Sashe 132
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan sati d'aya da yin hakan takira mahaifiyarta hajia mama suka gaisa sannan tayi mata batun komawarta gida wajen wankan jego, ai kuwa nan hajia mama tayita yimata fad'a had'e da cewa tayi haquri ta zaunawarta gidan mijinta ta haihu babu abunda zai faru da ita in sha ALLAH tunda tana samun cikakkiyar kulawar da koda itace ke tare da ita iyakar ta zata bata, duk da bata so hakan ba haka ta haqura don kuwa ba k'arya gwargwado babu abunda tanema tarasa a fannin kulawa tun daga kan mijinta har zuwa mahaifiyarsa da sauran natare da ita, sun zame mata uwa da uba kuma sunyi mata gatar da bata tab'a tsammani ba aduniya don haka dole ta haqura da ra'ayinta tabi umurnin mahaifiyarta, haka taci taci gaba da renon cikinta yau ciwo gobe lafiya har watan haihuwarta ya kama,
Ranar tana zaune taga little yashigo kai tsaye yawuce d'aki yaje ya harhad'o mata kayanta cikin akwatuna biyu ya fiddosu falo sannan yakoma ya d'auko mata mayafinta yana fad'in.
"Gimbiya tashi muje.."
Binshi tayi da wani irin kallo dake cike da tarin tambayoyi kala kala da take buqatar ya amsa mata kafin sutafi yayi murmushi had'e da cewa.
"Easy madam! Bafa Saida ki zanyi ba, wannan irin kallo haka ai sai kisa 'yan kayan cikina zubikkewa."
Saida tayi dariya sannan yace. "Ahh.. to! Ba dole ba naga notice tsakar rana bazato ba tsammani."
'Dan matse fuska yayi kamar mai shirin kuka had'e da cewa. "Yana iya gimbiya! Gwaggo tace nakawo mata 'yarta yau d'innan ba sai gobe ba tunda watan haihuwarki yakama bazai yuyu kizauna ke kad'ai agida ba, nace zan ajiye aikina mu zauna gidan tare tace a'a, nace aturo maki Shahida shima tace bata amince ba, kinga kuwa dole na cika umurninta."
"Aw! Akan wannan abun d'an abun kake b'ata rai?, Lallei Abu sumayya kice kashagwab'e da yawa yanzu, Ina can d'in ba baqonka bane tunda bawani waje za'a kaini ba, ni danaso komawa kano gaba d'aya nahaihu can da sai kayi qaqa?"
"Tab inbiki mana!"
"Da kuwa katabbata bita zaizai gaskiya."
Taqare maganar had'e da tuntsirewa da dariya can kawai yaga hawaye na zubo mata dariyar takoma kuka, da sauri yaqarasa kusa gareta ya zauna tare da jawota ajiki yana fad'in.
"Gimbiya menene?" Ta d'ora kanta aqirjinsa had'e da cewa.
"Abbana, Ina son naga Abbana ko sau d'ayane, bana son namutu ban ganesa ba."
"Yaa salaam! Gimbiya meya kawo zancen mutuwa kuma, bazaki mutuba har sai muntarawa Abba jikoki da yawa da zaiyi alfahari dasu, kinsan ko jiya saida likita yafad'a maki cewa kirage damuwarnan da yawa tana tab'a lafiyar babynmu, shine kike kuka yanzu bakya son yafito very healthy ne?"
"Ina so mana, Amma bazn iya dena damuwa akan Abbana ba, Ina so naji muryarsa pls Abu sumayya ko a'ane."
Ganin yanda duk tabi tarikice masa yasa yaciro wayarsa had'e da kallonta yace.
"Idan kikaji muryarsa kinyimun alqawarin zaki dena wannan kukan?"
