← Book details Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 144

Sashe 8

Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da haka dai suka rabu tana jiran kiransa ita kuma Mama Zuwaira jiran zuwan yayan nasu suke wanda ya zame musu kamar Uba da uwa yaya Sunusi domin ayi wacce za"ayi yau su da su iya Tunda basu san mutumci ba.
*Littafin Saifuddeen na kudi ne pay N500 via 0552179550 Jamila umar Gt bank,sai a turo evidence of payment ta wannan Lambar 09069067488 ko kuma katin waya na Mtn sai adauki Hoton katin a tura ta wannan Layin kai Tsaye 09069067488 mutanen mu na Niger kuma zasu tuntubi Kausar aglan Nissa ta wannan lambar domin karin bayani +22796562223 Ina maraba da masoya na a duk inda suke*
*Janafty*
*SAIFUDDEEN*
_(Ba mutum ba ne)_
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
_Ga wadan'da ke amfani da Wattpad su yi following din Anty Habiba Iman ikra domin samun Labaranta masu Dadi da Ma'ana akan@habibaiman1986_
*Amnaf_sudanese _collection*
*Tana saida original laffaya kala daban daban daga Sudan kama daga na Amare da Kuma casual muna da available a Nigeria kuma Muna aikawa daga Sudan Zuwa Nigeria ko'ina a fadin Jahohi talatin da shida har ila yau dai akwai humra da turarrukka sadidan na matan aure daga Sudan,ba fa anan kada'i muka tsaya ba Muna saida kayan lalle akan sari da Rahusa da kuma siyan Daya,akwai mayuka da dilka da kayan gyaran jiki na ainahin ba Mix ba, wadan'da zasu fitar Miki da fatar ki tas ba bleaching fuskarki tayi haske tayi walwal kina kyalkyali and duk abunda kikeso a Sudan Muna kawo Miki shi har gda Nigeria Amnaf Sudanese collaction ba abunda bama saidawa kama daga kayan kamshin jiki na kaya da na fata +249923097401*
misalin wajen biyu saura na Rana bayan Azahar sannan Ya sunusi ya iso Shi da D'ansa Isma"il da Inna iyami data kasance kamar uwa a wajensu saboda da Wanda ya Haifi mahaifinsu da ita ubansu Daya shiyasa bayan dawowarsu gaya da zama Kawu sunusi ya Daukota suna zaune tare tunda duk yan"uwan sunkare sai wadanda ba"a rasa ba.

Su iya suna nan basu jirka daga inda suke ba har gwara ma Baffa Hashimu sun je sun yi sallah sun dawo kafin isowar su Ya sunusin..

Koda suka iso Su Ummi suna cikin bedroom basu sake lekowa ba sai da sukaji Tashin muryan yayan nasu sannan suka Fito tunda ya iso.

Gaban iya suka sameshi ya baza Babban Rigansa kansa a kasa cikin Ladabi da Alhini Bayan sun gama hannu da su Baffa Hashimu ya kalli Iya Cikin Dattakonsa yace"Iya ashe abunda kuma ya faru kenan..?

Da Safan nan Zuwaira ta Kirani take Fadamin abunda kuka wayi gari dashi..Ban ji Dadi ba matuka Hankalina ya tashi,har nama fita na koma gida Isma"il makaranta yaso ya koma yau ni na Hanasa saboda ya Tukani zuwa Lere Inna iyami najin abunda ya Faru tace zata Biyo mu zo muji abunda ke Faruwa."
Yafada cikin bayyana jimaminsa Inna Iyami na zaune saman kujera tana gyara Lullubinta tace"Abu kam bai yi Dadi ba Sunusi..yaron nan bai kyauta ba ammh ni na fara Tunanin baza"a Tashi Tsaye ba kuwa..?

