Sashe 152
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ke Hassan karkije kema asakaki kuka, bakiga wancan garin mutum mai farin gashin yasa ummanmu nildown tana kuka kuma shima wai kukan yakeyi, sai nafad'awa kaka wannan sunfimu iya muguntar ikram da take cewa munayi idan mun sakata kuka."
Bushewa da wata irin dariya shurahbil yayi har yana riqe ciki kafin daqyar ya samu ya tsaidata yace.
"Kunga, uncle bazai yimaku mugunta ba, ai kinga ni bana kuka sai dariya ko?,"
"Eh amma dariyarka tayi yawa kaima, bakyau inji kaka." Hassana tafad'a tana kallonsa, d'an d'aure fuska yayi had'e da durqusowa saiti tsawonsu y miqa masu hannu.
"To nadena kuzo muje ko?"
"Zakije hussaina?"
Ganin ta miqa masa hannu yasa itama bata tsaya wata wata ba tamiqa masa hannun yariqesu suka nufi wajen da har lokacin su uncle ake tsattsaye ana sake gaggaisawa sannan aka shiga cikin gida fuskokin kowanensu d'auke da farinciki, tana ganin mahaifiyarta hajia mama tarungumeta cike da farinciki,
Murmushi hajia mama tayi tare da d'ora hannunta agefen fuskar batool tace.
"A gaisheki d'iyar albarka sarkin kafiya, wato haka kika yimana tafiya batare da kin fad'a mana ba duk kika d'aga mana hankali ko, wannan wace irin rayuwace haka, ALLAH yasa ba haka kike bawa mijin naki da gwaggon yara ciwon kai da kafiyar nan taki."
'Dan cije baki Batool tayi tana dariya sannan yace.
"Ayi haquri hajia mama, kewarku tasa bazan iya jira ba, kuma nasan idan nafad'a kema zaki hanani kamar yanda abbana yahanani, gashi zuciyata nafad'amun kamar cikin nan bazai barni in sake had'uwa dashi ba shiyasa, ammafa munyi arziqi har sau biyu."
Nan fa tashiga Basu labarin abunda yafaru, Abba dasu uncle suka shiga jinjina al-amarin ubangi, tabbas addu'a gaskiyace kuma duk wanda yayita ALLAH na sauqaqa al-amurransa saidai kawai qaddararce baza'a guje mata ba, haka itama sadaka tana tunkud'e kowace irin fitina ce aduniya, mafarki kuwa baya tabbata gaskiya sai abunda ALLAH yaso acikinsa, kusan atare duk ahalin gidan dake waje d'aya aka shiga yiwa Allah hamdala kafin hajia mama tace.
"Wannan abun daya faru izinane ga rayuwarki data mahaifinki harma damu duka, amma alhamdulillah tunda ALLAH yakawo sauqi cikin al'amarin, duk mutumen dake tsananta addu'a arayuwarsa to haka ALLAH zai dinga sauqaqa masa al-amurransa, idan ALLAH yayi nufin silin sai fad'o maka inkana addu'a to sai kaga kana zaune qasar silin ta burbuso maka a fuska saboda addu'ar da kayi, to shi Kuma ALLAH idan ya rubutowa mutum qaddararsa to ba'a kankare masa ita, don haka sanadin addu'a sai a sauqaqa masa ita, sai kaga ta tabbata akanka amma cikin sauqi, don haka muriqe addu'a acikin kowane lamari basai munajin tsoron faruwar wata musiba akanmu ba, sai muga ALLAH na tafiyar da rayukanmu cikin sauqi, ya ALLAH ka sauqaqa mana dukkanin wani Abu daya tsananta."
Duk aka amsa da Amin, nan aka halarto da abincin kowane part kowa yaci yasha ya qoshi su hassana na laqe da shurahbil sunqi yarda da kowa saida sukaga anzage anata fira kowa yasaki jiki sannan suma suka saki nasu jikin,
Little nahutawa yayi sallama dasu ya nufi bebeji wajen su baffa yanajin wani nishad'i aransa.
