Sashe 38
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bin bayanta da kallo baffa yayi kafin yayi ajiyar zuciya yace. "Alhamdulillahillazi bini'imatihi tatimmusswalihat, haqiqi Nuraddeen Ina tayaka murna da kuma alfaharin zab'in da kayowa 'ya'yanka, banida shakku akan cewa ALLAH yagama mallaka maka rabin addininka yanzu yarage wajenka kanemi rabin don samun kyakkyawar makoma, Ina roqon ALLAH nima daya dubi zuciyata ya shirya mani mahifiyarka, bansan meyake damunta ba da har zata d'auki karan tsana ta azawa wannan nagartacciyar yarinya wacce samunta tamkar samun zinarine acikin qasa, narasa wane irin zunubi na aikata da har iyalina ta kasance ahaka, ubangiji ALLAH kaganar da ita tun aduniya basai ranar da nadama baza tayi amfani ba." Nisawa nuraddin yayi yana d'an muskutawa sannan yace, "Amin baffa."
Sun d'an jima kad'an suna fira kafin yayi masa saida safe snadiyar baffa Usman daya shigo d'akin riqe da 'yar ledarsa wacce tazamo masa jiki duk daren ALLAH sai ya riqowa baffa ita, wani lokaci gasashshen nama ne aciki, wani lokaci kuma kifi ko kuma sharare (had'in dankali da kifi).
'Dakin Yaya hawwa yashiga itama ya gaisheta sannan ya d'auko mata zancen abunda yafaru d'azu, duk da cikin girmamawa da kuma tausasa harshe yake yimata maganar hakan bai hanata yimasa tas ba sannan ta jadda masa cewa bazata dena abunda take so ba tunda gidansa ne kuma ita ta haifesa duk yanda taga dama haka zatayi, daga qarshema korarsa tayi tace yaje yabata waje bacci take ji, haquri yabata sannan ya tashi yawuce sashensa, ruwa yafara watsowa sannan sukaci abinci bayan sun gama itama tashiga toilet ta watso ruwan had'e da yin shirinta na kwanciya tahaye gadonta, duk abunda takeyi yana zaune gefen gadon yana kallonta da gefen idanuwa saida ta kwanta ya mulmula tare dasa hannu ya jawota yana fad'in. "To ranki ya dad'e ai baki isa ba, kin manta karatu zamuyi ne?".
Jan abun rufarsu tayi had'e da rufe fuskarta "habiby kabarni bacci nakeji don ALLAH."
"Tab..ina yimasa Amma kinsan ALLAH bazaki kwantaba, kawai kitashi, Yanzu muna qarfe tara awa d'aya da rabi kacal zamuyi seki koma ki kwanta abunki kinji ko, daure kitashi mana habibtyn habibyyy." yafad'a yana d'agota daga kan filo, wartsake idanuwanta tayi don tasan tunda yafad'a to dole haka za'ayi tajuyo tana d'an harararsa. "Naji dai ko mai zaki mun bakomai." Yafad'a yana ciro littafi da biro a gefen bedside loka, murmushi tayi ta aza kanta saman kafad'arsa yace. "Karki damu, zan baki abunda kike so." Hakan daya fad'a yasa ta zauna daidai, cikin qwarewa yafar koya mata qananan kalmomin turanci da kuma hausa irinsu (I, you, she, we, he, they, them, us, e.t.c) (ni, ku, ita, shi, su, mu da sauransu.)
Gwargwado kuma ta maida hankali tana fahimta sai dai bini bini tanayi tana duba agogo, awa d'aya na bugawa tayi baya da jikinta zata kwanta ya tarota yana dariya. "A'a habibty kiji tsoron ALLAH saura rabin awafa."
"Bacci nakeji habiby."
"Kiyi haquri, rabin awar tawace addu'o'i zaki koya mun, kinga sai kema kizama malamata."
