← Book details Kishiyar Kabila Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 157

Sashe 45

Kishiyar Kabila Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hakan sosai yy masa dadi aransa dan its alwys feels insulting to him musammn inya shiga gidan ya kalle kafayat tare da babansu, aganin sa gara ace bata wani zama tare da su din zaifi musu mutunci da samun kwanciyar hankli.

Zama sukayi awajen suna hira mai cike da shakuwa da fahimtar juna sunata dariya zaka iya rantsewa da cewa itace ta haife sa, har sai can da brother hamzat ya taho wajen shima ya same su suka cigaba da zuba mata labarin ayyukansu suna ta dariya.

sunkai past 10 na dare suna hirarrikin rayuwa kafin nan tace zata wuce room dinta ta dan huta dan gobene zataje final interview dinta a abuja bayan shi kuma zata jira date of resumption snn ta tafi ga kuma tafiyar zainab gobe dolene ta tsaya tay mata sallama da sassafe kafin ta tafi

Dukansu sun ji matukar dadi aransu da ta kawo wann babban cigaban na komawa kan aikin gwamnati a rayuwarta.

Dan awajensu tamkar wani hanya ta samo na kare musu mutuncinsu dan zamanta tare da kafayat agidan a matsayin kishiyoyi har yau lamari ne dayake ci musu tuwo a kwarya .

They all agree dat bazasu gayawa Ahmed komi ba harsai an kammala shirya komi dan sun san yadda yake matukar son mamanshi yanzu shima zai fara tunanin yin jigila a hanyar lagos kowani lokaci da sunan yana zuwa wajenta hutu.

Itakanta tunani take na yadda zata soma gaya ma dan nata musammn ma datake son ta daura masa wani nauyi shi da matarsa Adiaha.

Ta lura kamr Adiaha bata da wani matsala Aranta ta riga ta yanke cewa idan har yar uwansa YASRAH ta dawo nigeria shine zai zamo cikakken guardin dinta anan Abuja msmn ma inta fara Attending din babban makaranta....
[6/15, 8:56 PM] SURAYYAHMS: Wajajen karfe sha daya na dare saura suka rabu da y'ay'an nata bayan sun kammala yar hirarsu nan kowa ya shigeciki domin yin bacci.
A fannin Alhaj bello kuwa yasha matukar mamaki daya koma bangarensa ya tararda kafayat tana kwance shame shame akan makaken gadonsa ta tura baki cikin sakin yatsine ayayin da take latsa wayarta hankli kwance.

Sallama yay mata batako daga ido ta kalleshi bare ta amsashi ba.

Jikinshi harna rawa ya iso gareta,wani irin kallonta yakeyi tun kafin nan ta hankara har ya jawota jikinsa wani irin rungumar daya sakar mata kamar na wanda za'a kwace mishi ita saida ya sakata cikin jin matsanancin mamakin sa dan har wani sauke ajiyar zuciya yakeyi kamar wanda ya jima yana nemanta bai sameta ba.

Duk aransa gani yake kamar itace dagaskiya anata cutar da itane sabida tsabar kishi da bakin hali.duk sanda ya tuno da abunda malamin nan ya gaya masa akan matarsa hjy khadijatu baya iya hadiye wann bakincikin Jin cewa hjya khadijat itace ke shiga tsakaninsa da kafayat snn itace ta rabashi da yaransa na cikinsa tsabar baqar kishi da mugunta.

Gabaki daya kafayat bata fahimce emotional state dinsan ba,sai shishigewa jikinta take yanamai bata hakuri yanamai ce mata shima baisan abunda yake yawan shiga tsakaninsu da har yake iya barinta tay yaji ta koma gida ba..

Tun daga ranar auren daurin auren su har izuwa yanzu ta tafi gidansu da fushi yafi sau akirga. Hakuri kawai yake bata batare da fayyace mata komi ba, duk mamakinsa ya cikata duk dama hakan kusan wani babban damane agareta amma ba hakan bane ya hanata cizga masa buhun rashin mutunci cikin izgili da walakanci take ce masa bazata yafewa walakncin dayake mata agidan ba.

Tace masa y'ay'an sa kaff sun rainata, snn shikansa duk sanda yaga matarsa jikinshi rawa yake daga nan kuma dolene tasha walakanci a hannunsa...

Tayi ta masa bori, Yau kam hakuri ya dinga bata duk aganinsa ba laifinta bane yasa take masa irin wann rashin kunyar sharrin sihirin matarsa khadijat ne da kyar ya lallabeta sukayi bacci.

Acikin baccin ma Tana ta masa borin karya Duk ta hanashi ya taɓata hakanan ya kwana da idanunsa a bude cikin tunani, washe gari da sassafe ta farka akan gabar mission dinta, ko kyaleshi yaje yay sallah batayi ba tafara janshi cikin wani irin salon romance bayan sunyi first round tafara yi kamr karfinta ya kare ficewa tay taje ta debo madara wanda already ta jikashi sosai da ruwan magani dan tun jiyan ta jikashi abisa umarnin goddess dan ta riga tace mata idan maganin ya jika sosai acikin madara toh tasirinsa zaifi dadewa ajikinshi yana aiki basai tasha wahala ba.

Madarar ta dauko kafin ta dawodakin tanashan nata wanda babu komi aciki acikin kwalin madarar, shikuma tazo da nashi a glass cup ta basa tare da tursasa masa yasha, tass tasaka shi ya shanye ganin baison ya kara bata mata ranta, tun bayan nan sai bai kara gane kansa ba.