••• ••• •••
Dr Nuraddeen kuwa nabarin anguwar suka nufi qauyensu, tun daga kan hanyar shiga qofar qauyen yafara ganin manya manyan sauye sauyen kala kala, haka ya dinga bin ko ina da kallo cike da mamaki, tabbas ako Ina ana samun cigaba don ko aqauyen nasu yagani ba laifi, ganin motocin 'yan jarida lokacin da suke shigowa cikin qauyen ya tabbatar masa da har yanzu suna kan dakon jiransa kenan!
Adai dai lokacin su kuma su baffa sunka fara miqewa suna qoqarin shiga cikin gida saboda yanda sukaga taron ya soma yawa, kawai sai sukaga d'aya daga cikin 'yan jaridar ya nufatosu had'e da yimasu sallama,
Suna juyo motar Dr Nuraddeen da 'yan jarida kebiye da ita tayi parking adaidai lokacin.....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)❤️
Page___104💎
Duk yanda little yaso yayi mata maganar mahaifin nasa daya dawo kuma ya sadasu awaya hakan gagara yayi don koda yasake gwada kiran wayar sai yaji ance masa kashe take, d'ago kai yayi ya kalli mahaifinsa da nan take yaji wani sauyi atattare don har hakan ta bayyana a fuskar, kenan habibty d'insa fushi take dashi sosai ya tambayi kansa, wato zuciyar ce ta amsa masa da cewa to ai ta cancanci tayi fushinma da yafi wannan domin al'amarin ne da quna sosai azuciya, murmushi little ya sakar masa tare da cewa. "Baba bara nakira maka gimbiya.!"
Saida yafad'a sannan yayi saurin toshe baki yana dariya, ya manta agaban mahaifinsa yake bai kamata yafad'i hakan ba yace cikin ransa, waskewa yayi tare da cewa.
"Aww Ina nufin batool baba."
Murmushi Dr Nuraddeen yayi had'e da cewa.
"Babu damuwa."
Yana rufe baki saiga aunty marwiyya ta iso wajen tana tafa hannuwa.
"Ikon ALLAH, yanzu Kai little shine zaka jaye mahaifinka anan ana son ganinsa, to kazo maigidanka nason ganinka mu zamu wuce."
Hakan yasa ya fasa kiran ya kad'a wayar aljihu sannan yabi bayanta, bayan ansake tab'a wata firar little yayi masu rakkiya har inda zasu hau mota suka wuce shikuma ya dawo,
Ataqaice dai ranar har kusan goma na dare suna karb'ar baqi masu zuwa yiwa Dr sannu da zuwa da masu taya baffa murnar dawowar d'ansa harma da masu zuwa tsogumi, Wanda hakan yasa little ya kasa komawa wajen batool saidai sukayi waya inda anan ya sanar da ita komai akan dawowar mahaifinsa wanda ya kasance shine mutumen daya taimakesu ayau, duk da tajima tana zargin mijin nata nada alaqa da mutumen aranta hakan bai hanata mamaki ba sosai, musamman da taji koshi waye, tayi farinciki sosai tare da jin dad'i, cikin daren ta iske mahaifinta tabashi labarin mahaifin little yadawo shima nana take yanuna farincikinsa, da kansa ya d'auki waya ya amshi lambar da tayi waya dashi yakirasa yana tayasa murna, nan little ya had'asa da mahaifinsa yayi masa barka da isowa tare da tabbatar masa da cewa gobe zasu biyo hanya suma in Sha ALLAH.
