yaqinin tana karb'uwa ijaba kawai ce bata sauka ba....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___79💎
Saida little yagama zagaye kasuwar sannan yasamu daqyar yagano hanyar da zai komawa shagon nasu, lokacin har qarfe sha biyun rana tagamayi, a wahalce ya dawo tare da fad'awa akan kujerar rubar dake ciki yana fitar da nishi a hankali, kallonsa baba balarabe yayi had'e da cewa.
"Ina katsaya ne tun d'azu naketa faman jiran dawowarka kazo ka zauna ka karya najika shiru, ga abincin nan dana anso maka har ruwan tean sun huce gaba d'ai"
"Bari kawai d'an tsohona, gaba d'aya nan agajiye nake ga yunwar cikina ta isheni, gaskiya kasuwarnan da girma take, ai kad'an yarage in b'ace ALLAH ya taimaka nadawo kan hanya."
"Kace ashe ka kuru?, Ai nazata kanacan wajen malan idris d'in ne?"
"A'a, ai tund'azu nabaro wajensa ina zazzagayawa cikin kasuwar saboda na d'ebe qeyar idanuwana, Amma dattijon nan gaskiya yakamata ace yazauna gida ya huta saboda ya manyanta sosai, halama bashida manyan 'ya'ya mazane suka barshi haka yana faman shan wahalar rayuwa?."
Saurin kauda zancen baba balarabe yayi had'e da d'auko masa biredi da wainar qwai yamiqa masa yana fad'in.
"Ungo nan nidai kaci abinci kar qwalsa(ulcer) ta kamamin kai, ga ruwan tea nan saika had'a dasu haka nan ka kora"
Yafad'a yana miqo masa cup d'in.
Karb'a yayi had'e da cewa.
"Bari naci biredin kawai ya isheni."
Miqewa baba balaraben yayi tare da d'aukar sauran kayan had'in tean daya sawo ya mayarwa mai tiredar shayin yace yabashi lemu mai sanyi da ruwa a maimakonsu da yake mai tiredar na sai dasu duka saboda masu buqata idan masu sayayyar kaya sunzo masu sannan yadawo ya kawo masa ya had'a dasu yaci abinshi ya qoshi.
Baba balarabe na ganin qarfe d'aya har da mintuna tayi yaciro d'ari biyar yamiqawa little had'e da cewa ya tashi yawuce makaranta tunda yace sunada lectures, sallama sukayi dashi sannan yamiqe zai tafi yana fad'in.
"Zan dawo tanan idan mun tashi zuwa qarfe shida na marece."
"A'a kabarshi sai kuma wani jiqon saboda daqyar mukai k'arfe shidan?"
"Kashh!...gashi kuma nacewa dattijon can ya aiko akirani idan zai tafi sai nariqa masa kayan,?"
"To saidai kayi haqura har zuwa wani lokacin don suna ma riganmu tashi saboda ba'a gari d'aya bane su samu su isa gida dawuri."
"Shikenan bari naje!"
Har yayi nisa sai kuma yadawo had'e da cemasa,
"Bari dai naje nafad'a masa kada ya aiko kuma asamu bana nan, kasan bakyau karya alqawari ko kuwa?"
Ya wuce batare da yajirayi jin amsar da zata fitowa daga bakinsa ba,
Yana zuwa ya iskosa tare da wasu manyan mutane da sukazo sayen kajin har angama cinaki sun bashi kud'in yana qirgawa, sallamar da yayi tasa baffa juyowa yana kallonsa kafin yayi qoqarin qarasa qidaye kud'd'in ya sallamesu sannan yamaido hankalinsa ga little d'in daya nemi waje ya zauna.
"A'a lele kadawo?" Baffa yafad'a yana kallonsa had'e da tura kud'in cikin aljihu, Saida little yayi murmushi sannan yace
"Eh kaka, dama zanwuce makaranta me yanzu saina tuna nayi maka alqawarin cewa ka aika akirawoni idan zaku tashi zanriqa maki kaya, shine nace bara nazo na sanar dakai kada ka aika saboda tafiya zanyi, Ina fatar hakan ba damuwa ko kaka."
"Ikon ALLAH, to nikam meye abun damuwa anan, ai nasaba karaka wani damar da kanka kaji."
"A'a nidai kam bana son yanda ka manyanta haka kana d'aukar wud'annan abubuwan, don ALLAH kasamu wud'anda zasu dinga riqa maka zuwa titi ko biyansu ne sai kadinga yi?"
Shiru baffa yayi yana kallonsa irin yanda yanuna damuwa qarara a fuskarsa tabbas yasan dole akwai wani abu b'oyayye tsakaninsa da wannan yaron, haka kurum baza'a samu irin wannan tausayin ba har sai in akwai alaqa mai qarfi tsakani,
"Shikenan jikana in Sha ALLAH bazan d'auka ba, zan riqasa akaimun duka abakin titi Ina biya."
