Sashe 33
Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita dai ficewa tayi ta barsu suna ta caccakan Hammanta bai san ma sunayi ba ya juya musu baya,sai da suka gama koshi sannan suka fice kofar gida wajensu kawu,har La"asar suna garin Gaya sai da sukayi sallar La"asar ne sukayi shirin Tafiya,Sadiya sai gobe zata biyo su Ummi su sauketa Kaduna su wuce Abuja,Cikin gida suka shiga sukayi musu sallama sannan suka fito kofar gida su Datti sun rakosu bakim mota su Tim daman Tun zuwansu suna bakin mota kamar ita suke tsaro.
Da zasu yi sallama da Kawu sai yayi ma Saifudeen Nasiha fadi yake"Baka sha"awar Dan"uwanka Saifudeen..?ka isa aure kana da abun yin auran nan me zai hana kayi ko domin ka saka zuciyar Mahaifiyarka tayi sanyi..In wadanchan baka son su ai sai ka zaba ga mata nan birjit daidai da Zabinka duk yarinyar da kace kana so ko yar gwamnace wlh bamai cewa bazai baka ba Don Allah kayi Tunani kaji ko zama haka din ba amfani.
Sun kama Hanyar barin Kano Saifudeen yace"Zuwana Gaya yau ban je a sa"a ba..Fada ne nasha shi Step by Step.."
Mujaheed sai kwasan Dariya yake yi Saifudeeen yace"Wlh kamin shuru kafin na Sauke ka a dajin nan..
Mujaheed yace"Ai ba wulakantattace bane ni..Balle in ka Saukeni na wulakanta.
Daga haka suka bar mgana Daganan ma kowa sai ya koma Danna wayarsa,Sun shiga kaduna bayan mangariba har gida suka kai mujaheed sannan ya wuce gidansa Ranar bayan ya gama abunda zai yi ya kwamta mganar kawu sai ta Dawo mai to shi a ina zai samu wacce ta Dace dashi?
Ina take..?
Wacece ita..?
Kuma zai ji ya fara sonta.?.
Shima yana so yayi auran zabin sa ko domin Farimcikin Ummi ammh wacce zau auran ne wacce zata Dace dashin bai gani ba har yau duk da ga tarin mata nan kala kala masu kyau da Nasaba da ilimi har yau bai ji in ya kallesu yaji wani abu so in ya auresu zasu iya taka matsayin da su Majeeda suka taka suma shima bai taba kwantatawa ba Har barci ya kwashe shi bai samu mafita ba.
Washegari Zaria ya shigo Yana da lecture karfe10 na safe bayan ya gama Dasu Kaura ya wuce daganan Saboda Duba aikin kwangilan makarantar da gwamna ya bada har an fara dagachan yayi zagaye sosai sai yammah ya Dawo gida duk ya gaji aikin al"umma daman sai an Daure.
Suma su Inna da Yaya Habibu aranar sukaje gaya din ta hadu da Ummi da Mama zuwaira sun dade basu ga juna aka zauna aka gaisa da tambayan bayan Rabuwa sun yi gaisuwa sannan sun karisa gidansu Inna ta gaida Hajiya,da su goggo Naja sannan tayi musu Allah sanya alheri da Ranar da aka sanya ma Autar Inna Firdausi Basu kwana ba aranar suka juyo zuwa zaria.
********
*Zaria.
Muhibba ta Zage Damtse batayi wasa da aikin da D.Musa ya bata ba,wani karin jin Dadinta Taimakon Hafiz gareta sai abun yazo mata da Sauki Cikin ikon Allah yaran sun yi Rizahal kuma komai ya tafi daidai bangaran Drama ma haka ranar kawai ake jira sannan an tsara za"a raba kyattuka ga Prefect da Dalibai masu hazaka da wadanda suka ci duka Quiz da Debete din da za"a gudanar.
Komai sun shirya kawai suna jiran Ramar ne tunda Har Daliban SS3 din sunfara Neco,An buga Invitation card an saka acikin Farin Mblog an bama kowani Dalibi ya kai ma iyayansa sannan an yi na waya an Turama wadanda katin bazai je hannunsu ba,Duk da dai mai makarantar yace Iyayen yara kadai ya amince a gayyata bayason yan Siyasa ko wasu masu Mulki makarantarsa bata yan siyasa bace bata masu mulki bace shiyasa ba wani sunan wani bako ajiki banda Babban bako Wato shugaban makarantar sai iyayan yara da yan"uwansu kawai.
Duk da basu da tabbacin zuwanshi ammh Dan"uwanshi ya Tabbatar ma da D.Musa zai hallata insha Allahu shiyasa sai ya samu yakini.