"Habiby mubarshi sai gobe." Rashida tasake fad'a tana zamewa daga riqon daya yimata tayi kwancenta, a 'yan kwanakin nan yarasa meyake damunta take yawan bacci, gyara mata kwanciyarta yayi sannan ya miqe yaje yayo arwalar bacci ya kashe masu wuta shima ya kwanta, addu'ar bacci yayi masu ya shafe mata jikinta sannn ya jawota ajikinsa ya rungumeta sosai sukaci gaba da baccinsu hankali kwance.
Misalain qarfe shabiyu biyu da rabi na dare Rashida n bacci taji wata irin qara da kururuwa na fitowa daga cikin falonta, addu'o'in data sani tafara karantowa abakinta sannan ta sauko kan gadon, fitilar d'akin ta kunna had'e da kallon yanda Nuraddeen ya qaqume abun rufarsu yana baccinsa hankli kwance, toilet tawuce tayo fitsari had'e da d'auro arwala akai tanufo falon, wani irin qugi taji yna tashi cikin dakewa takoma ta d'auko wayar Nuraddeen ta kunna karatun k'ur'ani tanufo falon dashi, tana shiga taga wata irin qatuwar mage tayo kanta tadake tana kiran sunan ALLAH tare da runtse idanuwanta, tsaye tayi tana jiran taji mezai faru da ita amma sai taji wani iska maiqarfi kamar guguwa yayi wani qugi daidai saiti kunnenta sannan yayi shuuu...yawuce ta gefen labulen tagarta.
Sautin karatun ta sake qarawa sannan ta shimfid'a abun sallah ta kabbarta sallarta cike da yaqini da kuma miqa dukkanin al'amurranta ga ALLAH, hankali kwance take gudanar da sallolin nata na nafila kamar yanda tasaba duk daren ALLAH matuqar tanada tsarki har aka kusa kiran sallar asuba, daidai lokacin Nuraddeen ya farko tare da laluba gefen da take kwance yaji ba kowa, d'an shafa goshinsa yayi cikin yanayin bacci tare da jaye mayafin da suka lullub'a ya sauko akan gadon, falon yanufo ya tarar da ita zaune ta d'aga hannayenta tana addu'o'inta kamar yanda tasaba, murmushi yayi tare da komawa toilet ya d'auro arwala shima yayi raka'o'insa biyu na raka'atanil fijir sannan ya zauna yana jiran atada sallar asuba.
Tana gama sallar asuba tayi zaunenta tana karanto azkar d'inta na safiya da marece har rana tafito sannan tawuce kitchen tad'ora dahuwar indomie kafin ta d'ora abun kari saboda yunwar da takeji shi kuma ya riqa mata gyare-gyaren uwar d'akin dana falo yana gamawa ya iskota kitchen zaune da plate gabanta tana cin indomien data gama dafawa. Cike da mamaki yake kallonta kafin yace. "Habibty lafiyarki kuwa? Qarfe shida da rabi na safe yanzu, sekace wacce takwana da yunwa..."
Bai qarasa rufe baki ba ta tashi aguje tayo waje wajen makwarara tana sheqa amai, da sauri yayo kanta ya riqeta, gaba d'aya indomien da taci saida ta amayeta abun gwanin tausayi, kujerar tsugunno ya d'auko mata a kitchen ya zaunar da ita sannan yaje ya d'ebo ruwa ya wanke mata bakinta da inda ya b'ata mata hijabin dake sanye ajikinta, d'aki ya kaita ya zaunar saman kujera had'e da cire mata hijabin sannan yadawo tsakar gidan ya wanke bakin makwararar da tayi aman ya sake d'ebo wasu ruwan ya wanke hijabin ya shanya sannan yakoma cikin falon yana jero mata sannu, kuka ta saka masa kai kace wata qaramar yarinyace sosai. "Habibty meye haka, laifinki ne fa, kinsan bama Kari dawuri don me zakici abinci yanzu beside kofa brush bakiyi ba ba dole k'wayun cutukan da suka zauna maki a baki su sakaki amai ba."