Irin wannan al"amarin sai kuga da Sa hannun Junnu aciki."
Iya data gama jinsu ta tabe baki kafin tace"Ba wani junnu Hajiya..Ba kowa ke sakashi yi mana rashin D'a ba sai Uwarsa Zaliha,Sunusi Ina ganin girmanka matuka domin tun shekarun baya saboda Ladabinka da Tausasawarka yasa da Salahudden ya kawomin Zaliha a matsayin matarsa nayi Hakuri na karbeta,To yanzu ma saboda kai ne nace zan jira na Saurare ka ammh Wlh da na Rantse ko ni ko Zaliha acikin gidan nan ita da kanwarta gatanan zuwaira sai abunda ta manta na ci mana Zarafi."
Iya ta karishe Fada tana Sharan hawaye da Haban zaninta Ya sunusi ya Rankwafa yana Fadin"Ashsh.Abu bai yi Dadi ba..Don Allah Iya kiyi Hakuri..Ina mai baki Hakuri akan wannan lamarin."
Iya batayi mgana ba Baffa Hashimu ne yace"Nifa duk bama wannan ba..?

Saifudden nake son gani yanzu agaba na kila sai na Huce Daga Takaicin Daya kunsamin."
Ya sunusi ya kallesa cikin wani yanayi lamarin bai mai Dadi ba ya juya yana kallon Ummi da Mama Zuwaira Dake gefen Inna iyami,su sadiya suna ciki basu fito ba, Isma"il ya shiga ya Dauke musu hankali da Hira Domin gaye ne sannan dan Fafa ne sannan dan Jami"a ne dake karatu a jami"ar Bayero kano.

Gaishesa suka farayi Ya amsa cikin wani yanayin bacin rai kafin yace"Zuwaira me nake jin kin aikata ne haka..?.

Ta Dago kanta da niyar mgana ya Dakatar da ita da Hannu Cikin bacin rai yace"Juya ki bata Hakuri ko bakomai ki Daraja girmanta..Sannan ki Mutumta zuru"ar Dake Tsskaninta da yar"uwanki nasha miki Fada bana son Haka Zuwaira.."
Ranta bai so ba ta juya kanta na kasa tace ma Iya"Kiyi Hakuri.."
Daganan ta juya kanta takaici na cinta ina Laifinta a wannan mganar..?

Ba domin Ya Sunusi kamar Uba suka Daukesa ba,Bata ga mai sata bama wannan Tsohuwar Hakuri ba.

Ummi kuma kanta na kasa tana sharan kwallah Inna iyami tace"Ai hakuri duka za"ayi..Abunda Hakurin nan bai bamu ba to rashinsa fa bazai bamu ba.

Iya ta jinjina kai tana Fadin"Hakane..Tunda kuka saka baki naji zuciyata tayi sanyi..yanzu sai muje ga mafitan domin bazan Dauki wannan iskancin Wajen Saifu ba..Wato yayi na Farko yaji Dadi shine yanzu ya kara jiya jiya Daga kai yarinya har ya sakota..?

Gata chan ita da uwarta da Danginta suna ta famam koke wazai ce su bari..?

Ai abun kuka ne ya same su dole su koka."
Ya Sunusi ya gyara zama yana Fadin"Sosai Iya gaskiya Saifudddeen bai kyauta ba..Ya kuma shammace mu domin jiyan nan muna tare dashi bai nuna komai ba Har nasiha nayi mai fa ya nuna ya Dauka ban taba Zaton zai aikata Hakan ba."
Mama zuwaira ta karkace kai tana Fadin"To ita kanta ya zalihan fa..?

Jiya kamar zata ari baki wajen yima Saifu Fada kuma ya nuna yaji,Sai dai kasan ita Uwa ko yaya D'anta yayi abun Tir sai ace laifinta ne..."
Kallon da Ya sunusi ya bita dashi ne yasa ta kasa karisa mganarta goggo Atika ta yi kyafci kafin tace"Indai zata shiga mganar da ba nata ba nima kuwa ashe zamln iya shiga.

Inna iyami ta kalli Mama zuwaira tana Fadin"Kul zuwaira kada na kara jin bakin ki anan wajen"
Dole ta koma tayi shuru tana maida ma Atika martanin Hararanta.

Ya sunusi ya kalli Baffa Hashimu yana Fadin"Kun samu wayar shi Saifudden din..?

