Sashe 135
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kusan mintuna ashirin da wani abu sukayi suna rigima akan wanda zaije cikinsu, shidai baffa Usman ya nace shi zaije don ayanzu bai shirya rasa d'an uwan nasu ba tunda har ya tubarwa laifinsa, shi kuma baya cikin wud'anda haqo asirin zai iya cutarwa kamar yanda bokan yafad'a idan har aka haqo abun shi baffa Ali da matarsa da sukayi asirin su zai koma mawa balle wani abun ya samesa, shi kuma baffa Ali yana ganin tunda har yatuba to dole yayi qoqarin gyara laifukan daya aikata da hannunsa da kansa ko zai samu sassaucin hukuntawa daga ubangiji, ya sani ubangijinsa zai karb'i tubarsa amma haqqin wud'anda ya zalunta dolene sai yayi duk yanda yakamata wajen ganin sun yafe masa kafin ALLAH yabarshi.
Dole badon baffa Usman yaso ba ya haqura ganin yanda ya dage harda kuka, amma ya tabbatar masa dacewa Dole tare zasuje koma inane bazai barshi yaje shi kad'ai ba.
Da sauri sauri baffa ke tafiya ko gabanshi ma baya gani saboda tsananin b'acin rai har ya isa gida yana fitar da haki d'aid'ai ya samu gefe da tsakar gidan ya fad'i zube kwance yana kuka, gaba d'aya yau yarasa qarfin zuciya da jarumtar da zai iya hana kansa kuka, Babu abunda yake tunanin in banda lafuzzan d'an uwan nasa, ace kimanin kusan shekaru talatin yana fama da damuwar rabuwa da kuma fushi akan d'an nasa tilo duk ta adalilin kaidi da baqin sammun da d'an uwansa na jini uwa d'aya uba d'aya yayi masa, meye rauninsa a matsayinsa na babba agaresa daya cancanci wannan hukuncin?, Meyayi masa aduniya da bai cancanci yafiyarsa ba har sai ya rabasa da d'ansa na tsawon wannan lokaci?, Wace irin kulawace bai bashi ba aduniya daya zab'i jefasa cikin mummunan hali haka?, Haka yayita tambayar kansa yana tsiyayar da hawaye har ya gaji don kansa ya bari.
kallon baba nusaiba da tun shigowarsa taqaraso wajen d'aya zube kwance hankalinta atashe, yanda yake kukan ya tabbatar mata daba abu qarami bane ke damunsa ba, don haka saita d'auko mafifici ta shiga yimasa fiffita batare da race masa uffan ba har sai da taga yasamu natsuwar da zai iya kallonta, murmushi ta sakar masa had'e da cewa.
"Waye ya tab'a mani adilin mai gidana baban nura abban Rashida har ya karya zuciyarsa haka tasashi zubar da qwalla, kayi haquri da yanayin da rayuwa kanzo dashi na farinciki ko akasinsa, kayarda da wanzuwar qaddara mai kyau ko marar kyau agareka, ka amince babu mai yimaka sai ALLAH domin shine kad'ai ke iya sarrafa zukatan bayinsa, shiga damuwarka daidai yake da rushewar dukkanin farincikin gidannan musamman na wacce ke rayuwa bisa walwalarka da kuma farinciki, idan ni nayi maka laifi kayafeni baban nura idan kuma waje akayi maka kayafesu baban Abba amininsa?"
Duk da yana jin wani nauyi a zuciyarsa da kuma wani abu da yazo ya tokare masa amaqoshi hakan bai hana jin tasirin kalamanta azuciyarsa ba da sukasa nan take yaji wani irin sanyi ya mamaye masa ita,
Murmushin ya mayar mata kamar yanda tayi masa had'e da cewa.