Nuraddeen yafad'a yana qoqarin jawota ajiki, k'wacewa tayi tana fad'in. "Ko ba yunwa nakeji ba, kuma cikina duk a toshe yake bana jin dad'insa."
"Ayya yi haquri habibty, amma anya wannan ci da kikeyi a kwanakinnan ba macijin cikine ke damunki ba, ga yawan bacci dana lura kinayi gaskiya yau zanyiwa baffa Usman magana idan yaje daji yasamo maki maganin macijin ciki da basir."
"Wlh kuwa habiby nima nafara jin tsoro kada yafara cimun hanji kaga yanzu banci komaiba."
Rashida tafad'a tana yamutsa fuska, daidai lokacin taji ana yimata motsi aciki, wuntsil wuntsil, da sauri tamiqe tsaye tana zaro idanuwa tare da dafe saiti inda taji motsin kamar zatayi kuka yace. "Habiby wallahi macijinnan da gaskene, kaji yafaramun motsi, wayyo ummata, wayyo zan cinyemun hanji." Da gudu takoma kitchen d'in ta d'auki sauran indomien ta qarasa cinyewa shi kuma yana tsaye yana kallon ikon ALLAH, duk Wanda yasan ciki kallo d'aya zaiyiwa Rashida ya fahimci tanada shi saboda hasken da tayi ga breast d'inta suma duk sun cicciko duk da bai sata laulayi ba yakan sata jin matsananciyar yunwa da Kuma yawan bacci wud'an gaba d'aya Nuraddeen ya ta'allaqasu da cewa yawan bacci basirne ke damunta shi kuma yawan cin abinci macijin ciki ne da ita sabod ko kad'an ransa bai kawo masa zancen cikine da ita ba, be side bema San yanda ake gane cikin mace ba idan tanada shi, ko amai da yaga tayi a tunaninsa rashin brush ne da batayi ba kafin taci abincin....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___30💎
Cike da so da qauna ya amsa mata yana tambayarta ya qarfin jikin nata, a kunyace ta amsa da taji sauqi sosai, nan yayi ta saka mata albarka bisa zuwan da baffa Usman yayi wajensu amadadin baffa suna godiya bisa tarbiyar da suka bata tare da yabon kyawawan halayenta bisa haquri da juriya da take dasu da yanda take girmama kowa acikin gidan, hakan ba qaramin jin dad'i da alfahari ta sakasu ba shi da umma bugu da qari ga albishir da suka samu cewa sun kusa samun jika nan kusa bada jimawa ba, wannan dalilinne yasa yakirata da wannan safiyar don yanuna mata tsantsar farincikin data sakashi don har seda yayi qwalla.
"Rashida Ina matuqar alfaharin kasantuwarki 'yata saboda kin janyo mani girma da kimata sun qaru a idanun duniya kin sakani farincikin da ko mai 'ya'yaye goma bai isa yanuna mun shiba, kin fahimtar Dani cewa ba ilimin boko kad'aine kesa kayi alfahari da d'anka ba matuqar kabashi tarbiya da ilimin addini, Ina mai addu'a ALLAH yakareki Kuma yafaranta zuciyarki kamar yanda kika faranta tamu nida mahaifiyarki, ki kula da kanki sosai kinga yanzu bake kad'ai kike ba, ki dage da yiwa abunda ke cikinki addu'a da neman tsari daga sharrin shed'an tun kafin yazo duniya domin shine hikimar ALLAH da yabar uwa tayi renon cikinta har na tsawon wata tara don samu isashhen lokacin yimasa addu'a badon haka ba da yanda akayiwa nana maryam kun fayakum haka za'a yiwa kowace mace saboda haka ki kula sosai kinji iko, kiqara hak'uri Kuma ki kai kukanki ga ALLAH da SANNU SANNU zai yaye mana damuwarmu, ALLAH yayi maki albarka, ga umman taki."
