← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 146 OF 160

Sashe 146

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Godiya litte yayi masa sosai cike da farinciki sannan ya amshi makullin motar yanufi inda take, bayansa Dr yabi yariqa masa suka cire ledar dake jikinta sannan yashiga cikinta bakinsa d'auke da addu'a ya fiddo tare da sake fita ya kwaso kayansu a waccan motar yazuba sannan suka sake yimasu sallama suka shiga suka tafi su Dr da ita rashidar da Fatima da sauran yaransu nayi masu addu'ar ALLAH ya saukesu lafiya bayan ya tabbatar masa dasu tafi ahankali har su isa lafiya don SANNU SANNU bazata hana tafiya ba...tunda har sun tashi dawuri.

Suna kan hanya hajia nafeesa takira awaya don tun jiya sukayi sallama dasu tace mata gasu sun kama hanya a sakasu a addu'a, cike da jin dad'i tayita zuba masu addu'a tanaji tamkar tabisu taga irin farincikin da Abba zaiyi idan yaga yanda batool d'insa takoma fiye da yanda take son ta kasance akoda yaushe, tasan baqaramin dad'i zaiji ba musamman idan yaga 'yan kyawawan jikokinsa.

Suna gama waya takira hajia mama da Abba tayi masu albishir cewa Batool d'insu nakan hanya batare da tasan zullumin da suke ciki akan faruwar hakan ba.

Suna gama wayar hawaye suka ratatowa hajiya mama a fuska, cikin tawakkali tare da miqa dukkanin lamurranta ga ALLAH tace.

"Ubangiji ALLAH ya kawosu lafiya, dama nasan kafiyar batool bazata bari ta haqura ba, musamman yanda kullum take fata da d'okin ganin wannan ranar da abbanta zai jaye tsattsaurar katangar daya shata a tsakaninsu."

Kallon Abba tayi da fitowarsa kenan wanka yana goge jiki yaji abunda hajia nafeesa tafad'a yayi mutuwar tsaye awajen.

"Kayi haquri ka amshi duk abunda ALLAH zai zo mana dashi duk da ni aqasan zuciyata banyi Imani da mafarkinka zai tabbata akansu ba, Abu d'aya nayi imani dashi shine, ALLAH yakan sassauta jarabawar bayin da suka roqesa kuma ya sauqaqa qaddarar daya tsaro zata faru akansu, don haka kawai ku haqura da wannan tafiya kuma muyi fatan ALLAH yakawosu lafiya."

Kasa cewa komai yayi yayi qarfin hali yagyara yaje ya sanar da 'yan uwansa da tuni suma sun shiryo da zimmar tafiyar, nan take duk sai sukaji jikinsu yayi sanyi Amma sai sukayi qoqarin b'oye hakan don kar damuwarsa ta lunku.

Arwala hajia mama tayi taje taci gaba da ganawa da ubngijinta akan ALLAH ya kawo masu su lafiya.

••• ••• •••
Dr Nuraddeen kuwa yana tashi da asuba bayan ya gama sallah tare da azkar yasamu manajan hotal din yace yana buqtar a bincika masa idan akwai jirgin da zai tashi zuwa kano yau ayi masa booking..

Nan take da yake sun gashi da maiqonsa ba'afi mintuna goma ba suka binciko masa amma jirgin sai zuwa Sha biyu da rabi na rana zai tashi, baiso hakan ba, gashi bazai iya doguwar tafiya ba saboda yanayin gajiyar dake tare dashi da wani iri da yake jin kansa saboda fargabar data addabesa kuma bazai iya bin motar kasuwa ba yasa dole ya haqura yace ayi masa booking dinsa hakanan.

Tuni ma'aikatan airport d'in suka sanar da 'yan jarida da 'yan redio cewa shahararren likitan da ska buqaci subasu bayani akansa jirginsa zai tashi nan da awanni hud'u da rabi kamar yanda yayi booking da safennan.

Kan kace me tuni manema labaran suka Isa filin jirgin bayan sun sanar da abokanan aikinsu dake kano cewa su zamo cikin shiri don wanda suke neman labaransa zai iso nan da awanni biyar da rabi masu zuwa.

Lokaci na cika ya shirya cikin suit d'insa farare sai jar riga ta ciki da farin necktie yasa takalma irin cover shoe's din nan suma farare sannan ya d'auki jikkarsa yaje ya biya charges din masu hotel d'in tare da yimasu alkhairi Mai tsoka suna ta jin dad'i had'e da yimasa godiya.

Tsabar farinciki manajan da kansa ya d'aukesa cikin motarsa ya kaisa airport,

Yanda yaga taron manema labarai ya tabbatar masa da cewa sun samu labarin dawowarsa kenan, cikin halin ko inkula yafito ya fara takawa zuwa bakin jirgin don tuni an soma kiran pasinjas don har sun soma makara, kasancewar tuni fuskarsa ta bayyana ga labaran qasar malesia yasa suna ganin fitowarsa sukayo ruuu kansa, sai dai yaga hasken kyamarori na bugar masa buska da wasu dogayen abun magana da aka karo masa,

Fuskarsa ba yabo ba fallasa ya tsaya yana fuskantarsu daidai yana jiran tambayoyin da suka shirya yimasa, Wanda kai tsaye labaran suke tafiya ga kafafen yad'a labarai.

Tunda suka fara tambayoyinsu bai amsa masu ko d'aya ba har sai da yaji sun saurara.