"Me zakiyimun aduniya maman nusaiba da zai b'atamun rai har yasani kuka inba alkhairi ba, kin zamo mani haske alokacin da nake cikin duhu, kin kauda mani kad'aita alokacin dana rasa makusantana gaba d'aya, kin zamo sanyi agareni alokacin da zafi yayi mani qawanya tare da qoqarin share mani hawaye ga dukkanin damuwar dake neman durqusar dani, taya kike tunanin duk tarin wud'annan alkhairan da kikayimun zaki iya yin wani laifi da zaisa hawayena sake kwaranya bayansu, aike 'yar aljannah ce in sha ALLAH maman Rashida, ki kwantar da hankalinki damuwata dai irin ta yau da kullumce kamar yanda kika sani."
"Akan Nuraddeen kenan!"
"Sosai kuwa, saidai awannna karon ta tarin nadamar fushin dana d'auka dashi ba bisa haqqinsa ba, wataqilma fushin nawane ya dad'a jefasa cikin halin da har aka samu yin galaba akansa, ya ALLAH ka yafemun kuma ka yaye masa wannan mummunan hali da aka kad'asa aciki."
Yaqarasa maganar wasu zafafan hawayen na sake biyo masa fuska,
"Amin" baba nusaiba tafad'a tana kallon mijin nata da gaba d'aya tsufa yarufes, furfura tako ina ta cika masa fuska ga tarin jijiyoyi da suka taso masa tako Ina suka bayyana ajikinsa, wata 'yar sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke aranta tana maijin tausayinsa, a wannan lokacin yakamata ace yana samun cikakken hutu ne bawai wahala ba, Amma tsabar neman halal d'insa da yake da kuma tarin damuwowi dake cike fal azuciyarsa da mabanbantan qalubalen da yayita fuskanta arayuwa sunsa tsufa yayi saurin bayyanar masa tayanda kallo d'aya zaka yimasa ka d'auka shekarunsa sunfi qarfin gangar jikinsa saboda manyancin da yayi,
Nan baffa yashiga labarta mata abunda kefaruwa, sosai itama bataji dad'in hakan ba amma saboda ta tausasa zuciyar baffa akan d'an uwan nasa tace.
"Ashsha! Gaskiya abun baiyi dad'i ba kam, Amma kayi haquri Kuma ka godewa ALLAH daya kawo qarshen lamarin alokaci d'aya, kaga dai ALLAH ya karb'a maka addu'ar shiriya da kaketa roqawa d'an uwanka sannan kuma zai dawo mana da d'anmu a hannunmu in sha ALLAH don na tabbata Ali yayi nadama kuma tubar gaskiya yayi don haka zai karya koma meye da SANNU SANNU sai kaga hankalin Nuraddeen yadawo gida, kaga kuwa banda godiya babu abunda yakamata kayiwa ALLAH, nufin alkhairansa agaremu yasa ya bayyana mana gaskiyar a fili tafito, da yaso sai yakarb'i rayuwar Ali da matarsa batare da sun sanar da abunda suka aikata ba agaresa kaga kuma shikenan babu yanda zamuyi sai dai mucigaba da haquri har zuwa lokacin da ALLAH yaso karya asirin da kansa, Amma yanzu wannan shiriyar da yayiwa Ali har yatuba ga laifinsa yafad'i abunda suka aikata ita zata haska mana al-amarin sai muga nesa ta matso mana kusa da yardar ALLAH, kayi haquri kayafi d'an uwanka ka jawosa ajiki don yanzu babu abunda yafi buqata sama da haka, shizaisa ya dad'a nadama da kuma dana sani akan abubuwan da suka aikata."
"Maman Rashida nariga da nayi rantsuwa akan babu ni babu shi har sai yaje ya tonikke abunda suka binne shida matarsa, taya zan karya wannan rantsuwar ."
"Haquri zakayi kayafe masa, ai hannunka bazai rub'e ka cire kayada ba, kabari tunda akwai hatsi sai in fiddar maka da kai."
"Maman Rashida.."