Baba nusaiba kam yau gari nasu, abinci na musamman ta shiryawa babban d'a tare da babban jika, sannan ta kwashikke kayan yaranta mata tamayar a d'akinta tasa aka sharesa tass akasa qatuwar katifar nan mai tuli irinta family ta feshesa da room freshner da sababbin labulayye yayi gwanin sha'awa, koda suka shigo gidan su uku saisu baffa da suka rakkosu acan tayi masu masauki wanda hakan ba qaramin dad'i yayiwa baffa ba ta kawo masu lafiyayyen abincin data shirya masu sukaci suka sha suka qoshi sannan su baffa Usman sukayi masu sallama don lokacin dare ya miqa har qarfe d'aya tayi, Dr Nuraddeen yaso yabi su baffa ya kwana acan wajen mahaifiyarsa amma shauqin soyayyar d'ansa tasa ya shafa'a har dare ya raba suna zaune su uku suna fira cike da soyayya, duk little ya kalli mahaifinsa sai yaji wani dad'i aransa ya rufesa marar misaltuwa, yayinda shi kuma Dr ji yake ya tsani kansa sosai idan yakalli yanda mahaifinsa yakoma, Wanda ya tabbatar wahalace da kuma damuwar rashinsa akusa dashi ta jefasa aciki, nanma kasa jurewa yayi saida yayita kuka yana roqon mahaifin nasa da d'ansa yafiya don yasamu nauyin da yakeji aransa ya ragar masa.
Har aka kira sallar asuba suna zaune suna fira Dr nabasu labarin halin daya tsinci kansa aciki awaccan qasar da irin rayuwar da yayi, sun matuqar tausaya masa sosai don kam ba rayuwace mai dad'i ko ingantacciya yayi ba daga qarshe duk suka taru suka yafi juna tare da addu'ar ALLAH yabawa kowanensu tsawon rayuwar da zasuji dad'in juna, shidai baffa murmushi kawai yayi tare da amsawa da Amin don yasan shikam ai tafiya tayi tafiya saidai fatan cikawa da Imani, Saida baffa yatada baba nusaiba sannan suka wuce masallaci bayan sunyi arwala, da aka gamo sallah Dr Nuraddeen ya kalli mahaifinsa bayan ya gaishesa sannan yace yayi can babban gida wajen mahaifiyarsa.
Baffa ya amsa masa da "To ALLAH yatsare hanya ka gaisheta."
Ba kunya ba tsoron ALLAH little yaja qafafuwa yanda kukasan zariya yabi mahaifinsa yana yiwa baffa sai yadawo.
Baffa ya amsa masa da "Adawo lafiya" yana murmushi.
Baffa nakomawa gida yanemi waje ya kwanta saboda akwai bacci sosai a idanuwansa, kan kuma kace me har yayi awon gaba dashi.
Su Dr kuwa Saida suka lelleqa d'akunan baffa Ali da baffa Usman suka gaishesu sannan suka wuce d'akin Yaya hawwa, tanaji anturo qofa tace.
"Bilki ce?, Wai Ina yaron nan nura yaje ko yamani wayau yasake tafiyarsa."
Dariya sukayi atare Dr. Nuraddeen yaje kusa da ita ya zauna tare da jawo hannunta yariqe yana d'an mammatsa mata sannan yace.
"Ina zanje kuma nabarki innarmu?, Barka da safiya, Ina kwana kin tashi lafiya?"
Saida ta zare hannunta tad'an shafa fuskarsa sannan tace.
"Lafiya klw, Ina katafi tunjiya baka dawo ba."
"Kiyi haquri innarmu, a gidan baffa na kwana kinga nan babu waje, amma yau anan zan kwana tare dake."
"A'a nura, kaje ka dawo da matarka, a wajenta yakamata ace ka kwana ba'a nan ba, Ina ance batayi wani auren ba ko?"
"Eh innarmu, Amma abune mai wahala tayarda nadawo da ita koda naje."
"Kaje zanyi maka addu'a, nasan zuciyarta mai kyauce zata biyoka kudawo tare, idan ba haka ba kuwa kada ka kuskura kadawo nan har saita amince kaji ko?."
Shiru yayi yana mamakin maganganun dake fitowa daga cikin bakin mahaifiyarsa, wai yau ita da kanta take bud'e baki tace yaje ya dawo da matarsa duk irin tarin tsanar da tayi mata ada, tabbas rayuwa na koyar da mutum darasi aduniya kuma duk abunda yasaka kuka to da SANNU SANNU wata rana zai saka dariya, yana wannan tunaninne yaji muryarta kamar zatayi kuka tace.