Tunda suka koma wa junansu ya dingajin kansa na juyawa kamar baya duniya haka yake ta kallonta dishi dishi tamkar wanda giya yasha ya bugu sosai baya hayyacinshi

yana kanta yana aiki tana enchanting soul dinsa da wasu sirrikan dake fita daga bakinta duk sai da ta janye kurwanshi ta miƙawa goddesss batare da sanninsa ba, Bai tashi
Sauka akanta ba har sai wajajen karfe 8.30am yay na safiya shikansa yau yaji jiki da kyar ya dawo hayyacinshi Kafin nan ya tuno da cewa baiyi sallan safiya ba...kafayat kuwa mutuwa ne kawai baza ace tayi ba dan ko iya hade cinyoyinta bata yi sabida tsawon lokcin da suka dauka suna abu daya, yauma a wawware ta kwanta rigib inda wani wahalallen bacci yay awon gaba da ita.

Wanka yay bayan ya idar da sallah snn ya saka sabon jumfarsa na wata yadin shadda fara kal da hula ya nufi dakin hjy khadijatu cikin bacin rai.

Tun da ya doso hanyar yakejin tsananin bacin rai ya rasa menene yasaka yakejin kamar zai iya kasheta ma dan tsananin haushi.

Bai lura da cewa lokaci yaja sosai ba har saida ya taɓa yaji kofar dakinta a kulle,hakanan ya sauko
Kasa cikin jin takaaici jin gidan ya dauƙa da wani irin shiru tamkar babu kowa aciki.

Kafin kafayat ta farfado ta farka yunwan yabi ya ishesa nan ya fice neman abinci agidan su anty mojushola, yana isa ko zama baiyi a gidan ba saiga kirar sister zainab a waya, nan suka gaisa snn tay masa sallama tace masa karfe goma da rabi jirginsu zai tashi.

Addua yaso yay mata amma koda yaji cewa tana tare da hjy khadijatu a dede lokcin sai yaji zuciyarsa yana harbawa da fushi duk ransa ya lalace sosai kawai yace mata inta isa ta nemeshi.

Duk son dayake ma yarsa zainab haka yau yay zuciya da ita Basuyi wani dogon sallama ba ya katse wayar yacigaba da jimamin baqqinciki najin cewa khadijatu ta asirce masa yaransa.

Adiaha ce kadai a gidan taci kwaras ta fito falonta tana rubuta iya abubuwan da ranta yake so, yau banda lissafin yadda zata fitowa Ahmed da maganan business dinta babu abunda takeyi agidan tunda ya fita don itama so take ta fito tana haskawa kamar kowacce mata musammn ma danta koyawasu anty nurat hankli.

Yau da wuri Ahmed ya fice aiki wanda yasaka bata samu daman yin wata magana mai tsayi dashi ba, dama inba wknds ba shi bai fiye samun lokacin kanshi hakann kawai ba gashi ba son dawowa da wuri sai can dare irin after ishai ko harma karfe tara izuwa goma snn yakan iya ficewa akowani lokci idan aikinsa ya taso.

8:00am Dr hassan's hospital maitama

Wuraren 8 na safe Ahmed ya fito daga cikin wani confrence hall yana takawa izuwa cikin office dinshi sanye yake da black trouser yau normal wandon jean yasa saidai ya dame wandon yasa blue long sleeve shirt da kake iya hango shatin agogon sa dake kyalli a wuyar hannunshi shi yay tucking yakawo belt mai kyau da tsada yasa, yasa black cover shoe dake shining na zuwa aiki ya shigo yana kokarin gyara tie din wuyarshi hanunshi daya kuma rike da white ironed lab coat dinshi sai kamshi yake looking very cooperate, fatarshi har wani glowing yake sabida gyrar data sha ga gashin kanshi da sajen shi sun kwanta lub lub

Shigowarsa ciki ya samu Abokinshi banji ne kadai azaune akan kujera ga cofee nan agabanshi anjera kala kala. Ahnkli yay sallama yana mai Tabe baki cikin neman tsokana yace "D'Banj"ya mika masa hannu suka dan gaisa dan tun da ya shigo yake kallonshi baiko ansa shi ba yanata mamakin yadda Ahmed ya dawo kamr bashi ba

Zama yayi kafin nan yadau cup din coffee dake gaban banjin sanin ba ya son rainin hankli amma sai yakai bakin sa yasha coffen son ransa kafun ya aje masa sauran yanamai sauke ajiyar zuciya.

Banji ya watsa masa harara dan iska ince Sai yanzu ka ga daman kulani?

Dariya yay dn So yake lallai sai ya kular dashi aikuwayana budan baki yayi sauri Yace heys i admit im wrong, dalla tafi chan sei shegen zuciya kamr kuturu, bakasan meya faru bane da jiya na ajiyeka kanata jirana,

Banji yace banason naji bayan kasa na baata lkci na ina jiranka agidan kallon ball U still off ur phone on me.

Yace am really soryy wallh bacci ne ya kwasheni a gidan, nagaji, dat girl was oll over me, she is just a bug batama kyaleni nasha iska. Bansan ko sauran maza ba but am not really excited about being married yet..i want sumtin more challenging inason babe mai aji da fitinan shan qamshi, i want to be a king but Not sooo kinging...inka ga yadda aka maidani baby agidan ko?

Kasa cewa komai banji yay ya tsaya gum yana kallon bakinsa a gumshe da dariyar takaici, Ahmed kace matar ka is a bug?? tun bai amsa ba ya karayin dariyan wai meyasa kake cewa hakane yaushe xaka dena wannan dabian naka ne, ure a grown up man...damn it.
Chapter 45 · 0% Book details