"Haba babn nura bansanka da haka ba, kayi afuwa da yafiya ga sabba balle d'an uwanka." Tayi saurin katsesa tana fad'ar hakan cikin sigar rarrashi da ban magana, badon baffa yaso ba ya amince da maganarta saidai ya tabbatar mata da cewa shi bazaiyi kaffara ba kuma bazai fidda kai ba, amma ALLAH yasheda ya yafe masa abunda yayi masa, maganar sulhu tsakaninsu kuwa sai lokacin da suka warware abunda sukayi tukuna, ganin hakan yasa dole itama tahaqura taci gaba salwantar masa da hankali tahanyar dad'ad'an kalamai har saida taga ya sauka daga fushin da yayi kuma yasamu natsuwa sosai sannan tamiqe taje takawo masa ruwan tukunya masu sanyi da abinci yaci yasha ya qoshi ta kaimasa ruwa ban d'aki yayo wanka sannan yanemi waje ya kwanta, ko mintuna uku da kwantawa baiyi ba wani nannauyan bacci yayi awon gaba dashi.
Tare su baffa Usman da baffa Ali suka nufi inda yake tunanin sun binne maganin da aka basu, yawo suka sha sosai amma basu ga wajen ba saboda gaba d'aya anguwar ta canza tunda jiya ba yau ba, kusan yini sukayi suna kaida komo a tsakankanin wajen da baffa Ali ke tunanin sun binne maganin amma ya kasa ganewa don duk anyi gine gine wajen, ko banza shi tun daga ranar da suka binne maganin bai koma zuwa wajenba saidai idan hanya tabiyo dashi ya hango wajen hakan yasa yakasa tantace wajen, wani irin kuka ya fashe dashi had'e da cewa.
"Kaicona nayi asara, na rabe tsakanin d'a da uba kuma na tab'ar da kaina, wayyo ALLAH na nashiga uku bansan meye makomata ba aduniya idan har nakoma ga ALLAH batare da yaron nan yadawo mahaifarsa ba ga mahaifinsa."
Haka yayita sabbatu shikad'ai yana kuka duqe agaban baffa Usman da alokacin wata damuwa ta taso ta lullub'e masa zuciya, ya rasa yanzu ko meye mafitar wannan al_amarin, matsalar sammu kenan, koda za'ayi addu'a to samun warakarsa yana ta allaqane ga karye surqullen da akayi, gashi shida suka aikata b'arnar yakasa gano wajen.
Sunfi mintuna biyar awajen kafin baffa Usman yaduqa ya d'aukowa baffa Ali iccensa(crutch) na qafa da yake dogarawa daya saki lokacin daya durqushe agabansa yana kuka ya miqa masa had'e dasa hannu ya taimaka masa yamiqe shima yana sharar qwalla.
Ji baffa Usman keyi kamar yayita dukansa saboda zafin abunda sukayi amma babu hali dole ya tunda yayi nadama kuma ya tuba, haka suka dawo gida agajiya baffa Usman yawuce shiyarsa Inna Bilkisu takawo masa abinci da ruwa tana yimasa sannu da zuwa, cike da damuwa yace a'a tabari yafara watso ruwa tukana sai yaci abincin shida d'an uwansa.
Shi kuwa baffa Ali zaune yayi bakin rumfa ya aza kansa saman iccen da yake tokarawa (crutch) yana kallon shiyar tasa kaca kaca ba wanda ya gyara asalima Inna ruqayyar bata nan tana wajen yawon baransa, gaba d'aya sai yaji ya muzanta awajen wasu zafafan hawaye nazubo masa afuska, tunani ya shigayi lokacin da yana Alinsa yanda Inna ruqayya ke nan nan dashi sai gashi yau ya rasa madogara, gashi da ransa Amma komai nagidansa yafi qarfinsa, abinci ma sai in Inna ruqayya tabashi shi ko yusuf idan yaje yanemo ya kawo masa, amma ita ko mutuwa zaiyi bata bashi acewarta tunda yasamu damar da zaije yayi bara ataimaka masa amma yaqi to ita kam bazata sake ci dashi ba yana zaunensa gida, haka yayita tunane tunanensa har baffa Usman yafito wanka Inna Bilkisu ta shimfid'a masu tabarma acan zaure takai abincin da ruwa ta ajiye masu had'e da 'yar redion da baffa Usman ke sauraren labaran duniya,
Kallonsa yayi had'e da cewa.