"Bakaji bane nura!, ko kana haufine da jin tsoron kada in aikata mata wani abunne makamancin waccan da nayi?"
Bushewa da wata irin dariya shurahbil yayi har yana riqe ciki kafin daqyar ya samu ya tsaidata yace.
"Kunga, uncle bazai yimaku mugunta ba, ai kinga ni bana kuka sai dariya ko?,"
"Eh amma dariyarka tayi yawa kaima, bakyau inji kaka." Hassana tafad'a tana kallonsa, d'an d'aure fuska yayi had'e da durqusowa saiti tsawonsu y miqa masu hannu.
"To nadena kuzo muje ko?"
"Zakije hussaina?"
Ganin ta miqa masa hannu yasa itama bata tsaya wata wata ba tamiqa masa hannun yariqesu suka nufi wajen da har lokacin su uncle ake tsattsaye ana sake gaggaisawa sannan aka shiga cikin gida fuskokin kowanensu d'auke da farinciki, tana ganin mahaifiyarta hajia mama tarungumeta cike da farinciki,
Murmushi hajia mama tayi tare da d'ora hannunta agefen fuskar batool tace.
"A gaisheki d'iyar albarka sarkin kafiya, wato haka kika yimana tafiya batare da kin fad'a mana ba duk kika d'aga mana hankali ko, wannan wace irin rayuwace haka, ALLAH yasa ba haka kike bawa mijin naki da gwaggon yara ciwon kai da kafiyar nan taki."
'Dan cije baki Batool tayi tana dariya sannan yace.
"Ayi haquri hajia mama, kewarku tasa bazan iya jira ba, kuma nasan idan nafad'a kema zaki hanani kamar yanda abbana yahanani, gashi zuciyata nafad'amun kamar cikin nan bazai barni in sake had'uwa dashi ba shiyasa, ammafa munyi arziqi har sau biyu."
Nan fa tashiga Basu labarin abunda yafaru, Abba dasu uncle suka shiga jinjina al-amarin ubangi, tabbas addu'a gaskiyace kuma duk wanda yayita ALLAH na sauqaqa al-amurransa saidai kawai qaddararce baza'a guje mata ba, haka itama sadaka tana tunkud'e kowace irin fitina ce aduniya, mafarki kuwa baya tabbata gaskiya sai abunda ALLAH yaso acikinsa, kusan atare duk ahalin gidan dake waje d'aya aka shiga yiwa Allah hamdala kafin hajia mama tace.
"Wannan abun daya faru izinane ga rayuwarki data mahaifinki harma damu duka, amma alhamdulillah tunda ALLAH yakawo sauqi cikin al'amarin, duk mutumen dake tsananta addu'a arayuwarsa to haka ALLAH zai dinga sauqaqa masa al-amurransa, idan ALLAH yayi nufin silin sai fad'o maka inkana addu'a to sai kaga kana zaune qasar silin ta burbuso maka a fuska saboda addu'ar da kayi, to shi Kuma ALLAH idan ya rubutowa mutum qaddararsa to ba'a kankare masa ita, don haka sanadin addu'a sai a sauqaqa masa ita, sai kaga ta tabbata akanka amma cikin sauqi, don haka muriqe addu'a acikin kowane lamari basai munajin tsoron faruwar wata musiba akanmu ba, sai muga ALLAH na tafiyar da rayukanmu cikin sauqi, ya ALLAH ka sauqaqa mana dukkanin wani Abu daya tsananta."
Duk aka amsa da Amin, nan aka halarto da abincin kowane part kowa yaci yasha ya qoshi su hassana na laqe da shurahbil sunqi yarda da kowa saida sukaga anzage anata fira kowa yasaki jiki sannan suma suka saki nasu jikin,
Little nahutawa yayi sallama dasu ya nufi bebeji wajen su baffa yanajin wani nishad'i aransa.
