← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 160

Sashe 60

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Zan nema Maya tafiyarsu baffa, ALLAH kayafe Maya Kuma ya shiryar da ita damu baki d'aya, jarabawar innar mu ce tazo mata ahaka wacce dukkaninku bamu wuce tab'a awurin ALLAH, fatanmu d'aya ALLAH karya jarabcemu ta irin hanyar da aka jarabtata," ajiyar zuciya baffa yayi yana kallon Nuraddeen, tabbas gaba d'aya halayensa na sanyin hali ya d'ebo amma anan harya zartasa tunda take kallon son zuciyar mahaifiyarsa a matsayin kuskure da jarabawar rayuwa, sab:'anin shi dake kallon abun a matsayin mugunta, rashin imani da kuma rashin tausayi, murmushi yayi yana godema ALLAH daya bashi d'a k'waya d'aya tamkar da dubu kafin yace.

"Amin Nuraddeen, bar na watso ruwan nima, idan baffanka yazo kace masa yajirani sai muje tare ko?"

"To baffa" yafad'a had'e da zaunawa gefen katifar dake cikin d'akin yana d'aure zaren takalminsa daya saka yanzu, azahiri idan ka kallesa cikin natsuwa zaka fahimci fuskar a sake take ba yabo ba fallasa amma acan cikin zuciyarsa akwai d'imbin miki da damuwa a cunkushe da ita, yana nan zaune baffa usman ya shigo shida Yusuf d'auke da kayan karin da aka Saba kawo masu, da sauri Nuraddeen yamiqe yana gwadawa baffa Usman gefen katifar daya tashi akai tare dasa hannayensa ya dafa kafad'un Yusuf yana fad'in.

"Sannu da zuwa baffa, Ina kwana antashi lafiya?"

"Lafiya klw Nuraddeen, Ina zuwa da wannan snyin safiya haka?"

Baffa yafad'a yana qoqarin zaunawa bakin gadon yana kallonsa, Saida ya d'an sosa qeyar kansa sannan yace, "zanje yarimawa ne nadubo jikin umma da baba.

"Af! To Masha ALLAH, dama shirin da nayo kenan saboda jiya dasu nakwana araina, kwana biyu dani har Yaya bamu samu muka leqosa ba, shiyasa nace idan nazo zanyi masa magana idan yanada dama sai muje anjima, ga Bilkeesu can itama ta dage akan lalle yau da ita zamuje don ta dubosu."

"Eh shima naji yace zaije, yashiga wankane ynzu amma yace kajirasa" yafad'a tare da jan hannun Yusuf suka fita, firarsu da mintota baffa yafito ya kimtsa sannan suka gaisa da d'an uwansa kamar yanda suka saba ko yaushe sannan su Nuraddeen suka dawo shida Yusuf suna tafe Yana yimasa firar maganganun daya ji su baffa Ali nayi aranar akan zancen korar Rashida cikin gidan don ya auri yayarsa muneera, tuni Nuraddeen yagama sadaqarwa da anhalakar masa da Maya wanda inba ubangiji ba Babu wanda ya isa yace yasan inda take, murmushin da yafi kuka ciwo yayi had'e da rumqe hannun Yusuf sosai sannn yace.

"Yusuf me kake tunani akan auntynka Rashida, za'a ganeta kuwa?, tana raye ita da abunda ke cikinta ko kuma..."

Bai qarasa fad'aba sakamakon k'wace hannun da yasufa yayi tare da tsayawa agabansa yana d'aga yatsa had'e da cewa. "Kada kace komai Yaya, ai ba'a yanke qauna da rahamar ALLAH, muci gaba da addu'a in Sha ALLAH za'aganeta kome daren dad'ewa kuma da yardar ALLAH suna cikin qoshin lafiya duk inda suke."

"Yusuf waya fad'a maka haka?."

Nuraddeen ya tambayesa cike da mamakin kalaman dake fita daga bakinsa, riqe hannunsa Yusuf yayi sannan yace. "Inajin baffa Usman da Inna Bilkisu nafad'a akoda yaushe kuma suna addu'a shiyasa nace haka don nasan addu'ar iyaye karb'ab'b'ace."

"Tabbas hakane yusuf ALLAH ya karb'a mana addu'o'inku baki d'aya."

"Amin Yaya, wai yaushene zaka wuce?"