Bayan sun gama da wannan bangaran sai bangaran tsara Halla da Mc da zai gabatar da wajen Wannan Uncle James zaj ji da bangaran,Sai kuma barayin Snkas da za'a raba da lemuka Shi kuma Uncle Hafiz yace Muhibba ta iya irin wadanan abubuwan ita da yayarta,Sai D.Musa ya ce tayi lissafin abunda za"a kashe na Meatpie da Cake da Donut,Ruwa kuma da Lemu mota guda ce zata zo ta sauke shi basu da matsalan wannan bangran gift kuma Hafiz da sauran malaman sun Tsara shi Daki daki Daga matakin Farko har zuwa mataki na wanda yayi na uku.
Muhibba gidan Anty Habiba taje ta Fadamata abunda D.Musa yace,Duka kowanne yana son Spicess 400 ne aikin da yawa tare suka zauna suka Lissafa komai da komai,washegari da taje makaranta ta fadamai yace ta bashi acct Number dinta in lokacin ya kusa zai Tura mata kudin Komai da komai harda na Ladan aikin.
Su Khadija basu sani ba Dayake ba"a gaban Mutane akayi ba,Hafiz ne a wajen dasu Headteacher kuma ai ita bazataje ta fada ba ballatana Hafiz Dayake Namiji,Ba wanda ya sani sai Anty jidda ita kuma ba Shashensu daya da Su ba ballatana su dameta iyakarta dasu gaisuwa in sun hadu.
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah gashi har Taron ya matso ana Saura Sati Daya D.Musa ya turo ma Anty Habiba kudin abunda za"a kashe har da 20k kudin aikinta Daman Acct Nomber dinta Muhibba ta basa,ta Kirata tana fadamata tace ta kirasa ta mai godiya bata da lambarsa sai ta shiga group dinsu na Managent na makaranta dake manhajar WhatApps,ta Dauka ta kirasa tamai godiya yace kada ta damu she Deserve it,Suna tsakar gida Ranar Asabar din ita da Inna tana tayata bare waken Yaya Habiba na gona da aka ciro,Inna ta shanya sai da ya Bushe suka zauna suna barewa Dayake ma bai da wani yawa irin karshen gona ne.
Suna barewan suna hira Tana Fadama Inma yadda sukayi da Yaya Habiba Inna tace"To yaushe ne Taron..?
Muhibba tace"Inna Saura kwana bakwai fa Rana ita yau ne.
Inna tace"Allah ya kaimu..Sau kuyi musu da wuri saboda su ji dadin aikin naku kunga in sukaji dadi sai ima wata makaranta zata yi sai kuji an yaba da aikin ku har kun ci gaba."
Muhibba tace"Hakane Inna..Anty Habiba tace nazo Tun ranar Laraba ne mu fara aikin tunda yana da yawa kilama sai ta kira kanwar Baban Waled Asma"u ta tayamu.
Inna tace"Eh to sai ta kira ta din Allah ya taimaka.
Kafin Muhibba ta amsa da Ameen Sani yayi sallama ya shigo gidan,Sanye da riga da wando,sai Katuwar bakar jaka goye a bayansa sai Akwatinsa trolley yana ja Muhibba ta waiga ta gansa ai sai ta saki aikin Inna ta Nufesa tamai oyoyo ta Daka Tsalle ta Rumgumesa tana Fadin"Oyoyo..oyoyo..!
Riketa yayi tana neman kada su Cikin Dariya yace"Inna me kika bama Autar naki ne ta kara girma haka.
Yafada yana dariya Dayake sun shirya Tuni sun daina gaba.
Inna da bakinta yaki rufuwa tace"Maraba da sani.maraba da kanawa..!
Muhibba ta sakeshi Lokaci Daya tana karban Akwatinsa ta sa hannu taja jakar bayansa yace"Ke ban da wannan..yara basa tabawa.
Baki ta tabe kafin tace"Ai nasan Shopping din yan matanka ne cike a cikin Jakar..!"
Yana karisawa gaban Inna yace"Eh sune acikin ina ruwanki..?
Muhibba ta ja akwatinsa zuwa Dakin Inna Tana fadin"Babu fa.
Gaban Inna ya durkusa yana gaisheta ta amsa cikin Fara"a tana fadin"Dawowa ba sanarwa Sani haka ake yi..?
Yana dariya yace"Inna suprise nake son baku..mun gama jarabawa tun wanchan satin na tsaya wani abu ne yasa ma kuka ganni sai yau.