Baffa Hashimu yace"Ina..Tun Safe muke kiransa a kashe wayarsa."
Ya sunusi yace"Nima na kirasa bayan mun yi mgana da zuwaira a kashe..Ke Zaliha jiya kafin ya bar wajen ki me ya Fada miki..?

Ummi kanta na kasa tana sharam kwallah tace"Wlh Allah d'aya Ya sunusi bai fadamin komai ba bai kuma nuna min wani abu ba.Mun rabu akan Sai da safe cike da Fatan alheri na uwa da abunda ta Haifa..Ammh wlh bansam komai ba."
Sai kuka wiwi Ya sunusi ya jinjina kai yana Fadin"Ya isa Zaliha..ya isa haka..!

Sai ta Saussauta kukanta Baffa Hashimu ya kallah kafin yace"Ya Rubuta takarda ne shi Saifun..?

Ba musu Baffa Hashimu ya Saka hannu a aljihu ya dauko wata Farar Takarda ya mikama Ya sunusi shi kuma ya karba ya bude ya karanta ai duk wanda yasan Saifuddeen da wannan Hand writting din ya san sa sannan Har da karin shedar saka Hannunsa.

Yana gama karanta Takardan yace"Bai kyauta ba sam..Sai dai naji Dadin da ba Saki uku bane saki Daya ne akwai yuyuwar zamu iya samun gyara."
Baffa Hashimu yace"Ta ina..?

Yaya Sunusi yace"Hakuri zamu taru muyi yanzu saboda bamu da tacewa Tunda Saifuddem bashi anan wajen..Ni kaina nayi ta nemansa ban Samesa ba,Kenan duk abunda zamu yanke ko mu Tattauna bai da amfani yanzu Dole sai in yana nan wajen.."
Baffa Hayatu ne yayi mgana yanzu yana Fadin"Ai naji ita Sadiya tana Fadin mijinta yaje chan gidan gwamnati ya samu suna taro da gwamna kuma yana da yakinin shi Saifuddeen zai je taron a kirasa aji indan sun hadu.

Ya Sunusi yace"To..To ai bansani bane..Ke Zuwaira haka akayi..?

Kai ta dagamai da Sauri yace"Kiramin Sadiyar..!

Ba musu ta mike ta shiga Cikin Mintina kadan sai gata ita da Sadiya ta Zube gaban Ya sunusi tana Fadin"Sannu da zuwa kawu..ya Hanya..?

Ya amsa mata cikin Sakewa ta juya tana gaida Inna Iyami itama ta amsa Kafin Ya Sunusi yace"Kin yi mgana da Megidan ki kan Saifudden ko..?

Ta daga kanta cikin,ladabi Ya sunusi yace"To kun sake mgana dashi ko sun hadu..?

Sadiya tace"Mun rabu zai kirani in ya samu ganinsa ammh har yanzu bai kira din ba."
Ya sunusi bai yi mgana ba ya karkace ya Fiddo wayarsa ya mikama Sadiya yana Fadin"Zaki ga Mujaheed kiramin shi.

Ba musu ta karba bata tsaya ma neman suna ba ta rattaba lambar Saboda ai yana kanta sai gata ta fito sai ta kira masa,Kiran har ya katse bai Dauka ba Sadiya ta kallesa tana Fadin"Kawu bai Dauki kiran ba.

Ya Sunusi yace"Baya Daukan kirana..Sai dai nasan zai kira Daga baya."
Ko gama rufe baki bai yi ba wayarsa ta fara kara Da Sauri Sadiya tace"Shi ne kawu..

Kai ya jinjina mata kafin yace"Daga kiran ki saka ta a amsa kuwwa."
Haka kuwa tayi ta Daga ta sanyata Cikin Speaker ta mika ma kawu ya amsa Lokaci Daya yana amsa sallamar Mujaheed bayan gaisuwa da Tambayan aiki kawu yace"Mujaheed gani na dawo lere saboda matsalan Dan"uwanka..Ko kun hadu dashi..?
Chapter 8 · 0% Book details