"Ali taso muje muci abinci ko?" Ya d'ago kai ahankali had'e da cewa.
"Naqoshi Usman, ko kad'an bana sha'awar cin komai yanzu."
"To taso muje can ko kuma nazo nakai maka ruwa kaima ka watsa ko karage gajiyar kafin ruqayya tadawo."
Dole badon baffa Usman yaso ba ya haqura ganin yanda ya dage harda kuka, amma ya tabbatar masa dacewa Dole tare zasuje koma inane bazai barshi yaje shi kad'ai ba.
Da sauri sauri baffa ke tafiya ko gabanshi ma baya gani saboda tsananin b'acin rai har ya isa gida yana fitar da haki d'aid'ai ya samu gefe da tsakar gidan ya fad'i zube kwance yana kuka, gaba d'aya yau yarasa qarfin zuciya da jarumtar da zai iya hana kansa kuka, Babu abunda yake tunanin in banda lafuzzan d'an uwan nasa, ace kimanin kusan shekaru talatin yana fama da damuwar rabuwa da kuma fushi akan d'an nasa tilo duk ta adalilin kaidi da baqin sammun da d'an uwansa na jini uwa d'aya uba d'aya yayi masa, meye rauninsa a matsayinsa na babba agaresa daya cancanci wannan hukuncin?, Meyayi masa aduniya da bai cancanci yafiyarsa ba har sai ya rabasa da d'ansa na tsawon wannan lokaci?, Wace irin kulawace bai bashi ba aduniya daya zab'i jefasa cikin mummunan hali haka?, Haka yayita tambayar kansa yana tsiyayar da hawaye har ya gaji don kansa ya bari.
kallon baba nusaiba da tun shigowarsa taqaraso wajen d'aya zube kwance hankalinta atashe, yanda yake kukan ya tabbatar mata daba abu qarami bane ke damunsa ba, don haka saita d'auko mafifici ta shiga yimasa fiffita batare da race masa uffan ba har sai da taga yasamu natsuwar da zai iya kallonta, murmushi ta sakar masa had'e da cewa.
"Waye ya tab'a mani adilin mai gidana baban nura abban Rashida har ya karya zuciyarsa haka tasashi zubar da qwalla, kayi haquri da yanayin da rayuwa kanzo dashi na farinciki ko akasinsa, kayarda da wanzuwar qaddara mai kyau ko marar kyau agareka, ka amince babu mai yimaka sai ALLAH domin shine kad'ai ke iya sarrafa zukatan bayinsa, shiga damuwarka daidai yake da rushewar dukkanin farincikin gidannan musamman na wacce ke rayuwa bisa walwalarka da kuma farinciki, idan ni nayi maka laifi kayafeni baban nura idan kuma waje akayi maka kayafesu baban Abba amininsa?"
Duk da yana jin wani nauyi a zuciyarsa da kuma wani abu da yazo ya tokare masa amaqoshi hakan bai hana jin tasirin kalamanta azuciyarsa ba da sukasa nan take yaji wani irin sanyi ya mamaye masa ita,
Murmushin ya mayar mata kamar yanda tayi masa had'e da cewa.
"Me zakiyimun aduniya maman nusaiba da zai b'atamun rai har yasani kuka inba alkhairi ba, kin zamo mani haske alokacin da nake cikin duhu, kin kauda mani kad'aita alokacin dana rasa makusantana gaba d'aya, kin zamo sanyi agareni alokacin da zafi yayi mani qawanya tare da qoqarin share mani hawaye ga dukkanin damuwar dake neman durqusar dani, taya kike tunanin duk tarin wud'annan alkhairan da kikayimun zaki iya yin wani laifi da zaisa hawayena sake kwaranya bayansu, aike 'yar aljannah ce in sha ALLAH maman Rashida, ki kwantar da hankalinki damuwata dai irin ta yau da kullumce kamar yanda kika sani."