••• ••• •••
Dr Nuraddeen kuwa nabarin anguwar suka nufi qauyensu, tun daga kan hanyar shiga qofar qauyen yafara ganin manya manyan sauye sauyen kala kala, haka ya dinga bin ko ina da kallo cike da mamaki, tabbas ako Ina ana samun cigaba don ko aqauyen nasu yagani ba laifi, ganin motocin 'yan jarida lokacin da suke shigowa cikin qauyen ya tabbatar masa da har yanzu suna kan dakon jiransa kenan!
Adai dai lokacin su kuma su baffa sunka fara miqewa suna qoqarin shiga cikin gida saboda yanda sukaga taron ya soma yawa, kawai sai sukaga d'aya daga cikin 'yan jaridar ya nufatosu had'e da yimasu sallama,
Suna juyo motar Dr Nuraddeen da 'yan jarida kebiye da ita tayi parking adaidai lokacin.....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)❤️
Page___104💎
Duk yanda little yaso yayi mata maganar mahaifin nasa daya dawo kuma ya sadasu awaya hakan gagara yayi don koda yasake gwada kiran wayar sai yaji ance masa kashe take, d'ago kai yayi ya kalli mahaifinsa da nan take yaji wani sauyi atattare don har hakan ta bayyana a fuskar, kenan habibty d'insa fushi take dashi sosai ya tambayi kansa, wato zuciyar ce ta amsa masa da cewa to ai ta cancanci tayi fushinma da yafi wannan domin al'amarin ne da quna sosai azuciya, murmushi little ya sakar masa tare da cewa. "Baba bara nakira maka gimbiya.!"
Saida yafad'a sannan yayi saurin toshe baki yana dariya, ya manta agaban mahaifinsa yake bai kamata yafad'i hakan ba yace cikin ransa, waskewa yayi tare da cewa.
"Aww Ina nufin batool baba."
Murmushi Dr Nuraddeen yayi had'e da cewa.
"Babu damuwa."
Yana rufe baki saiga aunty marwiyya ta iso wajen tana tafa hannuwa.
"Ikon ALLAH, yanzu Kai little shine zaka jaye mahaifinka anan ana son ganinsa, to kazo maigidanka nason ganinka mu zamu wuce."
Hakan yasa ya fasa kiran ya kad'a wayar aljihu sannan yabi bayanta, bayan ansake tab'a wata firar little yayi masu rakkiya har inda zasu hau mota suka wuce shikuma ya dawo,
Ataqaice dai ranar har kusan goma na dare suna karb'ar baqi masu zuwa yiwa Dr sannu da zuwa da masu taya baffa murnar dawowar d'ansa harma da masu zuwa tsogumi, Wanda hakan yasa little ya kasa komawa wajen batool saidai sukayi waya inda anan ya sanar da ita komai akan dawowar mahaifinsa wanda ya kasance shine mutumen daya taimakesu ayau, duk da tajima tana zargin mijin nata nada alaqa da mutumen aranta hakan bai hanata mamaki ba sosai, musamman da taji koshi waye, tayi farinciki sosai tare da jin dad'i, cikin daren ta iske mahaifinta tabashi labarin mahaifin little yadawo shima nana take yanuna farincikinsa, da kansa ya d'auki waya ya amshi lambar da tayi waya dashi yakirasa yana tayasa murna, nan little ya had'asa da mahaifinsa yayi masa barka da isowa tare da tabbatar masa da cewa gobe zasu biyo hanya suma in Sha ALLAH.