"Ina fa?"

Nuraddeen yafad'a cikin rashin sani don yama manta da zancen tafiyar tasu, Yusuf daya qura masa idanuwa yana kallo yace "baffa Usman yace zakaje malesia wajen qaro karatu."

"Oh! Kash ai namanta, in Sha ALLAH zuwa wani satin zamu fara tashi."

"Zamuyi kewarka Yaya sosai, yanzu ma da baka gida bkaji yanda muke kewar kana balle kamar qasarnan, no bana so katafi gaba d'aya ma." Dariya yayi yana shafa kansa had'e da cewa. "Nima bana so Yusuf saboda tunanin auntynka, Amma idan har Ina so damuwar da nake ciki ta rage dole sai nayi nesa da duk wani abun daya zamo silar rabani da ita wannan shi kad'aine zai ragemun zafi da sililin da nakeji azuciyata" da wannan firar suka qarasa shiga cikin d'akin baffa na qoqarin jawo kayan karin da suka zo masu dasu, zuwa yayi ya karb'a ya had'a masa tare da ajiye masa agabansa sannan shima ya had'a nasa yaci, bayan sun kammala baffa yad'ibi cikin kud'in da yazo dasu jiya sukaje shida baffa suka samo shatar mota bus akaje da ita qofar can gidan baffa Usman yashiga yace Inna Bilkisu tafito sannan ta sanarwa da mutanen gidan duk mai son take gano mahaifan Rashida sufito aje, ai kuwa kafin kace me motar tacika harda maqwabta, wasu zasujene don yiwa Nuraddeen kara, wasu kuma gulmace zata kaisu, Amma duk da haka baffa da Nuraddeen sunji dad'in yanda 'yan uwa da abokan arziqin suka nuna masu karamcin zuwa suyo dibiyar.

••• ••• •••
A can borno kuwa kuwa ganin yanda jikin yaron Rashida ya qiya yasa dr. Nura tunanin karb'ar masu sallama su koma gida agwada maganin hausa ko ALLAH zaisa adace tunda nan ankasa gano takamammiyar matsalar yaron, cikin sa'a kuwa daya yiwa likitocin bayani suka fahimta aka basu sallama suka koma gida, ranar Rashida taqara shiga tashin hankali ganin yanda d'an qaramin yaro da bayada alhakin kowa keahan wahala, Babu abunda yafirgitata irin ganin yanda yake fizge fizge yana wani abun, hakan yasa tafara wani tunani aranta Wanda aqasan zuciyarta take neman ysarin ALLAH akan faruwar hakan, da marece Dr nura yaje yakirawo wani malami yazo dashi nan gida saboda yaduba yaron, ranar kam sunsha mamaki ganin abubuwan da malmin keyi masa wanda Fatima dake riqe dashi tausayinsa yasa takasa saidai shi Dr. Nura d'in ya karb'esa, addu'o'i ya dinga yiwa yaron yana tofawa aruwa had'e da watsa masa a fuskarsa da jiki shikuma yaron na wani irin kuka mai matuqar tsima rai sosai, duk lokacin da malamin ya watsa masa ruwan addu'ar sai ya kwanyara ihu tare da fashewa da kuka mai tsananin qara, hakan yasa Rashida dake d'aki ta daddad'e kunnuwanta da filo saboda yanda takejin kukan nasa har cikin ranta takasa jurewa, aguje tafito tanufi falon Dr. Nura inda suke zaune, Kai tsaye tashiga ciki ko sallama babu tare da karb'ar jaririn a hannun Dr nura tad'orasa asaman kafad'arta tana kuka, had'a hannayenta tayi waje d'aya tana ja da baya had'e da cewa.

"Malan don ALLAH kabarmun jaririna haka, zan iya jure rashinsa kamar yanda najure rashin mahaifinsa, zan iya yin haqurin ganinsa acikin halin da yake ciki kamar yanda nahaqura da rashin sanin halin da mahaifana keciki amma bazan iya jurewa wannan kukan nasa ba, domin jinsa nakeyi har cikin zuciyata da kuma rouhina, sannin akwai abunda akeyi masa yasa nakeji tamkar cutar dashi ne akeyi, kayi hak'uri malan don ALLAH kaje..." Cike da b'acin rai dr. nura ya taso ya nufo inda take zai karb'esa tace.

