Sashe 117
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda yafara magana Rashida batace dashi komai ba har saida ya dasa aya sannan tashare qwallan da suka zo mata, aduk lokacin da aka aibanta mata yaro sai taji wani qululu yataso azuciyarta ya tokare mata wuya, zafi da zugin da zuciyarta keyimata kuwa suke saka hawaye saurin kwaranya daga idanuwanta, murmushin qarfin hali tayi wanda saida ta tabbatar yaji sautinsa akunne sannan tace.
"Alhamdulillah daka fad'amun kowane irin mahifine kai batare dana b'ata lokacina wajen fahimtar dakai abunda nake da tabbaci ayanzu cewa bazaka tab'a fahimtarsa ba, sanin kima da darajar mutuntaka yasa nayi yunqurin kiranka don tunatar dakai girman qudura ta ubangiji akan abunda shi yake da iko akansa, amma yanzu nafahimci baka buqatar hakan!, Naji yarona bayada uban kmar yanda kace ko, bayada asali shima, yarona bayada nagarta da kima a idanun duniya musamman ga irinku to duka naji kuma nayarda da hakan, Amma Ina so kasani ayanzu yarona, shine rayuwar 'yarka!, shine kimar gidanka!, shine abun so ga dukkanin nakusa gareka!, yarona shine zab'in fatincikinka da kafi so aranka! Kuma shine wanda take alfahari dashi data jingina wanzuwar rayuwarta bisa samunsa!, Bana buqatar sanin abunda ke faruwa acikin gidanka domin 'yar taka da kake cewa yarona na bibiya tana tare damu, zuciyarta takasa amince mata ta zauna atare dakai saboda gazawarka wajen sama mata farinciki, hakan yasa tazo garemu cike da so da qauna kuma mun karb'eta hannu biyu dommu nuna mata yanda rashin uba ke iya samar da gata fiye da masu uba."
"Ka kwantar da hankalinka babu abunda zai sami 'yarka don nafahimci karazana da jin hakan, izuwa yanzu 'yarka na gab da isowa wajenka domin nasa yarona ya maido maka da ita, koba komai wannan inganci nasa da nagartarsa da duniya takasa ganewa kai ka ganota, sannan kasa aranka kausasan kalamanka basu isa susa infad'a maka waye ubansa idan har baka sani ba ko in rabasa da 'yarka domin nasan ko banyi hakan ba ina da tabbacin soyayyar da 'yarka keyi masa kawai ta isa tasa d'ana yayi nasara akanka wajen aure 'yarka, yawwa! Sannan naji kamar kace zaka nusar dashi kuskurensa ko? To Ina jiran hakan domin idan ka kuskura kayiwa d'ana wani abun ko kuma yadawo naga qwarzane ajikinsa to tabbas zan manta da cewa ni uwace in d'auko tsofaffin kayan da suka dad'e ajiye nasa don bimasa haqqinsa, Kuma Ina tabbata maka cewa idan nafara shari'a dakai bazan bari ba har sai na tabbatar da nima na nuna maka kuskurenka natab'a mun d'a da kayi, saboda haka kada kafasa ga fili ga mai doki, ni na barka lafiya."
Takashe wayarta tun kafin yayi qoqarin cewa wani abun zuciyarta fal cike da farincikin ta mayar masa da baqaqen maganganun daya yimata daidai shi.
Wani irin qugi Abba yayi tare da ture dispenser d'in dake gefensa a kan fridge yana mai jin d'acin kowace kalma d'aya da Rashida ta mayar masa, wanda ya ta'allaqa hakan da walaqanci da kuma cin zarafi da 'yarsa ta cikinsa tajawo masa takowane b'angare.
Qarar motar daya jiyo daga wajen gate ya sashi saurin fita tsakar harabar gidan yana huci ya d'auka su d'inne suka iso kamar yanda Rashida tafad'a, sai gashi ashe su uncle h ne suka dawo daga wajen nemanta agajiye rayukkansu duk ba dad'i saboda babu wani labari da suka samo akanta, har hajia nafeesa sun kirawo acan borno suji ko batool d'in taje can amma saboda batada wata masaniya akan zuwan nata yasa tace masu bata ganeta ba.
Har ya juya zai komawa ciki ya hango mota na kunno kai cikin gidan da sauri yadawo yanufi wajen motar tamkar wani zararre, hannu batool ta shiga yarfawa hawaye nazubo mata a fuska hango mahaifin nata da tayi ya tunkaro wajen motar tasu, sudai su Uncle h zura idanuwa sukayi suna jiran fitowar wanda ke cikin motar, qafar macce da suka gani tafara azowa lokacin da suka bud'e gambunan motar yasasu saurin qarasowa wajen motar suma, batool na ganinsu da sauri taqarasa fitowa jikinta narawa tanufi inda suke tana fad'in.