Da sauri ta d'aga masa kai yayi murmushi had'e da shafo kanta dake saman qirjinsa sannan yakira Abba da d'ayan layinsa na (data) da yake using dashi, don tunda ya gwada kiransa bayan auren sau d'aya suka gaisa yagano shine yadena samunsa daga baya idan yakira, may be ya kulle masa layine ta yanda bazai iya samun saba. Bugu d'aya Abba ya d'aga yana fad'in.
"Hello, hello assalamu alaikum." Can yayi tsaki jin ba'a amsa shiba had'e da kashe kiran, d'ago kai tayi ta kallesa hakan yasa yasake kiran lambar yana murmushi.
"Assalamu alaikum." Abba yafad'a awannan karon tare dayin shiru yana jiran a amsa masa a d'aya b'angaren, jin ba'a amsashi ba yasa ya sake tsinke kiran little yasake kira akaro na ukku.
A hasale abba ya d'aga kiran yana fad'in.
"Wai wayene halan? Idan ba'ada abuncewa kar asake kira, shashancin banza da wofi."
Amai makon ya katse kiran saiya ajiye wayar yaci gaba da fad'ansa yana fad'in.
"Wannan ai shashancine akira waya akasa magana, mutane sun d'auka yanda basada abunyi kowama baya dashi, saika rufesu da fad'a akama srry is wrong nomba."
Dariya batool takamayi ita da little tana goge hawayen da suka zubo mata, azahirin gaskiya taji dad'in jin muryar mahaifinta sosai amma aqarqashin zuciyarta wata irin kewarsa ce ta sake rufeta, tana matuqar son mahaifinta fiye da tsammani saboda tsananin shaquwar dake tsakaninsu abunma ba'a magana, qaddarowar son dake tsakaninta da little tajawo mata rabuwa dashi badon ranta yaso ba, cikin dubaru had'e da so da qauna little ya dinga fad'a mata kalamai masu sanyi da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga damuwar dake fuskarta ta gushe daga nan kuma ya karkata akalarsa izuwa muradinsa har saida suka farantawa juna rai sannan ya taimaka mata tayo wanka tashirya, akwatunan tajawo tasake gyara duk abunda take da buqata sannan yafito dasu yasa cikin mota, tana qoqarin fitowa yaja hannunta suka koma cikin d'aki shima ya d'auko wata jikka ya dinga jidar kayansa yana zubawa.
Turo idanuwanta tayi awaje tana dariya tace.
"Abu sumayya ya haka!, Ina zuwa da wannan uwar jikka haka kake ta loda kaya."
"Tab..ai wlh qafarki qafata bazan zauna ba, mezanyi agidan nima can zan koma ai inada nawa d'akin."
Dariya ta dinga yimasa har tana riqe ciki had'e da cewa.
"Ashe ko kaida gwaggo."
"Eh naji dai, amma bazan zauna anan ba ke kina acan sai kace wani mara gata." Yaqarasa maganar yana kulle zip d'in jikkar suka fice tare yanaci gaba da jinini tana dariya.
Satinta uku da komawa gidan Dr wajen Rashida wanda gaba d'aya duk kulawar daya kamata tasamu Rashida nabata wand idan kagani kai karantse kace 'yartace ba suruka ba, yauma kwance take saman gadon bayan sallar magrib Rashida na gefe tana jan carbinta sai kawai taga ta zabura, da sauri ta katse lazumin had'e da miqewa tanu wajenta ganin tariqe kunkuru,
"Batool lafiya?."
"Wash..gwaggo bayana."
"Subhanallahi sannu ko haihuwarce?" Bata tsay jin amsar da zata bata ba da sauri tajawo wayarta takira little sannan tayi cikin gida ta sanar da fatima."