"Akan Nuraddeen kenan!"
"Sosai kuwa, saidai awannna karon ta tarin nadamar fushin dana d'auka dashi ba bisa haqqinsa ba, wataqilma fushin nawane ya dad'a jefasa cikin halin da har aka samu yin galaba akansa, ya ALLAH ka yafemun kuma ka yaye masa wannan mummunan hali da aka kad'asa aciki."
Yaqarasa maganar wasu zafafan hawayen na sake biyo masa fuska,
"Amin" baba nusaiba tafad'a tana kallon mijin nata da gaba d'aya tsufa yarufes, furfura tako ina ta cika masa fuska ga tarin jijiyoyi da suka taso masa tako Ina suka bayyana ajikinsa, wata 'yar sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke aranta tana maijin tausayinsa, a wannan lokacin yakamata ace yana samun cikakken hutu ne bawai wahala ba, Amma tsabar neman halal d'insa da yake da kuma tarin damuwowi dake cike fal azuciyarsa da mabanbantan qalubalen da yayita fuskanta arayuwa sunsa tsufa yayi saurin bayyanar masa tayanda kallo d'aya zaka yimasa ka d'auka shekarunsa sunfi qarfin gangar jikinsa saboda manyancin da yayi,
Nan baffa yashiga labarta mata abunda kefaruwa, sosai itama bataji dad'in hakan ba amma saboda ta tausasa zuciyar baffa akan d'an uwan nasa tace.
"Ashsha! Gaskiya abun baiyi dad'i ba kam, Amma kayi haquri Kuma ka godewa ALLAH daya kawo qarshen lamarin alokaci d'aya, kaga dai ALLAH ya karb'a maka addu'ar shiriya da kaketa roqawa d'an uwanka sannan kuma zai dawo mana da d'anmu a hannunmu in sha ALLAH don na tabbata Ali yayi nadama kuma tubar gaskiya yayi don haka zai karya koma meye da SANNU SANNU sai kaga hankalin Nuraddeen yadawo gida, kaga kuwa banda godiya babu abunda yakamata kayiwa ALLAH, nufin alkhairansa agaremu yasa ya bayyana mana gaskiyar a fili tafito, da yaso sai yakarb'i rayuwar Ali da matarsa batare da sun sanar da abunda suka aikata ba agaresa kaga kuma shikenan babu yanda zamuyi sai dai mucigaba da haquri har zuwa lokacin da ALLAH yaso karya asirin da kansa, Amma yanzu wannan shiriyar da yayiwa Ali har yatuba ga laifinsa yafad'i abunda suka aikata ita zata haska mana al-amarin sai muga nesa ta matso mana kusa da yardar ALLAH, kayi haquri kayafi d'an uwanka ka jawosa ajiki don yanzu babu abunda yafi buqata sama da haka, shizaisa ya dad'a nadama da kuma dana sani akan abubuwan da suka aikata."
"Maman Rashida nariga da nayi rantsuwa akan babu ni babu shi har sai yaje ya tonikke abunda suka binne shida matarsa, taya zan karya wannan rantsuwar ."
"Haquri zakayi kayafe masa, ai hannunka bazai rub'e ka cire kayada ba, kabari tunda akwai hatsi sai in fiddar maka da kai."
"Maman Rashida.."
"Haba babn nura bansanka da haka ba, kayi afuwa da yafiya ga sabba balle d'an uwanka." Tayi saurin katsesa tana fad'ar hakan cikin sigar rarrashi da ban magana, badon baffa yaso ba ya amince da maganarta saidai ya tabbatar mata da cewa shi bazaiyi kaffara ba kuma bazai fidda kai ba, amma ALLAH yasheda ya yafe masa abunda yayi masa, maganar sulhu tsakaninsu kuwa sai lokacin da suka warware abunda sukayi tukuna, ganin hakan yasa dole itama tahaqura taci gaba salwantar masa da hankali tahanyar dad'ad'an kalamai har saida taga ya sauka daga fushin da yayi kuma yasamu natsuwa sosai sannan tamiqe taje takawo masa ruwan tukunya masu sanyi da abinci yaci yasha ya qoshi ta kaimasa ruwa ban d'aki yayo wanka sannan yanemi waje ya kwanta, ko mintuna uku da kwantawa baiyi ba wani nannauyan bacci yayi awon gaba dashi.