Baba nusaiba kam yau gari nasu, abinci na musamman ta shiryawa babban d'a tare da babban jika, sannan ta kwashikke kayan yaranta mata tamayar a d'akinta tasa aka sharesa tass akasa qatuwar katifar nan mai tuli irinta family ta feshesa da room freshner da sababbin labulayye yayi gwanin sha'awa, koda suka shigo gidan su uku saisu baffa da suka rakkosu acan tayi masu masauki wanda hakan ba qaramin dad'i yayiwa baffa ba ta kawo masu lafiyayyen abincin data shirya masu sukaci suka sha suka qoshi sannan su baffa Usman sukayi masu sallama don lokacin dare ya miqa har qarfe d'aya tayi, Dr Nuraddeen yaso yabi su baffa ya kwana acan wajen mahaifiyarsa amma shauqin soyayyar d'ansa tasa ya shafa'a har dare ya raba suna zaune su uku suna fira cike da soyayya, duk little ya kalli mahaifinsa sai yaji wani dad'i aransa ya rufesa marar misaltuwa, yayinda shi kuma Dr ji yake ya tsani kansa sosai idan yakalli yanda mahaifinsa yakoma, Wanda ya tabbatar wahalace da kuma damuwar rashinsa akusa dashi ta jefasa aciki, nanma kasa jurewa yayi saida yayita kuka yana roqon mahaifin nasa da d'ansa yafiya don yasamu nauyin da yakeji aransa ya ragar masa.
Har aka kira sallar asuba suna zaune suna fira Dr nabasu labarin halin daya tsinci kansa aciki awaccan qasar da irin rayuwar da yayi, sun matuqar tausaya masa sosai don kam ba rayuwace mai dad'i ko ingantacciya yayi ba daga qarshe duk suka taru suka yafi juna tare da addu'ar ALLAH yabawa kowanensu tsawon rayuwar da zasuji dad'in juna, shidai baffa murmushi kawai yayi tare da amsawa da Amin don yasan shikam ai tafiya tayi tafiya saidai fatan cikawa da Imani, Saida baffa yatada baba nusaiba sannan suka wuce masallaci bayan sunyi arwala, da aka gamo sallah Dr Nuraddeen ya kalli mahaifinsa bayan ya gaishesa sannan yace yayi can babban gida wajen mahaifiyarsa.
Baffa ya amsa masa da "To ALLAH yatsare hanya ka gaisheta."
Ba kunya ba tsoron ALLAH little yaja qafafuwa yanda kukasan zariya yabi mahaifinsa yana yiwa baffa sai yadawo.
Baffa ya amsa masa da "Adawo lafiya" yana murmushi.
Baffa nakomawa gida yanemi waje ya kwanta saboda akwai bacci sosai a idanuwansa, kan kuma kace me har yayi awon gaba dashi.
Su Dr kuwa Saida suka lelleqa d'akunan baffa Ali da baffa Usman suka gaishesu sannan suka wuce d'akin Yaya hawwa, tanaji anturo qofa tace.
"Bilki ce?, Wai Ina yaron nan nura yaje ko yamani wayau yasake tafiyarsa."
Dariya sukayi atare Dr. Nuraddeen yaje kusa da ita ya zauna tare da jawo hannunta yariqe yana d'an mammatsa mata sannan yace.
"Ina zanje kuma nabarki innarmu?, Barka da safiya, Ina kwana kin tashi lafiya?"
Saida ta zare hannunta tad'an shafa fuskarsa sannan tace.
"Lafiya klw, Ina katafi tunjiya baka dawo ba."
"Kiyi haquri innarmu, a gidan baffa na kwana kinga nan babu waje, amma yau anan zan kwana tare dake."
"A'a nura, kaje ka dawo da matarka, a wajenta yakamata ace ka kwana ba'a nan ba, Ina ance batayi wani auren ba ko?"
"Eh innarmu, Amma abune mai wahala tayarda nadawo da ita koda naje."
"Kaje zanyi maka addu'a, nasan zuciyarta mai kyauce zata biyoka kudawo tare, idan ba haka ba kuwa kada ka kuskura kadawo nan har saita amince kaji ko?."
Shiru yayi yana mamakin maganganun dake fitowa daga cikin bakin mahaifiyarsa, wai yau ita da kanta take bud'e baki tace yaje ya dawo da matarsa duk irin tarin tsanar da tayi mata ada, tabbas rayuwa na koyar da mutum darasi aduniya kuma duk abunda yasaka kuka to da SANNU SANNU wata rana zai saka dariya, yana wannan tunaninne yaji muryarta kamar zatayi kuka tace.
"Bakaji bane nura!, ko kana haufine da jin tsoron kada in aikata mata wani abunne makamancin waccan da nayi?"