Kan kace me gaba d'ayansu hankalinsu yatashi suka nufi d'akin da sauri, dur qushe suka iskota gefen gado tana yarfi da hannuwa tana cizon baki, ga wani zufa daya tartso mata alokaci d'aya saboda tsananin azabar naquda, ganin haihuwarce zangu zangu yasa Rashida ta d'auko wata qatuwar leda ta shimfid'a mata tare da zane sabo sannan suka kamata ita da fatima suka maida wajen, tun batool na juriya har azabar zafin ciwon naquda tasa tafara kiran abbanta tana fitar da wani iska abaki,
Wani irin tausayinta yarufe Rashida tunawa da irin yanda azabar haihuwa take da tayi, safa da marwa ta shigayi tana karanto addu'o'in da tasani abaki tare da nema mata sauqin rad'ad'in da take ji, bini bini tajuyo tayi mata sannu fatima kuwa tuni tafita taje takirawo Dr, yana zuwa yasa suka riqota suka kaita a mota daidai lokacin little shima ya iso hankalinsa atashe Dr yace yashiga motar ya shiga sannan yaja suka nufi asibiti bayan Rashida takoma ciki ta d'auka kayan da za'a iya buqata.
Ko mintuna ashirin basuyi da Isa ba batool ta samb'alo qatuwar 'yarta kyakkyawa jawur da ita, ho ho zo kaga murna a wajen little ba'a magana don gaba d'aya bakinsa kasa rufuwa yayi musamman da aka fiddo yarinyar daga d'akin haihuwa Dr yamiqa mashi ita, gaba d'aya kamarta sak da batool d'insa babu ta inda tabarota tun daga kan hasken fata har zuwa kamannin fuska.
Kallon Rashida yayi yana dariya yace.
"Gwaggo kinga yarinyar nan gaba d'aya mamanta ta d'auko ko tayimun 'yar kara nima tayi kama dani."
Murmushi kawai Rashida tayi batare data tanka saba tanajin wani irin farinciki marar misaltuwa na mamaye mata zuciya, soqo Fatima tayi masa akai had'e da cewa.
"Lallai little ashe rashin kunyarka har takai haka ban sani ba, bazaka bamu 'yar ba kakame kariqe sai kace wanda za'a qwace mawa sai kamanninta kake fad'a mana."
"Kema dai kyafad'a, bana fad'a maki baida kunya ko kad'an ba kikace a'a, to ai gashi yau kingani da idanuwanki."
Saida yayi mata hud'uba ya rad'a mata sunanta da tunkafin tazo duniya mamanta ta rad'a mata wato (sumayya) sannan yamiqawa Fatima ita yana fad'in.
"ALLAH yaraya mana sumayya." Had'e da gyara mata d'an bargon da aka nad'ota dashi aciki daya d'an rufe mata fuska.
Baki bud'e Rashida ke kallonsa tare da mamakin rashin ta idonsa kafin taji Fatima tace
"Aikam little kabushe fitilarka, ALLAH dai ya shiryaka, in dai wannan narkakkarce badon kar in saketa tafad'i ba ace kishine nakeyi ai dana sakar maka abukka qasa."
"Mama kice dai kinga zata anshe maki Abba shiyasa kikace haka, dama tunda yafito da ita naga yanata kallonta da alama yagama qyasawa."
Taji muryar abbaty daya biyo bayansu yafad'a yana wasar baki shima, hannu yaba little suka tafe had'e da cewa.
"Congrat real Abu sumayya, ubangiji ALLAH yaraya mana."
"Amin" duk suka fad'a kafin dady yasake dawowa ya fad'a masu cewa batool na buqatar jini sai an qara mata don jininta yayi qasa, nan take suka nufi lab shi dasu abbaty da little cikin sa'a kuwa ana auna na little yazo daidai da nata aka d'ibi leda d'aya aka qara mata,
Sosai batool tasamu sauqi don anata fira da ita 'yan uwa da abokanan arziqi dake zuwa dubata, murna awajensu uncle h ba'a magana suda hajia mama da sauran mutanen gida, abbanta ma da aka sanar dashi saida wani annuri ya bayyana a fuskarsa har zaiyi magana sai kuma yayi saurin d'aure fuska yaci gaba da duba jaridarsa batare daya tanka ba, baiso tankawa ba azancen sai kuma yaji ya tsinci kansa da cewa,
"ALLAH yara itama yabata lafiyar shayarwa."