Inna tace"Masha Allah haka jiya yayanku sai cewa yake yana Tunanin kun gama jarabawa baya samun wayarka yace Auta tace kasheta kayi saboda jarabawa.
Sani yace"Eh Inna saboda mutun ya natsu waje daya..
Inna tace"Hakane kuma Allah ya bada sa"a gashi Tuwo Muhibba tayi mana da Rana Zeenatu na kaduna kanwarta ta haihu yau suna.
Sani ya bata rai kafin yace"Tuwo kuma Inna..?
Muhibba ta fito tana Dariya tace"Miyar kuka ce ammh kada ka damu taji kifi.
Hararanta yayi kafin yace"Muguwa ai nasan ke zaki tursasa ma inna ayi tuwon nan..Kije don kanki muhibba.
Dariya ta sakamai har da gwallo ya nuna kansa alamun ni ta daga kai ya kallli Inna yana Fadin"Inna ki na ganin Abunda Autarki kemin ko..?
Salon na maketa Ya habibu ya dawo ta Fadamai yace nayi zalunci.
Inna tace"Rabu da ita yau kaine Autana me zakaci na tashi na Dafa maka.?
Yana kallon muhibba yace"Inna Shinkafa da wake..ammh ki bar muhibba ta dafa min.
Muhibba na tsaye tace"Tab ai ni tuwona har dare nayi ni da shiga kitchen sai kuma gobe.
Sani ya mike yana fadin"Yarinya nazo miki da gurasa fa..!"
Muhibba ta washe baki tace"Da gaske..?
Sani yace"Ki dafamin abinci na baki..In kuma kikayi mungunta to kanki zata kare."
Muhibba tace"Inna kina ji ko..?
Inna na Dariya tace"Naji kina gamawa zai miko miki gurasarki"
Yana dariyan keta yace ya yarda jikin Muhibba na rawa ta fada kitchen din Inna tana Fadin"Yanzu za"a gama.
Sani sai dariya yake mata Inna ta dauko mai key din Dakinsa ya Bude duk yayi kura afili ya furta"Muhibba bata da mutumci irin kanne masu kirki kiga suna gyara dakin yayansu banda yarinyar chan."
Karsheta dai shi ya zage ya gyara yana gamawa ana kiran sallar La"asar ya fita yaje masallaci bai dawo ba sai wajen Biyar koda ya dawo Muhibba ta gama mai shinkafa da wakensa datace ya fito da gurasa yace ta bari yaci ya koshi yana gamawa suka mike zuwa Dakinsu inda zai Dauko mata suna zuwa Zaure ya arce a guje yana Fadin"Kin yi aikin Allah Autar Inna.
Da zasu yi sallama da Kawu sai yayi ma Saifudeen Nasiha fadi yake"Baka sha"awar Dan"uwanka Saifudeen..?ka isa aure kana da abun yin auran nan me zai hana kayi ko domin ka saka zuciyar Mahaifiyarka tayi sanyi..In wadanchan baka son su ai sai ka zaba ga mata nan birjit daidai da Zabinka duk yarinyar da kace kana so ko yar gwamnace wlh bamai cewa bazai baka ba Don Allah kayi Tunani kaji ko zama haka din ba amfani.
Sun kama Hanyar barin Kano Saifudeen yace"Zuwana Gaya yau ban je a sa"a ba..Fada ne nasha shi Step by Step.."
Mujaheed sai kwasan Dariya yake yi Saifudeeen yace"Wlh kamin shuru kafin na Sauke ka a dajin nan..
Mujaheed yace"Ai ba wulakantattace bane ni..Balle in ka Saukeni na wulakanta.
Daga haka suka bar mgana Daganan ma kowa sai ya koma Danna wayarsa,Sun shiga kaduna bayan mangariba har gida suka kai mujaheed sannan ya wuce gidansa Ranar bayan ya gama abunda zai yi ya kwamta mganar kawu sai ta Dawo mai to shi a ina zai samu wacce ta Dace dashi?
Ina take..?
Wacece ita..?
Kuma zai ji ya fara sonta.?.
Shima yana so yayi auran zabin sa ko domin Farimcikin Ummi ammh wacce zau auran ne wacce zata Dace dashin bai gani ba har yau duk da ga tarin mata nan kala kala masu kyau da Nasaba da ilimi har yau bai ji in ya kallesu yaji wani abu so in ya auresu zasu iya taka matsayin da su Majeeda suka taka suma shima bai taba kwantatawa ba Har barci ya kwashe shi bai samu mafita ba.