Baba yafad'a yana miqawa ummu wayar,
"Ummata." Rashida tafad'a hawaye na biyo kuncinta saboda tausayin kanta da halin da take ciki da basu sani ba, goge hawayenta tayi wani b'angare na zuciyarta nafad'a mata cewa bai kamata tayiwa ALLAH butulci ba tunda iyayenta nacikin farinciki Kuma ako yaushe addu'arsu natare da ita.
Muryar umma ta tsinkayo a kunnuwanta tana fad'in, "yarinyata ya kike?"
Sun d'an jima kad'an suna fira kafin yayi masa saida safe snadiyar baffa Usman daya shigo d'akin riqe da 'yar ledarsa wacce tazamo masa jiki duk daren ALLAH sai ya riqowa baffa ita, wani lokaci gasashshen nama ne aciki, wani lokaci kuma kifi ko kuma sharare (had'in dankali da kifi).
'Dakin Yaya hawwa yashiga itama ya gaisheta sannan ya d'auko mata zancen abunda yafaru d'azu, duk da cikin girmamawa da kuma tausasa harshe yake yimata maganar hakan bai hanata yimasa tas ba sannan ta jadda masa cewa bazata dena abunda take so ba tunda gidansa ne kuma ita ta haifesa duk yanda taga dama haka zatayi, daga qarshema korarsa tayi tace yaje yabata waje bacci take ji, haquri yabata sannan ya tashi yawuce sashensa, ruwa yafara watsowa sannan sukaci abinci bayan sun gama itama tashiga toilet ta watso ruwan had'e da yin shirinta na kwanciya tahaye gadonta, duk abunda takeyi yana zaune gefen gadon yana kallonta da gefen idanuwa saida ta kwanta ya mulmula tare dasa hannu ya jawota yana fad'in. "To ranki ya dad'e ai baki isa ba, kin manta karatu zamuyi ne?".
Jan abun rufarsu tayi had'e da rufe fuskarta "habiby kabarni bacci nakeji don ALLAH."
"Tab..ina yimasa Amma kinsan ALLAH bazaki kwantaba, kawai kitashi, Yanzu muna qarfe tara awa d'aya da rabi kacal zamuyi seki koma ki kwanta abunki kinji ko, daure kitashi mana habibtyn habibyyy." yafad'a yana d'agota daga kan filo, wartsake idanuwanta tayi don tasan tunda yafad'a to dole haka za'ayi tajuyo tana d'an harararsa. "Naji dai ko mai zaki mun bakomai." Yafad'a yana ciro littafi da biro a gefen bedside loka, murmushi tayi ta aza kanta saman kafad'arsa yace. "Karki damu, zan baki abunda kike so." Hakan daya fad'a yasa ta zauna daidai, cikin qwarewa yafar koya mata qananan kalmomin turanci da kuma hausa irinsu (I, you, she, we, he, they, them, us, e.t.c) (ni, ku, ita, shi, su, mu da sauransu.)
Gwargwado kuma ta maida hankali tana fahimta sai dai bini bini tanayi tana duba agogo, awa d'aya na bugawa tayi baya da jikinta zata kwanta ya tarota yana dariya. "A'a habibty kiji tsoron ALLAH saura rabin awafa."
"Bacci nakeji habiby."
"Kiyi haquri, rabin awar tawace addu'o'i zaki koya mun, kinga sai kema kizama malamata."
"Habiby mubarshi sai gobe." Rashida tasake fad'a tana zamewa daga riqon daya yimata tayi kwancenta, a 'yan kwanakin nan yarasa meyake damunta take yawan bacci, gyara mata kwanciyarta yayi sannan ya miqe yaje yayo arwalar bacci ya kashe masu wuta shima ya kwanta, addu'ar bacci yayi masu ya shafe mata jikinta sannn ya jawota ajikinsa ya rungumeta sosai sukaci gaba da baccinsu hankali kwance.