Tare su baffa Usman da baffa Ali suka nufi inda yake tunanin sun binne maganin da aka basu, yawo suka sha sosai amma basu ga wajen ba saboda gaba d'aya anguwar ta canza tunda jiya ba yau ba, kusan yini sukayi suna kaida komo a tsakankanin wajen da baffa Ali ke tunanin sun binne maganin amma ya kasa ganewa don duk anyi gine gine wajen, ko banza shi tun daga ranar da suka binne maganin bai koma zuwa wajenba saidai idan hanya tabiyo dashi ya hango wajen hakan yasa yakasa tantace wajen, wani irin kuka ya fashe dashi had'e da cewa.
"Kaicona nayi asara, na rabe tsakanin d'a da uba kuma na tab'ar da kaina, wayyo ALLAH na nashiga uku bansan meye makomata ba aduniya idan har nakoma ga ALLAH batare da yaron nan yadawo mahaifarsa ba ga mahaifinsa."
Haka yayita sabbatu shikad'ai yana kuka duqe agaban baffa Usman da alokacin wata damuwa ta taso ta lullub'e masa zuciya, ya rasa yanzu ko meye mafitar wannan al_amarin, matsalar sammu kenan, koda za'ayi addu'a to samun warakarsa yana ta allaqane ga karye surqullen da akayi, gashi shida suka aikata b'arnar yakasa gano wajen.
Sunfi mintuna biyar awajen kafin baffa Usman yaduqa ya d'aukowa baffa Ali iccensa(crutch) na qafa da yake dogarawa daya saki lokacin daya durqushe agabansa yana kuka ya miqa masa had'e dasa hannu ya taimaka masa yamiqe shima yana sharar qwalla.
Ji baffa Usman keyi kamar yayita dukansa saboda zafin abunda sukayi amma babu hali dole ya tunda yayi nadama kuma ya tuba, haka suka dawo gida agajiya baffa Usman yawuce shiyarsa Inna Bilkisu takawo masa abinci da ruwa tana yimasa sannu da zuwa, cike da damuwa yace a'a tabari yafara watso ruwa tukana sai yaci abincin shida d'an uwansa.
Shi kuwa baffa Ali zaune yayi bakin rumfa ya aza kansa saman iccen da yake tokarawa (crutch) yana kallon shiyar tasa kaca kaca ba wanda ya gyara asalima Inna ruqayyar bata nan tana wajen yawon baransa, gaba d'aya sai yaji ya muzanta awajen wasu zafafan hawaye nazubo masa afuska, tunani ya shigayi lokacin da yana Alinsa yanda Inna ruqayya ke nan nan dashi sai gashi yau ya rasa madogara, gashi da ransa Amma komai nagidansa yafi qarfinsa, abinci ma sai in Inna ruqayya tabashi shi ko yusuf idan yaje yanemo ya kawo masa, amma ita ko mutuwa zaiyi bata bashi acewarta tunda yasamu damar da zaije yayi bara ataimaka masa amma yaqi to ita kam bazata sake ci dashi ba yana zaunensa gida, haka yayita tunane tunanensa har baffa Usman yafito wanka Inna Bilkisu ta shimfid'a masu tabarma acan zaure takai abincin da ruwa ta ajiye masu had'e da 'yar redion da baffa Usman ke sauraren labaran duniya,
Kallonsa yayi had'e da cewa.
"Ali taso muje muci abinci ko?" Ya d'ago kai ahankali had'e da cewa.
"Naqoshi Usman, ko kad'an bana sha'awar cin komai yanzu."
"To taso muje can ko kuma nazo nakai maka ruwa kaima ka watsa ko karage gajiyar kafin ruqayya tadawo."