Washegari Zaria ya shigo Yana da lecture karfe10 na safe bayan ya gama Dasu Kaura ya wuce daganan Saboda Duba aikin kwangilan makarantar da gwamna ya bada har an fara dagachan yayi zagaye sosai sai yammah ya Dawo gida duk ya gaji aikin al"umma daman sai an Daure.
Suma su Inna da Yaya Habibu aranar sukaje gaya din ta hadu da Ummi da Mama zuwaira sun dade basu ga juna aka zauna aka gaisa da tambayan bayan Rabuwa sun yi gaisuwa sannan sun karisa gidansu Inna ta gaida Hajiya,da su goggo Naja sannan tayi musu Allah sanya alheri da Ranar da aka sanya ma Autar Inna Firdausi Basu kwana ba aranar suka juyo zuwa zaria.
********
*Zaria.
Muhibba ta Zage Damtse batayi wasa da aikin da D.Musa ya bata ba,wani karin jin Dadinta Taimakon Hafiz gareta sai abun yazo mata da Sauki Cikin ikon Allah yaran sun yi Rizahal kuma komai ya tafi daidai bangaran Drama ma haka ranar kawai ake jira sannan an tsara za"a raba kyattuka ga Prefect da Dalibai masu hazaka da wadanda suka ci duka Quiz da Debete din da za"a gudanar.
Komai sun shirya kawai suna jiran Ramar ne tunda Har Daliban SS3 din sunfara Neco,An buga Invitation card an saka acikin Farin Mblog an bama kowani Dalibi ya kai ma iyayansa sannan an yi na waya an Turama wadanda katin bazai je hannunsu ba,Duk da dai mai makarantar yace Iyayen yara kadai ya amince a gayyata bayason yan Siyasa ko wasu masu Mulki makarantarsa bata yan siyasa bace bata masu mulki bace shiyasa ba wani sunan wani bako ajiki banda Babban bako Wato shugaban makarantar sai iyayan yara da yan"uwansu kawai.
Duk da basu da tabbacin zuwanshi ammh Dan"uwanshi ya Tabbatar ma da D.Musa zai hallata insha Allahu shiyasa sai ya samu yakini.
Bayan sun gama da wannan bangaran sai bangaran tsara Halla da Mc da zai gabatar da wajen Wannan Uncle James zaj ji da bangaran,Sai kuma barayin Snkas da za'a raba da lemuka Shi kuma Uncle Hafiz yace Muhibba ta iya irin wadanan abubuwan ita da yayarta,Sai D.Musa ya ce tayi lissafin abunda za"a kashe na Meatpie da Cake da Donut,Ruwa kuma da Lemu mota guda ce zata zo ta sauke shi basu da matsalan wannan bangran gift kuma Hafiz da sauran malaman sun Tsara shi Daki daki Daga matakin Farko har zuwa mataki na wanda yayi na uku.
Muhibba gidan Anty Habiba taje ta Fadamata abunda D.Musa yace,Duka kowanne yana son Spicess 400 ne aikin da yawa tare suka zauna suka Lissafa komai da komai,washegari da taje makaranta ta fadamai yace ta bashi acct Number dinta in lokacin ya kusa zai Tura mata kudin Komai da komai harda na Ladan aikin.
Su Khadija basu sani ba Dayake ba"a gaban Mutane akayi ba,Hafiz ne a wajen dasu Headteacher kuma ai ita bazataje ta fada ba ballatana Hafiz Dayake Namiji,Ba wanda ya sani sai Anty jidda ita kuma ba Shashensu daya da Su ba ballatana su dameta iyakarta dasu gaisuwa in sun hadu.
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah gashi har Taron ya matso ana Saura Sati Daya D.Musa ya turo ma Anty Habiba kudin abunda za"a kashe har da 20k kudin aikinta Daman Acct Nomber dinta Muhibba ta basa,ta Kirata tana fadamata tace ta kirasa ta mai godiya bata da lambarsa sai ta shiga group dinsu na Managent na makaranta dake manhajar WhatApps,ta Dauka ta kirasa tamai godiya yace kada ta damu she Deserve it,Suna tsakar gida Ranar Asabar din ita da Inna tana tayata bare waken Yaya Habiba na gona da aka ciro,Inna ta shanya sai da ya Bushe suka zauna suna barewa Dayake ma bai da wani yawa irin karshen gona ne.
Suna barewan suna hira Tana Fadama Inma yadda sukayi da Yaya Habiba Inna tace"To yaushe ne Taron..?
Muhibba tace"Inna Saura kwana bakwai fa Rana ita yau ne.