Wannan addu'ar da yayi tasa kowa jin cewa tabbas nan kusa bada jimawa ba zai daina fushi da 'yar tasa kuma yadawo da ita cikin rayuwarsa kamar yanda take ada.
Ranar tana zaune taga little yashigo kai tsaye yawuce d'aki yaje ya harhad'o mata kayanta cikin akwatuna biyu ya fiddosu falo sannan yakoma ya d'auko mata mayafinta yana fad'in.
"Gimbiya tashi muje.."
Binshi tayi da wani irin kallo dake cike da tarin tambayoyi kala kala da take buqatar ya amsa mata kafin sutafi yayi murmushi had'e da cewa.
"Easy madam! Bafa Saida ki zanyi ba, wannan irin kallo haka ai sai kisa 'yan kayan cikina zubikkewa."
Saida tayi dariya sannan yace. "Ahh.. to! Ba dole ba naga notice tsakar rana bazato ba tsammani."
'Dan matse fuska yayi kamar mai shirin kuka had'e da cewa. "Yana iya gimbiya! Gwaggo tace nakawo mata 'yarta yau d'innan ba sai gobe ba tunda watan haihuwarki yakama bazai yuyu kizauna ke kad'ai agida ba, nace zan ajiye aikina mu zauna gidan tare tace a'a, nace aturo maki Shahida shima tace bata amince ba, kinga kuwa dole na cika umurninta."
"Aw! Akan wannan abun d'an abun kake b'ata rai?, Lallei Abu sumayya kice kashagwab'e da yawa yanzu, Ina can d'in ba baqonka bane tunda bawani waje za'a kaini ba, ni danaso komawa kano gaba d'aya nahaihu can da sai kayi qaqa?"
"Tab inbiki mana!"
"Da kuwa katabbata bita zaizai gaskiya."
Taqare maganar had'e da tuntsirewa da dariya can kawai yaga hawaye na zubo mata dariyar takoma kuka, da sauri yaqarasa kusa gareta ya zauna tare da jawota ajiki yana fad'in.
"Gimbiya menene?" Ta d'ora kanta aqirjinsa had'e da cewa.
"Abbana, Ina son naga Abbana ko sau d'ayane, bana son namutu ban ganesa ba."
"Yaa salaam! Gimbiya meya kawo zancen mutuwa kuma, bazaki mutuba har sai muntarawa Abba jikoki da yawa da zaiyi alfahari dasu, kinsan ko jiya saida likita yafad'a maki cewa kirage damuwarnan da yawa tana tab'a lafiyar babynmu, shine kike kuka yanzu bakya son yafito very healthy ne?"
"Ina so mana, Amma bazn iya dena damuwa akan Abbana ba, Ina so naji muryarsa pls Abu sumayya ko a'ane."
Ganin yanda duk tabi tarikice masa yasa yaciro wayarsa had'e da kallonta yace.
"Idan kikaji muryarsa kinyimun alqawarin zaki dena wannan kukan?"
Da sauri ta d'aga masa kai yayi murmushi had'e da shafo kanta dake saman qirjinsa sannan yakira Abba da d'ayan layinsa na (data) da yake using dashi, don tunda ya gwada kiransa bayan auren sau d'aya suka gaisa yagano shine yadena samunsa daga baya idan yakira, may be ya kulle masa layine ta yanda bazai iya samun saba. Bugu d'aya Abba ya d'aga yana fad'in.
"Hello, hello assalamu alaikum." Can yayi tsaki jin ba'a amsa shiba had'e da kashe kiran, d'ago kai tayi ta kallesa hakan yasa yasake kiran lambar yana murmushi.
