← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 160

Sashe 6

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai bayan kusan mintuna biyar sannan suka fito tare da Dr naseer d'in suka nufi wajen da su uncle h suke tsaye, gaisawa suka farayi dashi sannan yayi masu bayanin ALLAH yayiwa patient d'insu wato Abu sumayya rasuwa...salati suka farayi tare da jinjina al'amarin, tabbas sunji ba dad'i rasa nagartaccen mutum irin Abu sumayya adaidai wannan lokacin da suke tunanin shine cikar burinsa da kuma farincikinsa don uncle hussain ahadda hawayensa, haquri suka basu sosai tare da addu'ar ALLAH ya gafarta masa sannan Dr sadeeq yace suwuce gyni saboda ga alama Abba baizo nan ba,

Jikinsu a sanyaye suka bar wajen suna tuna irin muqabalar daya fuskanta kafin su bashi auren 'yar tasu.

Suna isa Dr da d'azu suka magantu da shurahbil nafitowa wasu nurses su biyu na biye da ita abaya d'auke da jarirai guda biyu a hannunsu, kallonsu tayi tace

"A'ah Dr sadeeq barka da Rana, yau kaine a ward d'inmu?"

"Barka Dr imaan, ya zamuyi nabiyo patient d'inmu da muka kawo anan wacce tasamu accident, so dama d'azu da mukazo ake fad'amun kece on duty keda su Dr odugun da Dr na'eem hop anyi nasara wajen aiki"

"Yeah upcouse, Ashe kaine Dr na'eem ke kwatantamun, ya aiki?"

"Alhamdulilah Dr." Tafad'a tare da kallonsu uncle h dasu Abba dake tsaye suka gaisa sannan tace

"Ok Dr wud'annan sune relatives d'in patient d'inka"

"Eh Dr imaan"

"Ok congratulation Alhaji anyi nasarar ciro mata 'yan biyu macce da namiji amma.." kafin ta iyar Abba yafashe da kuka yace,

"Shikenan dama nasan hakan zata faru, ya ALLAH kayafemun, yau gashi nayi sanadiyar jefa kaina cikin huznu dalilin nisanta kaina da ita da nayi, ta tafi tabarni da mikin da har lokacin da za'a karb'i tawa rayuwar bazai warkemun ba." Dafa kafad'arsa Dr imaan tayi had'e da cewa

"Haba baba! Waya fad'a maka 'yarka tarasu, 'yarka na a raye saidai ba wannan kukan naka take buqata ba, kayi hak'uri addu'arka ita take so yanzu kaji" wani irin sanyi yaji azuciyarsa wanda saida hakan ya bayyana qarara a fuskarsa ya juya gabas yayi sujudush shukur had'e da kallonsu uncle h da fuskokinsu suka kasa bayyana farinciki ko kuma damuwar da suke ciki yace,

"Alhamdulilah, Hassan hussaini 'yarku naraye bata mutu ba, kuzo kuyiwa ALLAH godiya kunji ko." ganin yanda fuskokinsu suke yasa hankalinshi ya koma akan mijinnata da sauri ya qarasa inda Dr sadeeq yake yace,

"Dr ya jikin mai gidan nata?"

"Sai hak'uri Alhaji shikam ALLAH yayi masa cikawa"

"Innalillahi wainna ilaihirrajiun" Abba yafad'a da k'arfi tare da fad'uwa zaune, duk wanda ke wajwn jikinsa yayi sanyi jin cewa Abu sumayya ya rasu, hatta Dr imaan saida taji shock atare da ita saboda tunowa da halin da matar ke ciki, "ALLAH yajiqansa tafurta tare da juyawa ta koma cikin d'akin tiyata"

Su uncle h suka karb'i yaran suna kallo tubarkallah masha ALLAH dasu, kyawawa dasu sak kamar mahaifiyarsu gasu da girma sosai, hud'uba suka yimasu sannan sukaba nurses d'in su aka koma dasu ciki saboda ga alama basuda lafiya don gaba d'aya hannuwansu saye suke da calular irinta qarin ruwa,