Daidai lokacin Rashida ta shigo cikin falon su Dr da fatima na zaune suna kallon labaran da tun safe suke jin ana yayatawar dawowar wani shahararren likita, amma ko kad'an basu kawo hakan aransu ba cewa wai Dr Nuraddeen ne mijin Rashida, Saida sukaji cikin harshensa na turanci yafara amsa masu tambaya d'aya wacce ita kad'ai yaji zai amsa, lokacin Rashida na bayansu tayi mutuwar tsaye ganin fuskar da bazata tab'a iya mancewa da ita ba.

_"Nadawo qasatane awannan lokacin saboda duhun da ALLAH ya yayemun dake kaina har nakasa banbance koni waye, Wanda shi kad'aine yasan dalilinsa na jarabtata da hakan, batun shekarun dana kwashe awaccan qasar batare dana waiwayo qasata ba shikuma rubutacciyar qaddarar rayuwata ce dako ina so ko bana so saita tabbata akaina, zancen iyayena, ahalina da iyalina Kuma..."_ kafin ya qarasa kawai sai akaga ya fashe da kuka tare da haye matattakalar da sauri.

Ita kuwa Rashida sai jin kukanta kawai sukayi ta duqe wajen, cikin wata irin murya mai cike da ban tausayi tana fad'ar.

"Ko kad'an bayada gaskiya, bazai iya wanke kansa ba, wannan kukan duka na kunya ne da nadamar abunda ya aikatawa qasarsa, iyayensa, matarsa da kuma d'ansa har taya zai iya bada wannan amsar bayan yasan tuni yabada ita ga idanuwan duniya."

_afuwan idan bakuji dad'in rashin had'uwar little da mahaifinsa ba, ko kad'an yau idan suka had'u a titi abun bazai bada ma'ana ba balle ya qayatar, SANNU SANNU dai bazata hana mu Isa wajen ba gobe in sha ALLAH, pls kuyi haquri kuma kusani cikin addu'o'in ku saboda zazzab'i na nema yayi Mani qawanya👏thanks all_

*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

_Gaisuwa tare da fatan alkhairi agareki ROUHINAH, *FATIMA TAMBARY (BATOOL)* Aminci ya tabbata agareki tare da dukkanin alkhairan Allah bisa soyayya da qaunar da kike nunamun, fatana ubangiji ALLAH ya baki miji nagari da zai kula dake har qarshen rayuwarki kuma yakare mana ke aduk in da kike, soyayyarki ga wannan littafi na matuqar faranta mani, ubangiji ALLAH yabar tare har a aljannah fiddausi👏_

Page___103💎

Tsaye sukayi had'e da qurawa motar idanuwa suna kallo, yayinda d'an jaridar naganin motar ya juya da gudu yanufi wajen riqe da makirfon d'insa hannu.

Kafin kace me tuni manema labaran sun dandazo a bakin motar sai hasken kemarori kawai kake gani nafita tako ina tun kafin yafito, so yake yafito amma duk sun tare wajen babu ta yanda za'ayi ya bud'e gambun motar balle yasamu fitowa, hakan yasa yayi zaunensa aci yana kallon ikon ALLAH, wata motar jami'an tsaro ce naga ta shigo aguje wanda mataimakin gwamnan jahane ya sake turosu saboda sanin taron da 'yan jaridu sukayiwa garin don kar wata matsala tafaru, tun kafin motar ta tsaya wasunsu suka dingi dirqowa daga samanta suna kukkutsawa cikin mutane da tutturesu gefe har suka iso bakin motar suna faman mazurai da idanuwa.

Saida suka tabbatar an saki hanyar da zai iya wucewa sannan wani yasa hannu ya bud'e masa gambun motar, a hankali ya azo qafarsa waje kafin ya ida fitowa da gangar jikinsa gaba d'aya yana qarewa qofar gidansu kallo, tana nan ayanda yasanta babu wani sauyi atattare da ita balle jikin gidan, wata irin damuwa yaji tarufesa yana mai tuhumar kansa akan cewa duk laifinsa ne daya jawo wannan rashin samuwar sauyin da aka samu ako Ina cikin wannan shekarun atattare da iyayensa, ji yayi wasu zafafan hawaye sun zubo masa xubo masa a fuska ga 'yan jarida kuwa sai famana aikinsu sukeyi na yimasa hotuna, cikin sanyin jiki ya fara takawa zuwa wajen yayin da su kuma su baffa dake kallon ikon ALLAH daya ishesu tun d'azu ganin yanda hankalin kowa yakoma akan wannan motar ana jiran fitowar ko suwaye aciki amma shiru yaqi fitowa suka fara qoqarin juyawarsu da nufin shigewa gida, suna juyawa suka sake juyowa da sauri saboda tozalin da idanuwansu suka yimasu da fuskar mai fitowa daga cikin motar da bazasu tab'a manta tab'a, cikin wani irin matsanancin mamaki baffa ya shiga nunasa da hannu, murza idanuwasa ya sakeyi yana son gasgata abunda suka gane masa, tabbas ba shakka wannan Nuraddeen d'insa ne, cikin karkarwar murya bakinsa na rawa yafara matsawa zuwa garesa yana cigaba da nunasa yana fad'in,

"Sh..shi..shinefa Usman, d'a..d'ana ne nu..ra!,"
Chapter 146 · 0% Book details