"Assalamu alaikum." Abba yafad'a awannan karon tare dayin shiru yana jiran a amsa masa a d'aya b'angaren, jin ba'a amsashi ba yasa ya sake tsinke kiran little yasake kira akaro na ukku.
A hasale abba ya d'aga kiran yana fad'in.
"Wai wayene halan? Idan ba'ada abuncewa kar asake kira, shashancin banza da wofi."
Amai makon ya katse kiran saiya ajiye wayar yaci gaba da fad'ansa yana fad'in.
"Wannan ai shashancine akira waya akasa magana, mutane sun d'auka yanda basada abunyi kowama baya dashi, saika rufesu da fad'a akama srry is wrong nomba."
Dariya batool takamayi ita da little tana goge hawayen da suka zubo mata, azahirin gaskiya taji dad'in jin muryar mahaifinta sosai amma aqarqashin zuciyarta wata irin kewarsa ce ta sake rufeta, tana matuqar son mahaifinta fiye da tsammani saboda tsananin shaquwar dake tsakaninsu abunma ba'a magana, qaddarowar son dake tsakaninta da little tajawo mata rabuwa dashi badon ranta yaso ba, cikin dubaru had'e da so da qauna little ya dinga fad'a mata kalamai masu sanyi da zasu kwantar mata da zuciya har saida yaga damuwar dake fuskarta ta gushe daga nan kuma ya karkata akalarsa izuwa muradinsa har saida suka farantawa juna rai sannan ya taimaka mata tayo wanka tashirya, akwatunan tajawo tasake gyara duk abunda take da buqata sannan yafito dasu yasa cikin mota, tana qoqarin fitowa yaja hannunta suka koma cikin d'aki shima ya d'auko wata jikka ya dinga jidar kayansa yana zubawa.
Turo idanuwanta tayi awaje tana dariya tace.
"Abu sumayya ya haka!, Ina zuwa da wannan uwar jikka haka kake ta loda kaya."
"Tab..ai wlh qafarki qafata bazan zauna ba, mezanyi agidan nima can zan koma ai inada nawa d'akin."
Dariya ta dinga yimasa har tana riqe ciki had'e da cewa.
"Ashe ko kaida gwaggo."
"Eh naji dai, amma bazan zauna anan ba ke kina acan sai kace wani mara gata." Yaqarasa maganar yana kulle zip d'in jikkar suka fice tare yanaci gaba da jinini tana dariya.
Satinta uku da komawa gidan Dr wajen Rashida wanda gaba d'aya duk kulawar daya kamata tasamu Rashida nabata wand idan kagani kai karantse kace 'yartace ba suruka ba, yauma kwance take saman gadon bayan sallar magrib Rashida na gefe tana jan carbinta sai kawai taga ta zabura, da sauri ta katse lazumin had'e da miqewa tanu wajenta ganin tariqe kunkuru,
"Batool lafiya?."
"Wash..gwaggo bayana."
"Subhanallahi sannu ko haihuwarce?" Bata tsay jin amsar da zata bata ba da sauri tajawo wayarta takira little sannan tayi cikin gida ta sanar da fatima."
Kan kace me gaba d'ayansu hankalinsu yatashi suka nufi d'akin da sauri, dur qushe suka iskota gefen gado tana yarfi da hannuwa tana cizon baki, ga wani zufa daya tartso mata alokaci d'aya saboda tsananin azabar naquda, ganin haihuwarce zangu zangu yasa Rashida ta d'auko wata qatuwar leda ta shimfid'a mata tare da zane sabo sannan suka kamata ita da fatima suka maida wajen, tun batool na juriya har azabar zafin ciwon naquda tasa tafara kiran abbanta tana fitar da wani iska abaki,
Wani irin tausayinta yarufe Rashida tunawa da irin yanda azabar haihuwa take da tayi, safa da marwa ta shigayi tana karanto addu'o'in da tasani abaki tare da nema mata sauqin rad'ad'in da take ji, bini bini tajuyo tayi mata sannu fatima kuwa tuni tafita taje takirawo Dr, yana zuwa yasa suka riqota suka kaita a mota daidai lokacin little shima ya iso hankalinsa atashe Dr yace yashiga motar ya shiga sannan yaja suka nufi asibiti bayan Rashida takoma ciki ta d'auka kayan da za'a iya buqata.