"Nashiga uku, uncle don ALLAH kuyi haquri ku yafemun kada kubari Abbana ya dukeni, wlh Abba natuba bazan qara guduwa ba..bayansu ta b'uya tana kallon idanuwa abban nata da sukankad'a sukayi jawur kamar an watsa masa barkono, cikin fushi yanufi wajen da little yake tsaye yariqe gambun mota shi bai qarasa fitowa ba shi baikoma ciki ba yana kallonsu uncle h da suka juya suna kallonta cike da mamaki.
Wata irin cakuma Abba yayiwa little had'e da shaqo wuyan rigarsa ya had'asa da jikin motar tasa yana fad'in.
"Kai d'an gidan uban waye da zaka d'aukemun 'yah?, ubanme kaje kayimata ana saura kwanaki a d'aura mata aure?, Kafad'amun uban me kaje ka aikata mata?"
Yanda yake kakari yasa batool rugowa tariqe masa qafa tana fadin.
"Abba ka qyalesa, don ALLAH aba karabu dashi, ba abunda yayi mani asalima ninaje na iskosa har gidansu, Abba naroqeka kabarshi kada kacutar dashi don ALLAH."
Ko kad'an little baiyi yunqurin kwatar kansa ahannun abba ba saboda kada yace yayi kokuwa dashi duk kuwa da azabar da yakeji Kuma bawai bayada qarfin bane kawai ya shiraya rayuwa ko mutuwane akan masoyiyarsa.
Yanda batool takoma qoqarin cire hannunsa ga wuyan little tana kuka yasa Abba sakinsa tare da riqo hannunta ya d'auketa wani irin zazzafan marin da saida takife wajen asume, da gudu little yayi kanta yana kiran sunanta had'e da cewa.
"Kada ki karaya batool, wannan shine qalubalen da soyayyarmu tazo mana da ita, don ALLAH kitashi kada kibari wani abun ya sameki, bazan juri hakan ba, batool batool tun yana qeqqegar tab'ata har yasoma aza hannunsa akafad'arta yana jijjigata, a fusace Abba yasake yowa takansa ya shuresa gefe amma hakan bai hana little tasowa ba yana kuka yana kiran sunanta, qafa Abba ya d'aga zai sake shuresa uncle Hussain yazo ya jayesa yana fad'in.
"Ta b'angaren sa ya isa haka domin idan ma laifi yayi na d'aukarta kacire wannan rad'ad'in azuciyarka, ayanzu bakada hurumin sake tab'asa sai dai ko 'yar taka gatanan agabanka zaka iya qarasata idan kana buqata,"
Yana gama fad'ar haka ya juyawarsa riqe da hannun little ya shige part d'insa dashi, shi kuma sai waiwayen batool daya hango uncle Hassan na yayyafa mata ruwa yakeyi yana sharar hawaye,
Tana farfad'owa tafara waige waige tare da nufar art d'insu tana kuka ahankali tana kiran sunansa,
Karki kuskura qafafuwanki sutaka mani cikin gida domin ya haramta daga gareki, yanda kika fita kika barsa Ina so ki kama qafafuwanki kifice daga cikin gidannan kafin nacireki daga cikin 'ya'yana, tunda har kikasa aka ci mutuncina kika zubarmun da kima a idanuwan duniya kikasa 'yan uwana suka juyamani baya to nima daga yau babuni babu ke, kije can kinemi wasu iyayen da suka fimu Amma mu bama buqatarki,
"Madalla daka fad'i hakan, idan har kai baka buqatarta to mu muna buqatarta, gida kuwa tanada ikon ta zauna tunda tana damu, batool share hawayenki in Sha ALLAH daga yau sun dena zubowa, idan har shi yayi maki gata kina qaramarki to mu zamuyi maki ita ayanzu da kike da girmanki tahanyar aura maki wanda kike so"
Uncle Hassan yafad'i hakan tare da riqo hannun batool yawuce part d'in uncle Hussain da ita shi kuma Abba yawuce fuuuuu..zuwa nasa part d'in....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___85💎
Duk iya qoqarin su uncle h wajen ganin sun fahimtar dashi hakan ya cutara don gaba d'aya ida birkice masu ma yayi tamkar wata birkitacciyar kaca, shiru duk sukayi suna sauraren yanda take masifa yana qarawa har yayi mai isarsa yagama sannan suka miqe rayukkansu a 'bace sukabar wajen.
