← Book details Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 144

Sashe 31

Saifuddeen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sannan mganar Aljanah ta auresa bai yarda ba,Saboda shi baya yarda da wannan Chanfe chanfen sam,Koda Iya ta saka Baffa Hashimu ya kirssa tana kiramai jawabin abunda malamin da sukaje wajensa yace wai Aljana ce hatsabibiyace ta auresa in ba"a Dage ba shi da aure har Abada shi dai bai ce komai ba Sannan Iya ta matsamai sai da ya aika Bama ya karbo Mganguna suna bayan Booth tun sanda aka karbo masa ko kalan su bai gani ba,Sannan bayan haka akwai wani abu Dangane da mganar Mujaheed akan bai taba jin chanji Daga yanayinsa ba..?

Tabbas ya taba ji shekaru Takwas da suka gabata sanda yaje Standford University,akwai wata class mate dinsa Janet baturiya ce suna mutumci da ita har suka zama abokai watarana suna Dakin karatu ta kama bakinsa ta faramai kiss wani abu ne daya faru kamar kiftawan ido Ya mike jikinsa na rawa kansa ya juye ya shake janet Dakyar Dalibai suka ceceta sai da ta kwana asibitin makaranta shi kuma Ya kwashi Littafansa ya koma Inda yake zama Ranar har washegari kansa kamar ba nasa ba sannan lamarin da ya faru ba nasa bane wani Sabon Hali ne da bai sanshi ba yasan bai da Saurin hannu kuma domin Janet tamai kiss ai bai kai ya yi mata abunda yayi mata.

Washegari da yaje dubata tuni akace ta bar asibitin yaje gidan data ke zaune ya iske ta kwashe kayanta ta bar gidan sai daga baya ya samu Labarin ta tsorata da abunda yayi mata ta bar makaranta ta koma garinsu Daga wannan ranar ya rike abun a ransa duk da hakan bai kara Faruwa dashi koda yake daga wannan bai kara rike koda hannun wata macen da ba Muharraminsa ba.

Mujaheeed nata mgana bai ma jisa ba sai da ya taso gabansa ya Dafasa sannan ya dawo Hayyacinsa.

Ya kalli mujaheed da idonsa ya fara Kadawa jikinsa a sanyaye Mujaheed yace"Akwai damuwa ko..?fadamin naji Allah yasa,muna da hanyar warwareta."
Saifudeen yayi saurin kauda kai kafin yace"Mujaheed ka bar wannan mganar ni lafiyata Kalau..Mganar wannan wata aljana chanfi ne ni bazan hanaku yin tunaninku ba,Ammh ka sani ni am fine ba abunda ke Damuna.

Mujaheed na Nazarinsa yace"Kuma ka saki mata har biyu da aka Daura maka..?

Saifudeen ya mike yana Fadin"Bana son su ne kafini sanin bani nace ai ina so ba..Bazan iya zama dasu Allah ya kamani da laifin danne musu hakki ba."
Daga haka kawai ya shige bedroom dinshi ya bar Mujaheed sake da baki Yasan da wani abu domin bai yarda da Saifudeen ba daga mganarsa ya Fahimci akwai wani abu yasan sa da Zurfin ciki,bazai gayamai cikin Sauki ba.,bai matsa ma kansa ba ya juya ya Fice,ya hau motarsa ya fice Daga gidan,koda ya koma gida ya iske Sadiya Cikin Damuwa,bai wani Tsaya maata wata mgana ba ya dai lallasheta da tsawan da yayi mata ammh ita kanta ta tsorata da yanayin Damuwar da muhajeed ya kwana aciki Ta fara tunanin kodai Hamma ne wani abu ya sameshi..?