Misalain qarfe shabiyu biyu da rabi na dare Rashida n bacci taji wata irin qara da kururuwa na fitowa daga cikin falonta, addu'o'in data sani tafara karantowa abakinta sannan ta sauko kan gadon, fitilar d'akin ta kunna had'e da kallon yanda Nuraddeen ya qaqume abun rufarsu yana baccinsa hankli kwance, toilet tawuce tayo fitsari had'e da d'auro arwala akai tanufo falon, wani irin qugi taji yna tashi cikin dakewa takoma ta d'auko wayar Nuraddeen ta kunna karatun k'ur'ani tanufo falon dashi, tana shiga taga wata irin qatuwar mage tayo kanta tadake tana kiran sunan ALLAH tare da runtse idanuwanta, tsaye tayi tana jiran taji mezai faru da ita amma sai taji wani iska maiqarfi kamar guguwa yayi wani qugi daidai saiti kunnenta sannan yayi shuuu...yawuce ta gefen labulen tagarta.
Sautin karatun ta sake qarawa sannan ta shimfid'a abun sallah ta kabbarta sallarta cike da yaqini da kuma miqa dukkanin al'amurranta ga ALLAH, hankali kwance take gudanar da sallolin nata na nafila kamar yanda tasaba duk daren ALLAH matuqar tanada tsarki har aka kusa kiran sallar asuba, daidai lokacin Nuraddeen ya farko tare da laluba gefen da take kwance yaji ba kowa, d'an shafa goshinsa yayi cikin yanayin bacci tare da jaye mayafin da suka lullub'a ya sauko akan gadon, falon yanufo ya tarar da ita zaune ta d'aga hannayenta tana addu'o'inta kamar yanda tasaba, murmushi yayi tare da komawa toilet ya d'auro arwala shima yayi raka'o'insa biyu na raka'atanil fijir sannan ya zauna yana jiran atada sallar asuba.
Tana gama sallar asuba tayi zaunenta tana karanto azkar d'inta na safiya da marece har rana tafito sannan tawuce kitchen tad'ora dahuwar indomie kafin ta d'ora abun kari saboda yunwar da takeji shi kuma ya riqa mata gyare-gyaren uwar d'akin dana falo yana gamawa ya iskota kitchen zaune da plate gabanta tana cin indomien data gama dafawa. Cike da mamaki yake kallonta kafin yace. "Habibty lafiyarki kuwa? Qarfe shida da rabi na safe yanzu, sekace wacce takwana da yunwa..."
Bai qarasa rufe baki ba ta tashi aguje tayo waje wajen makwarara tana sheqa amai, da sauri yayo kanta ya riqeta, gaba d'aya indomien da taci saida ta amayeta abun gwanin tausayi, kujerar tsugunno ya d'auko mata a kitchen ya zaunar da ita sannan yaje ya d'ebo ruwa ya wanke mata bakinta da inda ya b'ata mata hijabin dake sanye ajikinta, d'aki ya kaita ya zaunar saman kujera had'e da cire mata hijabin sannan yadawo tsakar gidan ya wanke bakin makwararar da tayi aman ya sake d'ebo wasu ruwan ya wanke hijabin ya shanya sannan yakoma cikin falon yana jero mata sannu, kuka ta saka masa kai kace wata qaramar yarinyace sosai. "Habibty meye haka, laifinki ne fa, kinsan bama Kari dawuri don me zakici abinci yanzu beside kofa brush bakiyi ba ba dole k'wayun cutukan da suka zauna maki a baki su sakaki amai ba."
Nuraddeen yafad'a yana qoqarin jawota ajiki, k'wacewa tayi tana fad'in. "Ko ba yunwa nakeji ba, kuma cikina duk a toshe yake bana jin dad'insa."
"Ayya yi haquri habibty, amma anya wannan ci da kikeyi a kwanakinnan ba macijin cikine ke damunki ba, ga yawan bacci dana lura kinayi gaskiya yau zanyiwa baffa Usman magana idan yaje daji yasamo maki maganin macijin ciki da basir."