"Yawwa kaka, hakan yafi gaskiya, bari intafi lokaci na qulewa ALLAH yaqaro kasuwa."
"Amin ya rabbi."
Har zai tafi baffa yakirasa had'e da cewa,
"Yarona yau kafara ganina amma kana matuqar tausayina da kuma girmamani, ko meyasa haka?"
"Nima ban sani ba kaka, Amma nasan shi tsoho na kowane, yanada kyau ace duk inda yake angirmamasa ko badon wani dalili ba?"
"Hakane, to shikenan nagode sosai, amma zaka tafi baka fad'amun sunan kaba?"
Shiru yayi na tsawon wasu daqiqu tare dayin murmushi da alama wani abun ya tuna sannan yace
"Kaka sunana Abu sumayya."
"Abu sumayya.? Kanada aure ne?" Ya maimaita sunan cike da mamaki.
"A'a kaka, Ina dai son akirani da sunanne saboda wani dalilin amma sunana na gaskiya..."
Bai qarasa ba sakamakon wayar baffa da tayi qara yayi saurin cirota daga cikin aljihunsa had'e da d'aga masa hannu alamun ya tsaya don yasamu ya amsa kiran, kasancewar kiran daga gidane wajen iyalinsa nusaiba yasa yabar wajen zuwa can gefe inda babu hayaniya sosai ya d'aga kiran, shi kuwa little naganin haka ya shiga duba agogon hannunsa yaga lokaci na neman qurewa gashi akwai tazara sosai kafin yasamu yakoma gida har yayi zancen shiryawa ya wuce makarantar, wani saurayi dake nan gefe zaune da alama yaron baffane dake taimaka masa ya kalla tare da cemasa"
"Dan ALLAH idan kaka yadawo kace masa nawuce saboda nakusa makara."
Gyad'a masa kai saurayin yayi sannan shi kuma yawuce yana d'an d'aga qafa saboda yasamu yayi saurin isa da wuri.
Baiyi mintuna biyar da barin wajenba baffa yadawo yana tambayar saurayin ko ina yake? ya bashi amsa da cewa ai yawuce yace afad'a masa cewa sauri yakeyi yakusa makara shiyasa.
Ba haka baffa yaso ba don yaso ace yasan ainahin sunansa ko don mutuncinsa tare da kulawar daya bashi, amma duk da haka in sha ALLAH zai tambayi baba balarabe yafad'a masa tunda shi kullum suna tare a kasuwar.
Da lokacin tashinsu baffa yayi yasa masu yin dako suka d'aukar masa kwandunansa suka kaimasa bakin titi inda zai samu mota ya biyasu kamar yanda yayiwa little alqawari sannan ya d'auki kaji uku cikin sauran kajin da suka rage masa yanufi shagon baba balarabe dasu da niyar yabashi aba little amma ga mamakinsa sai ya isko shagon arufe da alama har ya rigashi tashi, Bai kawo komai aransa ba yawuce abunsa duk da aransa ba hakan yaso ba saboda dama wasu lokutan akwai lalurar da zata iya tasowa ya rigashi tashi ko shi yarigashi tashi, duk da dai su sunfi rigansu tashi saboda yanayin sana'ar tasu da kuma gari daba d'aya ba.
Baffa na isa gida bayan yawatsa ruwa yaci abinci yashiga labartawa matarsa nusaiba zancen saurayin daya gani d'an gidansu baba balarabe muryarsa da tafiyarsa sak ta Nuraddeen d'insa, kallo d'ayazakayi masa kaga banbancin farincikin daya samu yau fiye dana kullum, yaqare zancen yana fad'a mata cewa tabbas duk yanda akayi wannan yaron jininsa ne, amma zai tuntub'i balaraben yaji gaskiyar maganar don shidai jikinsa yabashi hakan.
Murmushi tayi itama fuskarta d'auke da farinciki saboda ganinsa cikin yanayin da tadad'e tana son ganinsa aciki tace.
"To kodai jita jitar da Yusuf yafad'a maku ashekarun baya gaskiyane cewa sunga yarinyarsu?"
"To banida tabbaci akan haka sai naje natuntub'esa tukuna, ada na musanta zancen na Yusuf saboda atunanina bazai yuyu ace anga yarinyarnan kuma akasa sanar damuba a matsayinmu na iyayen mijinta, koba komai muma munada haqqi musan halinda take ciki duk da mungaza wajen nemota, amma yanzu ganin yaron nan jikina yabani kamar akwai wani b'oyayyen al-amari da fushin zuciyar da nayi yasa nakasa saninsa."
"To koma dai meye ALLAH yasa hasashenmu yazamo gaskiya."
"Amin, maman Rashida, Ina suka shigane suda aminina."