••• ••• •••
Dady kuwa tunda suka koma shima ya canzawa hajia nafeesa, gaba d'aya baya shiga al-amurranta saboda yanda ransa yab'aci, ya tabbatar babu wanda ya shiryawa mahaifin batool wannan qullalliyar ta cewa little bayada uba sai ita wanda hakan baiyi masa dad'i ba ko kad'an, shiyasa ya d'auki fushi da ita don ya nuna mata kuskurenta, amaimakon ta fahimta sai itama ta sharesa tafita batunsa kamar yanda yake yimata, Saida taji tagaji don kanta sannan yau daya shigo part d'inta da daddare don ya duba yaransa saboda a part d'in ammie yake ta tsaresa akan lallai sai yafad'a mata dalilin da yasa yake fushi da ita har na tsawon sati biyu.
Waje yanema ya zauna fuskarsa a d'aure babu alamun walwala atattare da ita sannan yace
"Meye dalilinki na shegantawa Rashida d'ah da kuma shiga rayuwarsu?, meye yadameki da zuwam mu nemawa yaronsu auren da kikaje kika fad'i maganganun da zasu iya lalata komai?"
Wani irin sheqeqe ta d'ago takallesa had'e da cewa.
"Au dama akan wannan kake fushi dani?, Tirqashi! Ai wallahi da nasan akan wannanne dalilinka da ko kallonka bazanyi ba balle har indamu da fushin da kakeyi, Kuma da kake zancen shiga rayuwa dani dasu waya shiga rayuwar wani?, meye alaqarsu dakai da har zaka tambayeni zance sheganta yaronsu, yo ina uban nasa yakene da har don na shegantasa zakaga laifina?, Ina ganinsu kawai mukyi dashi tsakar rana shida da uwarsa da suka gudo ita da kakannisa batare da munga ubansa ba?, To don me an tambayeni bazan fad'i gaskiya ba?, Kama ajiye duk wannan agefe, kai kasan dolene ma nab'ata wannan auren tunda aka munafucceni akan za'a nemowa d'ana yarinyar sai akaje aka nemawa wanda ba'asan asalin saba saboda bid'ar suna, kaga kuwa koba komai yanda natsani kakarsa wlh in akwai abunda yafi lalata aure zan iyayi masu don bazan bari muhad'a jini dasu ba balle ace sunyi nasara akaina?."
"Haka kikace!?"
"Eh haka nace, nafad'a kuma naqara fad'a, indai ina raye wlh bazan bari wannan yaron ya auri 'yar uwata ba!."
"Alhamdulillah daka fad'amun kowane irin mahifine kai batare dana b'ata lokacina wajen fahimtar dakai abunda nake da tabbaci ayanzu cewa bazaka tab'a fahimtarsa ba, sanin kima da darajar mutuntaka yasa nayi yunqurin kiranka don tunatar dakai girman qudura ta ubangiji akan abunda shi yake da iko akansa, amma yanzu nafahimci baka buqatar hakan!, Naji yarona bayada uban kmar yanda kace ko, bayada asali shima, yarona bayada nagarta da kima a idanun duniya musamman ga irinku to duka naji kuma nayarda da hakan, Amma Ina so kasani ayanzu yarona, shine rayuwar 'yarka!, shine kimar gidanka!, shine abun so ga dukkanin nakusa gareka!, yarona shine zab'in fatincikinka da kafi so aranka! Kuma shine wanda take alfahari dashi data jingina wanzuwar rayuwarta bisa samunsa!, Bana buqatar sanin abunda ke faruwa acikin gidanka domin 'yar taka da kake cewa yarona na bibiya tana tare damu, zuciyarta takasa amince mata ta zauna atare dakai saboda gazawarka wajen sama mata farinciki, hakan yasa tazo garemu cike da so da qauna kuma mun karb'eta hannu biyu dommu nuna mata yanda rashin uba ke iya samar da gata fiye da masu uba."
"Ka kwantar da hankalinka babu abunda zai sami 'yarka don nafahimci karazana da jin hakan, izuwa yanzu 'yarka na gab da isowa wajenka domin nasa yarona ya maido maka da ita, koba komai wannan inganci nasa da nagartarsa da duniya takasa ganewa kai ka ganota, sannan kasa aranka kausasan kalamanka basu isa susa infad'a maka waye ubansa idan har baka sani ba ko in rabasa da 'yarka domin nasan ko banyi hakan ba ina da tabbacin soyayyar da 'yarka keyi masa kawai ta isa tasa d'ana yayi nasara akanka wajen aure 'yarka, yawwa! Sannan naji kamar kace zaka nusar dashi kuskurensa ko? To Ina jiran hakan domin idan ka kuskura kayiwa d'ana wani abun ko kuma yadawo naga qwarzane ajikinsa to tabbas zan manta da cewa ni uwace in d'auko tsofaffin kayan da suka dad'e ajiye nasa don bimasa haqqinsa, Kuma Ina tabbata maka cewa idan nafara shari'a dakai bazan bari ba har sai na tabbatar da nima na nuna maka kuskurenka natab'a mun d'a da kayi, saboda haka kada kafasa ga fili ga mai doki, ni na barka lafiya."