Shurahbil kuwa jiyayi tamkar kar arabashi da jaririyar dake hannunsa wacce itace hussaina d'an namijin kuma shine hassan yana ta kallonsu har suka shige dasu ciki, hakan ne yasa
ya tuno da yabaro 'yan uwansu a mota d'azu kuma bai rufeba, ai da sauri ya juya yamik'i hanyar inda suka ajiye motar,

Yana zuwa ya tarar basu cikin motar, nan take duk hankalinsa yatashi yafara dube dube harda qarqashin mota, kamar ance ya juyo ya hangosu cikin motar mutumen ya kunna masu laptop suna kallo hankali kwance, zaro idanuwa shurahbil yayi tare da qarasowa wajen yafara bubbuga glass d'in motar saboda duka a kukkulle suke saboda a.c da aka kunna, a hankali mutumen yafara sauke glass d'in motar tare da juyowa yana kallon shurahbil...

*_ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU👏🏻😭_*
[8/17, 10:18] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___5💎

A yanayin da barrister kamal yashiga wajen iyalinsa dake zaune a babban falon dake tsakiyar d'akunansu suna fira ya tabbatar masu da cewa akwai matsala, hakan yasa amaryarsa meenatu dake d'auke da tsohon ciki wata takwas miqewa da nufin barin wajen saboda 'yar uwar tata sajida da yake d'akinta tasamu damar rarrashinsa da kuma kwantar masa da hankali, kirawota yayi cikin sanyin murya yace

"Ina kuma zakije?."

"Zanje na kwanta dama muna jiran dawowar kane munji shiru."

"Shine kuma zaki tafi baki jira jin dalilin daya dad'ar dani ba?."

"Kayi hak'uri, baccin ne yariga yazo kuma kasan yanayin jikin nawa" tak'arasa maganar tana faman lumshe idanuwa irin na masujin baccinnan, hannunta yariqa tare da rakata har cikin d'akinta yasa taje tayo arwalar bacci sannan ta kwanta ya lullub'amata bargo tare da kashe mata fitala sannan yafito.

Zaune ya isko sajida takawo masa abinci da ruwa don gaba d'aya yau ko lunch besamu yayi ba saboda tashin hankali tana jiransa, qarasaw yayi tare da zaunawa k'asan kujera ya mik'e k'afafuwansa sannan yace,

"Sannu nabarki kina jirana ko, kinsan halin 'yar uwar taki..."

"Ba komai." tafad'a batare da tabari ya iyar ba ta tsiyaya masa ruwa masu sanyi a cup ta miqa masa, karb'a yayi ya kurb'a ruwan sannan ya ajiye agefe, k'ok'arin rik'e hannunta yayi lokacin da takai hannuwanta saman kular abincin yace,

"Kibarshi wifey, bazan iya ciba."

"Subhanallahi! Kayi hak'uri kaci kad'an kada yunwa ta kamaka"

"Bana cikin yanayin da abinci zai iya shiga cikina sajida..." Nan ya sanar da ita abunda kefaruwa da kuma rasuwar Abu sumayya.

Hannu biyu biyu tad'ora abaki tana qoqarin danne sautin kukan daya zo mata saboda ba b.kamal kad'ai ba hatta su da suke matansa sunsan da karamci da kuma kyautatawa irin ta abu sumayya, mutumne Mai mutunci da kuma tausayi da sanin haqqin musulmi d'an uwansa, rungumota yayi yana rarrashinta tare da cewa,

"Nayi rashin aminin qwarai daga cikin aminaina, yanzu babu abunda yarage awajena tsakanina dashi kamar inbisa da addu'a, haka kuma, domin shine zai tabbatar da soyayyarmu agaresa bisa kyautatawarsa agaremu." Addu'a tayi masa sosai tana kuka kafin yatayar da ita suwuce d'aki, har zasu shiga yaja hannunta suka shiga d'ayan d'akin da yaransu ke ciki ya kunna fitila yaga duk suna lafiya sannan ya sake gyara masu kwanciyarsu suka yimasu addu'a sannan suka wuce d'akinsu, kamar yanda yayiwa meenatu haka yayiwa sajida itama sannan yadawo falo ya zauna tare da rafka tagumi yana tunano hirarsu taqarshe kafin sutafi da kalar dariyar shaqiyancin da yatayi masa akan yanda yaga yana nan nan dasu meenatu saboda kada ran kowacensu ya b'aci, maganarsa zancensa na qarshe shine.