Sai dai da Safen bayan Mujaheed ya tafi wajen aiki Saifudeeen din ya kirata yana mata godiya sai hankalinta ya kwanta kad'an.
_Na fada muku Salo biyu ne acikin wannan Labarin in salon waje ya fito in da sunan Muhibba ya fito ni zan jagoranci Labarin in kuma Salon ciki ya fito Muhibba zata karbi Ragamar labarin nata ne,Tafiya in tayi tafiya ita zata ja
zaren ta har zuwa karshen Labarinta_
*Littafin Saifuddeen na kudi ne pay N500 via 0552179550 Jamila umar Gt bank,sai a turo evidence of payment ta wannan Lambar 09069067488 ko kuma katin waya na Mtn sai adauki Hoton katin a tura ta wannan Layin kai Tsaye 09069067488 mutanen mu na Niger kuma zasu tuntubi Kausar aglan Nissa ta wannan lambar domin karin bayani +22796562223 Ina maraba da masoya na a duk inda suke*
*Janafty*
*SAIFUDDEEN*
_(Ba mutum ba ne)_
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty*
*Amnaf_sudanese _collection*
*Tana saida original laffaya kala daban daban daga Sudan kama daga na Amare da Kuma casual muna da available a Nigeria kuma Muna aikawa daga Sudan Zuwa Nigeria ko'ina a fadin Jahohi talatin da shida har ila yau dai akwai humra da turarrukka sadidan na matan aure daga Sudan,ba fa anan kada'i muka tsaya ba Muna saida kayan lalle akan sari da Rahusa da kuma siyan Daya,akwai mayuka da dilka da kayan gyaran jiki na ainahin ba Mix ba, wadan'da zasu fitar Miki da fatar ki tas ba bleaching fuskarki tayi haske tayi walwal kina kyalkyali and duk abunda kikeso a Sudan Muna kawo Miki shi har gda Nigeria Amnaf Sudanese collaction ba abunda bama saidawa kama daga kayan kamshin jiki na kaya da na fata +249923097401*
Ya dad'e kafin ya iya cire mganar Mujaheed acikin ransa,saboda yana ganin kamar in ya auna mganarsa da kamshin gaskiya in ya tuna abunda ya faru tsakaninsa da Janet shekarun da suka gabata sai dai kuma shi ba ma'abocin yadda da canfi ne ba ne ko Aminta da irin wad'anan abubuwan na Aljanu ba shiyasa sai ya watsar da mganar yasa a ranshi Bai samu Macen dayake so bane ya tabbata Ranar daya hadu da wacce yake so komai zai zama tarihi.

Dalilin haka ya watsar da mganar Mujaheed da kuma Iya dake chan lere ta Damu kanta ko da yaushe cikin saka Baffa Hashimu take yana kiransa tana jadaddamai ya rika shan mgangunar da ta aikomai dashi ana so in ya shanye yazo su koma wajen malamin Tare yayimai bayanin yanayin dayake ji lokaci daya fara shan mganin jinta kawai yake yi baya gaddama amsar sa daya ce to da shikenan shi ko kalan mganin bai taba gani ba suna cikin Booth din Motarsa Tunda Bama ya karbosu bai bada Umarnin afito dasu ba ballatana yaga kalansu abu daya ya sani bayan Farin ruwa da Tea bazai iya shan kowani Ruwa ba mgani kuma indai ba na asibiti bane bai da alaqa dashi.

Achan bangaran Mujaheed shima bai kara mai mganar ba sai ya kyalesa ganin ya nuna bakomai kuma ya nuna mai a fuska bayason mganar ammh kuma agefe daya mujaheed yasan da wani abu jikinsa bai basa Lafiya Saifuddeen yake ba sai dai da bai sa ikon sanin komai ba sai ya kyalesa ammh aransa ya kuduri tayasa da addu"an koma menene Allah yaye mishi,Shiyasa ko da suka sake Haduwa bai kara tadamai mganar ba sai hankalin Saifudeen ya kwanta har saki jiki suka sha Hiransu,Sannan Ko Ummi in ya kirata korafinta yake yazo yayi aure in kuma ta fara fada sai tace kila ma gaskiyan su Iyan ne Aljannar ce ta auresa shi fa in aka fadi haka Dariya abun ke basa kawai sai Aljannah ta auresa Saboda mene..?Shi kadai ne mutum a wannan Duniya da sai shi..?wannan wani abu ne Feeling kuma shi har yanzu bai ji sa kan wata mace ba shi dai abu daya yake fadama Ummi bai samu wacce yake so bane in ya samu zai yi auran in ta sako mganar su Majeeda sai yace baya son su ne shiyasa ya rabu dasu kada ya zauna dasu domin ya farantamusu gefe daya kuma ya kasa Sauke Nauyin dake kansa,Allah ya kamasa,Ummi in yace haka bata iya mgana sai dai tayi shuru..
********
Bayan Sati Uku.

