← Book details Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 144

Sashe 10

Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sannan arana ta uku ne ya samu wayar parmanent Sacatary kan yana son ganinsa Dalilin Fitan ne kenan da yammah yaje chan Ministry suka Hadu suka Tattauna har yaja sa Gidansa sukayi Dinner awajen ma sai mai Tsiyan yaki aure yake yi shi dai baya mgana sai yake Allah fa na Rufamai asiri duka auransa da akayi mai ya saki bai taba gayyatan kowa ba Sannan har yanzu mganar bata Fasu ba.

Aranar Hotel din ya koma ya kwana Sai da Safe ne ya baro nan ya koma Gidansa Dake anguwan Sarki yasan Mujaheed ya kyalesa bazai kara Nemansa ba,Sannan yasa layin Ummi a Trak domin yaga ko ta na ina..?

Sai yaga ta koma Abuja tun jiya da Rana,Sai hankalinsa ya kwanta yasan yanzu matsalan kadan ne Lere zai Fara zuwa ya warware ta chan kafin Abuja Bangaram kawu mai Sauki ne bai da Zafafawa kan wasu al'muran Daga baya sai yaji da Muhajeed da Addarsa Domin yasa sun yi bala"in Daukan Zafi dashi
Kwana Hudu da Faruwar abun ya samu kiran Director Musa kan abunda ya shafi wata makaranta Dake Zaria sun Dade suna Tattauna kan dai abubuwan da makaranta ke bukata sannan da kuma Bikin Speech and Prize giving day din da za"a shiryama Dalibai a wannan Tearm din.

Duk da ba zuwa zai yi ba sai dai yana da Alhakin duba komai Kafin su Rabu da Director musa sai da yace ya Turamai jawalin duka Tsara tsaran ta Tab dinsa saboda ya Duba in ya samu Lokaci.

Shi kanshi bai da wani sukuni Saboda suna shiryen shiryen daukan Sabbin malaman sakandari,sannan akwai Jawalin Tsare tsaren gyaran makarantun gwamnati guda 100 ajahar kaduna kuma suna hannunsa shi zai gabatar ma gwamna duk da zaman da sukayi da shi ya dan shigar da mganar sannan sun Tattauna wasu da parmanent Sacatary da Diractor na Board Education ammh saboda yadda ya maida kansa Busy yasa abunda ya Faru a Lere ya bace gabadaya a Tunaninsa yana ganin abu ne mai sauki cikin lokaci daya zai Daidaita komai.
*******
Zaria.

Yau ta kama jumma'a ne gabadaya ake tashin makarantar ta SAIFUDDEEN ACADEMY 12:30pm ba kanar sauran ranakun ba da Shashen Nursing ke tashi 12:50pm Shashen Primary kuma su tashi 2:00pm Saboda basa lesson shashen Jss da SS kuwa sai 3:30pm suke tashi Gabadaya.

Gabadaya makaranta Ta Yamutse yara nata Haraman Tafiya Wadanda ake zuwa Daukansu a kan abun hawa suna Harama masu kekuna da mashina ma suna ta hawa abunsu malamai suna ta haraman tafiya ciki har da Muhibba Data Tattaro ya"yan yayar ta,Siyama dake primary 3,sai walid dake primary 5 sai babbansu Khalipa dake Jss2,Saboda ita yasa Babansu ya cire su a inda suke da farko nan Tudun wada ya kawo su inda muhibba ke koyarwa sannan makaranta ko wa ya santa akwai karatu saboda malamansu sun san abunda suke yi.

Akwai mai Adaidaitan dake kawo yaran yana kuma zuwa Daukansu to har yazo shi Muhibba zata bi domin yau tace ma Inna gidan Anty Habiban zata karishen yininta in ta sun tashi Daga makaranta.

Na gama saka yaran a daidaitan kenan zan shiga naji Muryan Uncle Hafiz na min mgana sai na Dataka na juyo ina kallonsu shi da Anty Khadija suna karisowa.