"Don ALLAH uncle kabarmun yarona, ka sallami malaminnan kace yatafi."

"Rashida Anya kina cikin hankalinki kuwa? Duk haqurin da kikayi na tsawon wata hud'u yaronnan baya tare dake batare da kin d'aga hankalinki akansa ba sai yau zaki kasa jurewa, karki manta kowace cuta aduniya tanada magani, Kuma ALLAH ya halasta anemesa, don haka miqo munshi kafin na sab'a maki."

"Uncle kukan nasa tamkar yana fita da lumfashina ne, idan zanci gaba da saurara zan iya rasa Raina, shi kad'aine farincikin daya yaragemun aduniya don ALLAH kubarmun shi kada shima narasa shi."

"Rashida.." Dr nura yafad'a da a tsawace ransa na neman b'aci. Sake dafe kan yaron tayi da hannunta tanajin yanda yake kukan zuciyarsa nabugawa da sauri saur, tasowa malamin yayi daga inda yake zaune ya dawo inda take tsaye yace.

"Shikenan ya isa koma can ki zauna." Adarare tabi ta gefensu ganin yanda ran Dr yad'an b'aci,

Bayan ta zauna malamin yaje gabanta ya zauna shida Dr nura, har lokacin yaron na rungume ajikinta tariqe sosai tamkar za'a k'wace mata shi, kallonta malamin yayi na tsawon mintuna kafin yace.

"Kece mahaifiyar sa." Kasa amsa masa tayi saidai ta d'aga masa kai idanuwanta na tsiyayar da hawaye.

Jinjina kai yayi kafin yaci gaba da cewa.

"Shin antab'a fad'a maki cewa kinada aljanu.?" Nan ma girgiza masa kai tayi da sauri cike da fargabar abunda take tsammanin zai iya fitowa daga bakinsa, kallon Dr nura yayi had'e da cewa.

"Wannan jaririn da kake gani tun yana ciki aljanu ke tare dashi, sunso su hallakasa ko Kuma su shiga jikinsa amma Allah ya sha makance shi da hakan, shine suka shafesa ba tare da sun iya samun nasarar shiga jikinsa ba, wanda nake tunanin su wud'annan aljanun kamar na mahaifiyar tasa ne, Amma sai gashi tace ba tadasu kuma natabbatar da hakan saboda yanda alamom suka nuna batada su, nan Dr nura yayi masa bayanin abubuwan da suka faru da ita dalla dalla har zuwa lokacin daya tsinceta kamar dai yanda tayi masu bayani a farko,

"To malam inaga wannan dalilin shiyasa sukabi ta wannan hanyar don su cutar dashi yaron tunda sun kasa shiga jikin mahaifiyarsa ko cutar da ita."

jinjina kai malamin yayi had'e da cewa.

"Tabbas hakane, kuma da yardar ALLAH, da qarfin ikonsa shima dole su barshi ta hanyar addu'o'i da magungunan da zan baki kafin suyi galabar shiga jikinsa gaba d'aya. Sannan zamuyi masa karatun al-qur'ani wato (ruquya) don kauda duk wata barazana da suke sonyi wajen shiga jikinsa."

Miqewa tayi ta d'orawa Dr. Yaron ajiki sannan tamiqi hanyar fita tana goge hawaye, a yanzu gaba d'aya ta gama gamsuwa da bayanin da malamin yayi don haka ta amince da duk abunda za'ayi masa kuma zata jure hakan.

"Dawo ki d'aukesa." Dr. nura yafad'a yana kallonta.

"Jeki." Malamin yafad'a ganin lokaci na dad'a qurewa, karb'ar yaron yayi yace yaje yayo arwala, bayan yadawo shima malamin yaje yayo tasa duk da yanada tabbacin yanada ita, nan take yafara yiwa jaririn ruquya, wani irin kuka yaron ya fashe dashi bayan tun d'azu ya dena kukan, tun yanayi da qarfi gidan ya karad'e da kukansa har ya farayi ahankali, itama tacan b'angaren Rashida da ita har fatimar kuka sukeyi jin kukansa da sukeyi har yadena, ganin sukayi jikinsa gaba d'aya ya saki tamkar wanda bayada rai lumfashinsa nafita ahankali, da alama baccine ya d'auki jaririn sosai, ajiyar zuciya malamin yayi had'e da cewa.
Chapter 60 · 0% Book details