"Wlh kuwa habiby nima nafara jin tsoro kada yafara cimun hanji kaga yanzu banci komaiba."
Rashida tafad'a tana yamutsa fuska, daidai lokacin taji ana yimata motsi aciki, wuntsil wuntsil, da sauri tamiqe tsaye tana zaro idanuwa tare da dafe saiti inda taji motsin kamar zatayi kuka yace. "Habiby wallahi macijinnan da gaskene, kaji yafaramun motsi, wayyo ummata, wayyo zan cinyemun hanji." Da gudu takoma kitchen d'in ta d'auki sauran indomien ta qarasa cinyewa shi kuma yana tsaye yana kallon ikon ALLAH, duk Wanda yasan ciki kallo d'aya zaiyiwa Rashida ya fahimci tanada shi saboda hasken da tayi ga breast d'inta suma duk sun cicciko duk da bai sata laulayi ba yakan sata jin matsananciyar yunwa da Kuma yawan bacci wud'an gaba d'aya Nuraddeen ya ta'allaqasu da cewa yawan bacci basirne ke damunta shi kuma yawan cin abinci macijin ciki ne da ita sabod ko kad'an ransa bai kawo masa zancen cikine da ita ba, be side bema San yanda ake gane cikin mace ba idan tanada shi, ko amai da yaga tayi a tunaninsa rashin brush ne da batayi ba kafin taci abincin....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___30💎
Cike da so da qauna ya amsa mata yana tambayarta ya qarfin jikin nata, a kunyace ta amsa da taji sauqi sosai, nan yayi ta saka mata albarka bisa zuwan da baffa Usman yayi wajensu amadadin baffa suna godiya bisa tarbiyar da suka bata tare da yabon kyawawan halayenta bisa haquri da juriya da take dasu da yanda take girmama kowa acikin gidan, hakan ba qaramin jin dad'i da alfahari ta sakasu ba shi da umma bugu da qari ga albishir da suka samu cewa sun kusa samun jika nan kusa bada jimawa ba, wannan dalilinne yasa yakirata da wannan safiyar don yanuna mata tsantsar farincikin data sakashi don har seda yayi qwalla.
"Rashida Ina matuqar alfaharin kasantuwarki 'yata saboda kin janyo mani girma da kimata sun qaru a idanun duniya kin sakani farincikin da ko mai 'ya'yaye goma bai isa yanuna mun shiba, kin fahimtar Dani cewa ba ilimin boko kad'aine kesa kayi alfahari da d'anka ba matuqar kabashi tarbiya da ilimin addini, Ina mai addu'a ALLAH yakareki Kuma yafaranta zuciyarki kamar yanda kika faranta tamu nida mahaifiyarki, ki kula da kanki sosai kinga yanzu bake kad'ai kike ba, ki dage da yiwa abunda ke cikinki addu'a da neman tsari daga sharrin shed'an tun kafin yazo duniya domin shine hikimar ALLAH da yabar uwa tayi renon cikinta har na tsawon wata tara don samu isashhen lokacin yimasa addu'a badon haka ba da yanda akayiwa nana maryam kun fayakum haka za'a yiwa kowace mace saboda haka ki kula sosai kinji iko, kiqara hak'uri Kuma ki kai kukanki ga ALLAH da SANNU SANNU zai yaye mana damuwarmu, ALLAH yayi maki albarka, ga umman taki."
Baba yafad'a yana miqawa ummu wayar,
"Ummata." Rashida tafad'a hawaye na biyo kuncinta saboda tausayin kanta da halin da take ciki da basu sani ba, goge hawayenta tayi wani b'angare na zuciyarta nafad'a mata cewa bai kamata tayiwa ALLAH butulci ba tunda iyayenta nacikin farinciki Kuma ako yaushe addu'arsu natare da ita.
Muryar umma ta tsinkayo a kunnuwanta tana fad'in, "yarinyata ya kike?"