Sai da suka kariso sannan Uncle Hafiz yace"Anty Muhibba tafiya ba sallama.."
Cikin yanayin mirmishina na sakar mai kafin nace "Laa..Naje staffroom sanda zan kai ma Headtecher key din clasas ban gan ka ba Har Anty Debora sai da na Tambaya tace itama tun Safe rabonta Dakai.."
Kansa ya shafa kafin yace"Wlh ina wajen Director ya Kirani kan Tsare tsaren Speech din na yara da zamu yi shiyasa bani a Shashen namu yau.."
Muhibba "Ayya shi yasa.."
Khadija na kalla wacce ta Dauke kanta sama kamar bata a wajen muhibba zata mata mgana kenan Walid ya leko yana Fadin"Anty Auta yunwa plz ki zo mu tafi.."
Siyama ce tace"Lala..ba Mommy tace ba sunanta Auta ba..?

Sai na Fada mata in muka koma gida.

Muhibba tace"Barsa ai sai na Dirje bakin sa sannan zai daina ce min Anty Auta..!

Khalipa na jinsu yayi Dariya bai ce komai bayan ya leko ya gaida Uncle Hafiz Siyama kuma nokewa tayi tunda shine class room Teacher dinsu ada kafin ya koma aji shidda.

Uncle Hafiz yayi Dariya kafin ya leka adaidaitan yana Fadin"Siyama Gambo..!

Ta amsa da Sauri"Present sir.

Yana Dariya yace"Baki taba fadamin sunan Anty Muhibba Anty Auta ba..?

Sai Siyama ta rufe baki kafin tace"Kai kai Uncle bata so..ko mommy ma in tace mata Fada suke yi"
Harara Muhibba ta yankama Siyama bata yi mgana ba Uncle Hafiz ya Dago yana Fadin"Anty Auta sai monday kenan ko..?

Muhibba ta hararsa shi Shi kuma yana Dariya,Khadija Dake gefe ta tabe baki ta wuce Tana fadin"Hafiz na tafi bazan tsaya ina jiranka kana ta wani shiririta kamar mace ba..!

Tayi gaba abunta ganin haka yasa Muhibba tace"Uncle kuje kawai..Sai monday."
Ya amsa min da Allah ya kaimu Daganan mukayi sallama su siyama na Dagamai hannu tana fadin"Bye bye uncle.

Adaidaitan na shiga muka fara Tafiya acikin raina nayi shiru duk da ina jin yadda gaddama ta Sarke tsakanin Walid da Siyama ammh na kasa mgana Tunani tlnake yi me na tsare ma Anty Khadija a makarantar nan ne Datake Bakinciki da ni..?

Ita da Anty Usaina ne basa kaunata a makarantar nan tun sanda suka je Interviuw domin tare aka Dauke mu aiki ko basu so na samu bane ban sani ba ammh abun nasu yayi yawa ko ganina sukayi kamar sun ga kashi in nayi musu mgana sai sun ga Dama suke amsa min suna kuma jin haushin wani yayi min mgana ko Hafiz ba"a son ransu yake kulani ba,Shi anguwansu Daya da Khadija a Samaru suke da zama Anty Usaina kuma Matar aure ce Cikin muciya take aure.

Har mai adaidata ya kai Cikin FCE zaria Muhibba bata sani ba sai da taji Siyama na fadin Anty mun kawo sannan ta Dawo Hayyacinta ta Daga kallonta kan Jerin Quaters din ma"aikatan Fce zaria tunda mijin Anty Habibar babban ma"aikaci ne anan cikin makarantar.

Har yaran suka yi gaba tana ina baya jikinna a sanyaye ina rumgume da littafaina,na shigo Falon gidan da Sallama Anty Habibi dake kokarin Taimaka siyama ta cire Safarta ta Dago tana amsa sallamar kanwar tata.

Zubewa nayi kan kujera da ni da Littafan nawa,yasa Anty Habiban ta kara kallonta tana Nazarinta..

Walid ne ne ya kwanta a kasa yana Fadin"Mommy yunwa wlh..yau bamu je da basket ba..!

Anty Habiba ta kallesa kafin tace"To acici sarkin ci..ga kanwar ka nan siyama itama ai haka taje kuma bata Dawo tana wannan korafin ba.

Walid ya tura baki kafin yace"Ai bani kadai bane Anty Muhibba ma tana jin yunwa ko Anty..?

Hararansa nayi kafin nace"Tunda nice Sa"arka ba.."
Siyama tayi karaf tace"Mommy hauahi take ji ya walid fa agaban Uncle din mu yace mata Anty Auta..!