Jiya da daddare aka wayi gari da rasuwar Diyar Yaya sunusi Rahina,yar kimanin shekara goma sha Daya daga ciwon ciki dare zuwa Safe Saifudeen yana office Ummi ta kirasa ta fadamai za"ayi Jana'iza karfe sha daya na Safe yayi mata gaisuwa yace yana da Taro a lokacin ammh in sun fito da wuri zai kamo Hanya in kuma yammah tayi sai gobe kenan da haka suka Rabu,ya kira kawu a waya yayi mai gaisuwa ya fadamai yadda ya fadama Ummi kawu yace in wani aikin ya rikesa ya bari sai gobe za"a wakilcesa da ga suka ijiye kan waya.

Zuwa chan Mujaheed ya kirasa yana Fadamai zai tafi gaya shi da Sadiya Saifudeen yace sai gobe zai tafi Shi yana da meeting Mujaheed yace shi yau in an kaita gidanta na gaskiya zai Dawo kaduna gobe in yana da Lokaci sai su koma tare.

Kamar ya sani bai samu kansa ba,sai Dare yadai kara kiran Ummi ta bama Umma ya mata gaisuwa tunda Ummi ajiyan ita dasu Laala suka je chan Gaya din Sadiya ma Mujaheed yace chan ya barta zata kwana shi dazu da yammah ya dawo kaduna,Suka shirya tafiyan gobe da wuri shi da Mujaheed saboda ba kwana zasu yi ba aranar zasu dawo kaduna.

Washegari tun takwas da wani abu suka fita a motar Saifudeen suka tafi wannan karon Tim ke Driving din Bama ya kame agidan gaba da wani bakin glass Saifudeen na gidan baya shi da Mujaheed da dukkansu ke sanye da manyan kaya Mujaheed shadda ce mai ruwan toka ajikinsa Har da Hula yayinda Saifuddeen ke sanye da wani sauka'ken yadi mai ruwan madara yana da cake cake ajikinsa sannan bai da wani Karfi Dinkin zamani yayi half Jamper sai dai kansa ba Hula gashinsa ya kwanta Daya sha gyara sau tari Saifudeen zai saka manya kaya ammh hula bata cika Damunsa ba,ba domin yana Tara suma ba, sai hulan ne bata dameahi sosai ba,kuma yana dasu kala kala kafarsa Takakmi ne sawu cikin kalan brown Na Fata mai kyau yana kyalli.

Hira suke yi Jefi jefi yayinda Saifudeen ke rike da Tab dinsa yana Duba karatun da sukayi na wannan Satin da bai samu duba ko Daya ba shima Mujaheed din waya ce a Hannunsa yana dannawa sanin Halin Saifudeen kayi ta mgana yayi kamar bai jika ba...

Sun bar kaduna sun Dumfari Hanyar Gaya Mujaheed kamar wanda ya Tuna wani abu ya dago da Sauri yana kallon Saifuddeen da hankalinsa ya tafi kan abunda yake karantawa Cikin Tab din tasa cikin Tambaya Mujaheed yace"Saifudeen kasan kuwa Director musa ya Kirani shekaran jiya...?

Saifudeen yadda ko motsi bai yi ba sai Mujaheed ya zata bai jisa bane har zai kara maimaita mganarsa sai yaji yace"Ta ina zan san ya Kira ka Tunda ni bai kirani ba."
Yafada hankalinsa na kan abunda yake yi Mujaheed yace"Ko bai kiraka ba nasan ya aiko maka da sakon da nima ya aikomin dashi.

Saifudeen ya tabe baki kafin yace"Wani Sako..?
Chapter 31 · 0% Book details