_ni dai Gimbiya ta isheni anan duniya babuni babu yimata kishiya balle inyi tunanin raba mata soyayyata da kuma kalaman bakina da zuciyata ita da wata, nayarda da ita da kuma nagartacciyar soyayyarta agareni, Ina fatar kuma ALLAH ya yarda da ita kuma ya sota, nine noora amma azahiri batool itace wannan sunan hasken da ake kirana dashi, wlh badon ALLAH yatsaro a aljannah dolene za'a bamu wasu matanba da ni Abu sumayya nace ALLAH yabarni da gimbiyata ta isheni, ALLAH kasa gaba d'aya matan hurul ayni da za'a bani kamanninsu da komai nasu irin na gimbiyata ne._

Girgiza kai yayi had'e da cewa, "ALLAHU akabar, duniya kennan, ya ALLAH ka amintar dashi ga dukkanin muradansa na alkhairi." Sannan yamik'e shima yayo arwala ya tayar da sallah, haka shima Abba kasa kwana yayi banda tunanin abubuwan da suka faru a shekarun baya da kuma tunanin halin da 'yarsa take ciki Babu abunda yakeyi, hakan yasa yayo arwala ya fuskanci gabas don samun sassauci, a b'angaren hajia mama ma dake asibiti itama d'in hakan tayi don samun sasauci acikin yanayin da suke ciki.

Daren ranar kam gaba d'aya wud'annan ahali guda biyu kasa bacci sukayi musamman Abba da gwaggo da hajia mama da kuma barrister kamal cikakken aboki managarci awajen Abu sumayya, kwana sukayi bisa abun sallolinsu suna addu'ah ALLAH yagafartawa Abu sumayya kuma yaba iyalinsa lafiya ya albarkaci abunda yabari, banda gwaggo da addu'arta ta tafi wajen ALLAH yaba yaronta lafiya ya tashi kafad'unsa shima yasamu cikar farincikinsa kuma yaraya masa abunda tahaifa yabata lafiya.

Tun da asubar fari ya kirawo abokanansu na kusa dana nesa ya sanar dasu rasuwar aminin nasu tare da tabbatar masu da cewa yanzu haka suna shirin tafiya can kano saboda acan yarasu kuma yanasa ran acan za'ayi jana'izarsa, rana nafitowa ya iske gwaggo bayan sun gaisa yace yakamata tashirya suje kano, hakan kuwa ya matuqar yimata dad'i saboda jiya zaune takwana ana nuno mata fuskar d'anta tare da hakaito mata yanayin da yake ciki, duk hankalinta yabi ya tashi taga nawar safiya tawaye, saboda yanayin da meenatu ke ciki yasa yace sajida tayi hak'uri tazauna gida Idan sun dawo shida gwaggo sai yakaita tayowa batool gaisuwa kafin itama meenatu ALLAH ya sauketa lafiya.

Haka kuwa akayi sajida ta gyara masa kayansa meenatu nata kuka don sai alokacin yasanar da ita abunda kefaruwa suka kama hanya shida gwaggo da wani mak'wabcinsu babban mutumne sosai tare da matar da kuma zainab da itama kukan takeyi jin d'an uwanta na kwance aadon asibiti shida autynta da take matuk'ar k'auna, abunda bata sani ba shi gaba d'ayama yabar duniya.

Koda k'arfe d'aya na rana tayi har sun isa garin kano dama yakira yasanar dasu Abba suna kan hanya, suna isa ambulance na ajiye gawar Abu sumayya a k'ofar gidansu Abba, tsayawa fad'ar halin da gwaggo tashiga ciki abun zubarwa hawayene sosai amma daga qarshe ta dangana tabarwa Allah,
Chapter 6 · 0% Book details