Tafada tana rufe baki Anty Habiba Tayi Dariya kafin tace"Lalle ko yau mun gan su arana..!

Tafada Lokaci Daya tana mikewa khalipa tuni ya wuce Dakinsu Walid ta kallah Tana fadin"Sai ka tashi kaje ka sauya kaya kabi khalipa ku tafi masallacin jumma"a..

Walid ya mike yana kunkunin yunwa Anty Habiba tace"aiko suma zakayi sai ka dawo masallaci zaka ci abinci acicin banza kawai..!

Haka ya wuce Siyama namai Dariya yana Fadin in ya kamata sai ta sani.

Anty Habiba Dakin da take tara Shirgi ta shiga Tunda wajen Bedroom Hudu gareta a flat din nata.

Har ta fito Muhibba na zaune tayi jugum da ita har zata shiga Kitchen sai ta fasa ta tsaya agaban muhibban tana kallonta itama kamar Muhibban haka take sai da ita tafi Muhibba jiki giant ga tsawo ga kiba sannan tafi muhibba hasken fata.

Ganin bata san ma tana Tsaye kanta bane yasa ta tabo kafarta tana Fadin"Ke Auta..?

Lafiyar ki kuwa..?

Sai sannan Muhibba ta Dawo Hayyacinta ajiyar rai na sauke ina kallon Anty Habiba kafin nace"Lafiya ne Gajiyar makaranta ce kawai..

Anty Habiba tace"Ko gaskiyan Walid ne da Yunwa kuma ko..?

Muhibba tace"A"a wlh ai kowa ba irin sa bane mai cin tsiya."
Anty Habiba tace"To kodai kin Hadu da Aljanin naki ne..?

Muhibba ta kalleta gabanta na Fadi kafin tace"Aljani na.?

Shi wa..?

Anty Habiba tace"Shi SAIFUDDEEN mana.."
Binta nayi da kallo sanda ta juya ta shige Kitchen din dake falon gabana na Fadi nima fa tunda su Inna suka ce Saifudden ba Mutim bane nake Fama da faduwar gaba duk sanda aka ambaci sunansa,Ni kaina dana zauna nayi nazari da kuma yadda Mallam Haruna yayi bayani ai naTabbatar ma da kaina Saifudden ba Mutum ba ne Aljanine..!
*Littafin Saifuddeen na kudi ne pay N500 via 0552179550 Jamila umar Gt bank,sai a turo evidence of payment ta wannan Lambar 09069067488 ko kuma katin waya na Mtn sai adauki Hoton katin a tura ta wannan Layin kai Tsaye 09069067488 mutanen mu na Niger kuma zasu tuntubi Kausar aglan Nissa ta wannan lambar domin karin bayani +22796562223 Ina maraba da masoya na a duk inda suke*
*Janafty*
*SAIFUDDEEN*
_(Ba mutum ba ne)_
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Amnaf_sudanese _collection*
*Tana saida original laffaya kala daban daban daga Sudan kama daga na Amare da Kuma casual muna da available a Nigeria kuma Muna aikawa daga Sudan Zuwa Nigeria ko'ina a fadin Jahohi talatin da shida har ila yau dai akwai humra da turarrukka sadidan na matan aure daga Sudan,ba fa anan kada'i muka tsaya ba Muna saida kayan lalle akan sari da Rahusa da kuma siyan Daya,akwai mayuka da dilka da kayan gyaran jiki na ainahin ba Mix ba, wadan'da zasu fitar Miki da fatar ki tas ba bleaching fuskarki tayi haske tayi walwal kina kyalkyali and duk abunda kikeso a Sudan Muna kawo Miki shi har gda Nigeria Amnaf Sudanese collaction ba abunda bama saidawa kama daga kayan kamshin jiki na kaya da na fata +249923097401*
Har Anty Habiba ta fito daga Kitchen,Muhibba na zaune ta kasa ko kakkwaran motsi ga yanayin data shigo,Sannan ga karin mganar Anty Habiba yasa sai abubuwan suka taru suka mata yawa,batama san Anty Habiba ta kariso gefenta ba sai da taji Tana fadin"Zaki ci abinci yanzu ko sai kin yi sallah..?
Chapter 10 · 0% Book details