Takashe wayarta tun kafin yayi qoqarin cewa wani abun zuciyarta fal cike da farincikin ta mayar masa da baqaqen maganganun daya yimata daidai shi.
Wani irin qugi Abba yayi tare da ture dispenser d'in dake gefensa a kan fridge yana mai jin d'acin kowace kalma d'aya da Rashida ta mayar masa, wanda ya ta'allaqa hakan da walaqanci da kuma cin zarafi da 'yarsa ta cikinsa tajawo masa takowane b'angare.
Qarar motar daya jiyo daga wajen gate ya sashi saurin fita tsakar harabar gidan yana huci ya d'auka su d'inne suka iso kamar yanda Rashida tafad'a, sai gashi ashe su uncle h ne suka dawo daga wajen nemanta agajiye rayukkansu duk ba dad'i saboda babu wani labari da suka samo akanta, har hajia nafeesa sun kirawo acan borno suji ko batool d'in taje can amma saboda batada wata masaniya akan zuwan nata yasa tace masu bata ganeta ba.
Har ya juya zai komawa ciki ya hango mota na kunno kai cikin gidan da sauri yadawo yanufi wajen motar tamkar wani zararre, hannu batool ta shiga yarfawa hawaye nazubo mata a fuska hango mahaifin nata da tayi ya tunkaro wajen motar tasu, sudai su Uncle h zura idanuwa sukayi suna jiran fitowar wanda ke cikin motar, qafar macce da suka gani tafara azowa lokacin da suka bud'e gambunan motar yasasu saurin qarasowa wajen motar suma, batool na ganinsu da sauri taqarasa fitowa jikinta narawa tanufi inda suke tana fad'in.
"Nashiga uku, uncle don ALLAH kuyi haquri ku yafemun kada kubari Abbana ya dukeni, wlh Abba natuba bazan qara guduwa ba..bayansu ta b'uya tana kallon idanuwa abban nata da sukankad'a sukayi jawur kamar an watsa masa barkono, cikin fushi yanufi wajen da little yake tsaye yariqe gambun mota shi bai qarasa fitowa ba shi baikoma ciki ba yana kallonsu uncle h da suka juya suna kallonta cike da mamaki.
Wata irin cakuma Abba yayiwa little had'e da shaqo wuyan rigarsa ya had'asa da jikin motar tasa yana fad'in.
"Kai d'an gidan uban waye da zaka d'aukemun 'yah?, ubanme kaje kayimata ana saura kwanaki a d'aura mata aure?, Kafad'amun uban me kaje ka aikata mata?"
Yanda yake kakari yasa batool rugowa tariqe masa qafa tana fadin.
"Abba ka qyalesa, don ALLAH aba karabu dashi, ba abunda yayi mani asalima ninaje na iskosa har gidansu, Abba naroqeka kabarshi kada kacutar dashi don ALLAH."
Ko kad'an little baiyi yunqurin kwatar kansa ahannun abba ba saboda kada yace yayi kokuwa dashi duk kuwa da azabar da yakeji Kuma bawai bayada qarfin bane kawai ya shiraya rayuwa ko mutuwane akan masoyiyarsa.
Yanda batool takoma qoqarin cire hannunsa ga wuyan little tana kuka yasa Abba sakinsa tare da riqo hannunta ya d'auketa wani irin zazzafan marin da saida takife wajen asume, da gudu little yayi kanta yana kiran sunanta had'e da cewa.
"Kada ki karaya batool, wannan shine qalubalen da soyayyarmu tazo mana da ita, don ALLAH kitashi kada kibari wani abun ya sameki, bazan juri hakan ba, batool batool tun yana qeqqegar tab'ata har yasoma aza hannunsa akafad'arta yana jijjigata, a fusace Abba yasake yowa takansa ya shuresa gefe amma hakan bai hana little tasowa ba yana kuka yana kiran sunanta, qafa Abba ya d'aga zai sake shuresa uncle Hussain yazo ya jayesa yana fad'in.