Ko mintuna ashirin basuyi da Isa ba batool ta samb'alo qatuwar 'yarta kyakkyawa jawur da ita, ho ho zo kaga murna a wajen little ba'a magana don gaba d'aya bakinsa kasa rufuwa yayi musamman da aka fiddo yarinyar daga d'akin haihuwa Dr yamiqa mashi ita, gaba d'aya kamarta sak da batool d'insa babu ta inda tabarota tun daga kan hasken fata har zuwa kamannin fuska.
Kallon Rashida yayi yana dariya yace.
"Gwaggo kinga yarinyar nan gaba d'aya mamanta ta d'auko ko tayimun 'yar kara nima tayi kama dani."
Murmushi kawai Rashida tayi batare data tanka saba tanajin wani irin farinciki marar misaltuwa na mamaye mata zuciya, soqo Fatima tayi masa akai had'e da cewa.
"Lallai little ashe rashin kunyarka har takai haka ban sani ba, bazaka bamu 'yar ba kakame kariqe sai kace wanda za'a qwace mawa sai kamanninta kake fad'a mana."
"Kema dai kyafad'a, bana fad'a maki baida kunya ko kad'an ba kikace a'a, to ai gashi yau kingani da idanuwanki."
Saida yayi mata hud'uba ya rad'a mata sunanta da tunkafin tazo duniya mamanta ta rad'a mata wato (sumayya) sannan yamiqawa Fatima ita yana fad'in.
"ALLAH yaraya mana sumayya." Had'e da gyara mata d'an bargon da aka nad'ota dashi aciki daya d'an rufe mata fuska.
Baki bud'e Rashida ke kallonsa tare da mamakin rashin ta idonsa kafin taji Fatima tace
"Aikam little kabushe fitilarka, ALLAH dai ya shiryaka, in dai wannan narkakkarce badon kar in saketa tafad'i ba ace kishine nakeyi ai dana sakar maka abukka qasa."
"Mama kice dai kinga zata anshe maki Abba shiyasa kikace haka, dama tunda yafito da ita naga yanata kallonta da alama yagama qyasawa."
Taji muryar abbaty daya biyo bayansu yafad'a yana wasar baki shima, hannu yaba little suka tafe had'e da cewa.
"Congrat real Abu sumayya, ubangiji ALLAH yaraya mana."
"Amin" duk suka fad'a kafin dady yasake dawowa ya fad'a masu cewa batool na buqatar jini sai an qara mata don jininta yayi qasa, nan take suka nufi lab shi dasu abbaty da little cikin sa'a kuwa ana auna na little yazo daidai da nata aka d'ibi leda d'aya aka qara mata,
Sosai batool tasamu sauqi don anata fira da ita 'yan uwa da abokanan arziqi dake zuwa dubata, murna awajensu uncle h ba'a magana suda hajia mama da sauran mutanen gida, abbanta ma da aka sanar dashi saida wani annuri ya bayyana a fuskarsa har zaiyi magana sai kuma yayi saurin d'aure fuska yaci gaba da duba jaridarsa batare daya tanka ba, baiso tankawa ba azancen sai kuma yaji ya tsinci kansa da cewa,
"ALLAH yara itama yabata lafiyar shayarwa."
Wannan addu'ar da yayi tasa kowa jin cewa tabbas nan kusa bada jimawa ba zai daina fushi da 'yar tasa kuma yadawo da ita cikin rayuwarsa kamar yanda take ada.