Inna tace"Allah ya kaimu..Sau kuyi musu da wuri saboda su ji dadin aikin naku kunga in sukaji dadi sai ima wata makaranta zata yi sai kuji an yaba da aikin ku har kun ci gaba."
Muhibba tace"Hakane Inna..Anty Habiba tace nazo Tun ranar Laraba ne mu fara aikin tunda yana da yawa kilama sai ta kira kanwar Baban Waled Asma"u ta tayamu.
Inna tace"Eh to sai ta kira ta din Allah ya taimaka.
Kafin Muhibba ta amsa da Ameen Sani yayi sallama ya shigo gidan,Sanye da riga da wando,sai Katuwar bakar jaka goye a bayansa sai Akwatinsa trolley yana ja Muhibba ta waiga ta gansa ai sai ta saki aikin Inna ta Nufesa tamai oyoyo ta Daka Tsalle ta Rumgumesa tana Fadin"Oyoyo..oyoyo..!
Riketa yayi tana neman kada su Cikin Dariya yace"Inna me kika bama Autar naki ne ta kara girma haka.
Yafada yana dariya Dayake sun shirya Tuni sun daina gaba.
Inna da bakinta yaki rufuwa tace"Maraba da sani.maraba da kanawa..!
Muhibba ta sakeshi Lokaci Daya tana karban Akwatinsa ta sa hannu taja jakar bayansa yace"Ke ban da wannan..yara basa tabawa.
Baki ta tabe kafin tace"Ai nasan Shopping din yan matanka ne cike a cikin Jakar..!"
Yana karisawa gaban Inna yace"Eh sune acikin ina ruwanki..?
Muhibba ta ja akwatinsa zuwa Dakin Inna Tana fadin"Babu fa.
Gaban Inna ya durkusa yana gaisheta ta amsa cikin Fara"a tana fadin"Dawowa ba sanarwa Sani haka ake yi..?
Yana dariya yace"Inna suprise nake son baku..mun gama jarabawa tun wanchan satin na tsaya wani abu ne yasa ma kuka ganni sai yau.
Inna tace"Masha Allah haka jiya yayanku sai cewa yake yana Tunanin kun gama jarabawa baya samun wayarka yace Auta tace kasheta kayi saboda jarabawa.
Sani yace"Eh Inna saboda mutun ya natsu waje daya..
Inna tace"Hakane kuma Allah ya bada sa"a gashi Tuwo Muhibba tayi mana da Rana Zeenatu na kaduna kanwarta ta haihu yau suna.
Sani ya bata rai kafin yace"Tuwo kuma Inna..?
Muhibba ta fito tana Dariya tace"Miyar kuka ce ammh kada ka damu taji kifi.
Hararanta yayi kafin yace"Muguwa ai nasan ke zaki tursasa ma inna ayi tuwon nan..Kije don kanki muhibba.
Dariya ta sakamai har da gwallo ya nuna kansa alamun ni ta daga kai ya kallli Inna yana Fadin"Inna ki na ganin Abunda Autarki kemin ko..?
Salon na maketa Ya habibu ya dawo ta Fadamai yace nayi zalunci.
Inna tace"Rabu da ita yau kaine Autana me zakaci na tashi na Dafa maka.?
Yana kallon muhibba yace"Inna Shinkafa da wake..ammh ki bar muhibba ta dafa min.
Muhibba na tsaye tace"Tab ai ni tuwona har dare nayi ni da shiga kitchen sai kuma gobe.
Sani ya mike yana fadin"Yarinya nazo miki da gurasa fa..!"
Muhibba ta washe baki tace"Da gaske..?
Sani yace"Ki dafamin abinci na baki..In kuma kikayi mungunta to kanki zata kare."
Muhibba tace"Inna kina ji ko..?
Inna na Dariya tace"Naji kina gamawa zai miko miki gurasarki"
Yana dariyan keta yace ya yarda jikin Muhibba na rawa ta fada kitchen din Inna tana Fadin"Yanzu za"a gama.
Sani sai dariya yake mata Inna ta dauko mai key din Dakinsa ya Bude duk yayi kura afili ya furta"Muhibba bata da mutumci irin kanne masu kirki kiga suna gyara dakin yayansu banda yarinyar chan."
Karsheta dai shi ya zage ya gyara yana gamawa ana kiran sallar La"asar ya fita yaje masallaci bai dawo ba sai wajen Biyar koda ya dawo Muhibba ta gama mai shinkafa da wakensa datace ya fito da gurasa yace ta bari yaci ya koshi yana gamawa suka mike zuwa Dakinsu inda zai Dauko mata suna zuwa Zaure ya arce a guje yana Fadin"Kin yi aikin Allah Autar Inna.