"Ta b'angaren sa ya isa haka domin idan ma laifi yayi na d'aukarta kacire wannan rad'ad'in azuciyarka, ayanzu bakada hurumin sake tab'asa sai dai ko 'yar taka gatanan agabanka zaka iya qarasata idan kana buqata,"
Yana gama fad'ar haka ya juyawarsa riqe da hannun little ya shige part d'insa dashi, shi kuma sai waiwayen batool daya hango uncle Hassan na yayyafa mata ruwa yakeyi yana sharar hawaye,
Tana farfad'owa tafara waige waige tare da nufar art d'insu tana kuka ahankali tana kiran sunansa,
Karki kuskura qafafuwanki sutaka mani cikin gida domin ya haramta daga gareki, yanda kika fita kika barsa Ina so ki kama qafafuwanki kifice daga cikin gidannan kafin nacireki daga cikin 'ya'yana, tunda har kikasa aka ci mutuncina kika zubarmun da kima a idanuwan duniya kikasa 'yan uwana suka juyamani baya to nima daga yau babuni babu ke, kije can kinemi wasu iyayen da suka fimu Amma mu bama buqatarki,
"Madalla daka fad'i hakan, idan har kai baka buqatarta to mu muna buqatarta, gida kuwa tanada ikon ta zauna tunda tana damu, batool share hawayenki in Sha ALLAH daga yau sun dena zubowa, idan har shi yayi maki gata kina qaramarki to mu zamuyi maki ita ayanzu da kike da girmanki tahanyar aura maki wanda kike so"
Uncle Hassan yafad'i hakan tare da riqo hannun batool yawuce part d'in uncle Hussain da ita shi kuma Abba yawuce fuuuuu..zuwa nasa part d'in....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___85💎
Duk iya qoqarin su uncle h wajen ganin sun fahimtar dashi hakan ya cutara don gaba d'aya ida birkice masu ma yayi tamkar wata birkitacciyar kaca, shiru duk sukayi suna sauraren yanda take masifa yana qarawa har yayi mai isarsa yagama sannan suka miqe rayukkansu a 'bace sukabar wajen.
••• ••• •••
Dady kuwa tunda suka koma shima ya canzawa hajia nafeesa, gaba d'aya baya shiga al-amurranta saboda yanda ransa yab'aci, ya tabbatar babu wanda ya shiryawa mahaifin batool wannan qullalliyar ta cewa little bayada uba sai ita wanda hakan baiyi masa dad'i ba ko kad'an, shiyasa ya d'auki fushi da ita don ya nuna mata kuskurenta, amaimakon ta fahimta sai itama ta sharesa tafita batunsa kamar yanda yake yimata, Saida taji tagaji don kanta sannan yau daya shigo part d'inta da daddare don ya duba yaransa saboda a part d'in ammie yake ta tsaresa akan lallai sai yafad'a mata dalilin da yasa yake fushi da ita har na tsawon sati biyu.
Waje yanema ya zauna fuskarsa a d'aure babu alamun walwala atattare da ita sannan yace
"Meye dalilinki na shegantawa Rashida d'ah da kuma shiga rayuwarsu?, meye yadameki da zuwam mu nemawa yaronsu auren da kikaje kika fad'i maganganun da zasu iya lalata komai?"
Wani irin sheqeqe ta d'ago takallesa had'e da cewa.
"Au dama akan wannan kake fushi dani?, Tirqashi! Ai wallahi da nasan akan wannanne dalilinka da ko kallonka bazanyi ba balle har indamu da fushin da kakeyi, Kuma da kake zancen shiga rayuwa dani dasu waya shiga rayuwar wani?, meye alaqarsu dakai da har zaka tambayeni zance sheganta yaronsu, yo ina uban nasa yakene da har don na shegantasa zakaga laifina?, Ina ganinsu kawai mukyi dashi tsakar rana shida da uwarsa da suka gudo ita da kakannisa batare da munga ubansa ba?, To don me an tambayeni bazan fad'i gaskiya ba?, Kama ajiye duk wannan agefe, kai kasan dolene ma nab'ata wannan auren tunda aka munafucceni akan za'a nemowa d'ana yarinyar sai akaje aka nemawa wanda ba'asan asalin saba saboda bid'ar suna, kaga kuwa koba komai yanda natsani kakarsa wlh in akwai abunda yafi lalata aure zan iyayi masu don bazan bari muhad'a jini dasu ba balle ace sunyi nasara akaina?."
"Haka kikace!?"
"Eh haka nace, nafad'a kuma naqara fad'a, indai ina raye wlh bazan bari wannan yaron ya auri 'yar uwata ba!."