Sashe 89
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita ta fara zuwa wajen ko dan ta ƙagu su haɗun ne oho. Sai da ta yi kusan Minti shatakwas kafin ya iso.
"Yi haƙuri Dan Allah, sanda kika kira ina wanke Machine ɗina ne da na gama na fito kuma na haɗu da friend ɗina a bakin layi..."
"Ya wuce ai, da ban san hali ba ne sai na yi ƙorafi"
"Da gaske na chanja" yai maganar yana murmushi.
Sai da ya nitsu sosai kafin ta sanar da shi maganar da su ka yi da Mommy.
"CabÉ—i!" Abinda ya furta kenan bayan ya gama sauraron ta.
"CabÉ—i kuma?"
"To mi zan ce, abin ne na ji banbaraƙwai. Yanzu Mommy ta ina ma take so ki fara?"
"Wallahi ban sani ba Ya Auwal. Ita gani take abu ne mai sauƙi kuma case ɗin nan babban sauƙi ne"
"Gaskiya kam. Duk ban san dalilin ta na cewa ki jagoranci case ɗin nan ba amma gaskiyar magana shine indai ki ka ɗau case ɗin nan ba inda za aje za a kori ƙarar nan"
Zaytoonan ta haÉ—e rai ta ce "irin ka rena ni É—in nan"
"Sorry Dear, kin san ke É—in JJC ce"
Zaytoonah ta murguÉ—a ma sa baki...
Duk da Auwal ya sa baki Mommy ba ta chanja magana ba, abu ɗaya ta jaddada mu su. Ko dai Zaytoonah ta jagoranci case ɗin ko kuma ta haƙura da case ɗin har abada. Wannan ya sa jikin Zaytoonah yai sanyi, ta kuma ɗaura aniyar bin umurnin Mommy duk da tana hango mu su rashin nasara a case ɗin.
"Mommy na amince" ta faÉ—i maganar lokacin da Mommyn ke shirin kwanciya. Jin ba ta tanka ma ta ba ne ya sa ta sake maimaita maganar "Mommy na amince zan jagoranci case É—in nan"
Wannan karan Mommy ta kalleta briefly kafin ta É—auke ido ta ce "Allah ya shige mana gaba"
Zaytoonah ta amsa da Amin.
Washegari Mommy ta sanar da ita details É—in yadda take son komai ya tafi. It wasnt easy kamar yadda tayi hasashe É—in.
"Mommy gani da ke a gida amma sai kin tura ni wajen wani yayi coaching ɗina" ta yi maganar tana flipping ƙwan da ke cikin Pan yayinda Mommy ke juye ruwan tea cikin flask.
"Yaushe rabon na yi zaman kotu, ni yanzu ai Malama ce"
Zaytoonah ta sa dariya " Malama Mommy kenan"
"Ki faÉ—a da kyau dan hakan ta ke"
"GrandMa! Hashir is not brushing his teeth very well" muryan Hadid ya katse mu su hiran.
Mommy ta ce "to kinga É—alibai na nan"
Zaytoonah ta sa dariya...
***
Ta kai minti biyar tana tuƙa da warwara kan yadda za ta tura text message. Ba za ta iya kiran sa ba gaskiya dan tsoron harka da manyan mutane ta ke yi musamman ma shi da aka ce ma ta mai sarauta ne. Daga ƙarshe kawai ta tura ma sa *fatan an wuni lafiya, Bar. Zaytoonah ce wacce za ta zo wajen ka ranan Monday* ko yayi ko bai yi ba ita dai ta riga ta tura. Kamar yadda ba ta tsammanci reply ba hakanan har rana ta faɗi ba ta ga reply ɗinsa ba duk da kuwa tanada yaƙinin cewa ya ga message ɗin.
Haka dai ta shirya ta wuce Abuja yammacin ranan Lahdi kuma har lokacin ba ta ji daga gareshi ba. A gidan Muhsina ta sauka duk da kuwa akwai wasu 'yan uwan Zuhayr a Abujan amma gidan Muhsina ya fi mata saboda tafi sakewa a gidan. Mijin ta yanzu baya ƙasar ya je yin Phd ɗin sa a South Africa. Gidan daga ita sai 'ya'yan ta guda biyu Nabil da Aysha sai kuma Azma ƙanwar mijinta da ke tayata kwana.
Ba ta san ya aka yi baccin ta yai nauyi har haka ba, dan ko bugawar alarm ba ta ji ba. Sanda ta tashi har ƙarfe bakwai na safe ta shige da 'yan mintuna.
"Shine ba ki tasheni ba" ta faÉ—awa Muhsina da ke shirin kai yara Makaranta.
"Au ni fa har na manta yau za ki fara fita"
"Wannan yawan mantuwa na ki anya????"
"Rufa min asiri yaushe Abban Nabil ya zo gida"
"Na sani ko lokacin da ki ka je ma sa ziyara kin taho da tsaraba" Zaytoonah ta yi maganar tana dariya.
"Ki dai ƙaraci gulman ki ni banida komai".
Tare su ka karya da Azma dan itama sai lokacin ta ke tashi. Ba ta zuwa ko'ina dan tun lokacin da ta yi jarrabawan WAEC ta dawo Abuja da zama, ko jarrabawar JAMB da ta yi ma a nan É—in ta yi.
Lokacin da Zaytoonah ta isa Chamber ɗin ƙarfe goma har da rabi. Ita kanta ta san ba ta kyauta ba balle kuma wanda za ta je wajen na sa. Gaskiya wajen ya tsaru iya tsaruwa sai dai taste ɗin su wajen furnitures bai ma ta ba.
A wajen Sakatare ta zauna tana jiran tsammanin man Rabbuka bayan ya shaida ma ta ta jira Honorable yana aiki. Tun tana duba agogo har ta haƙura kawai ta cigaba da buga game a wayarta.
Minti talatin da biyu cur ta yi a wajen kafin Sakataren ya ce ta shiga office É—in.
Office ne mai girma da ya wadatu da shelves wanda ke cike da manyan litattafai. Ta kai duban ta ga mamallakin office ɗin wanda ke zaune akan kujera yana nazarin wasu litattafai guda uku da ke gaban sa. Mutumin da aka kira da Justice Yunus Muhammad Abbas fari ne sosai, yanayin farin sa yana zubi da Larabawa, furfura daya wadaci sajen sa da gemun sa shi zai sa ka ma sa tunanin shekaru irin sittin ɗin nan amma a zahiri shekarun sa Arba'in da shida ne. Allah dai ya bashi baiwar furfuran ne, hatta gashin kan sa kusan rabi da furfuran. Sanye ya ke da baƙin suit, da ke a buɗe ta ke kana ganin farin shirt ɗin da ke ciki. Ko bai sa tie ba ne ko dai ya cire dan ba ta ga tie a wuyan sa ba.
"Good morning Sir" ta bashi 'yan sakanni amma ta ga shiru bai amsa ba, ta ɗan ƙara ɗaga murya ta ce "Barrister Zaytoonah Tijjani Abubakar Sir"
Still shiru bai yi magana ba bai kuma É—ago ya kalleta ba.
Tsaki ta yi a ranta tana faÉ—in Girman kai rawanin tsiya.
Ba za ta manta walaƙanci da ya mu su ba ranan da su ka haɗu a gidan sa, bai yaba aikin su ba, bai ma nuna ya ji daɗin aikin ba. Yana gama dubawa da ya sauko ƙasa lokacin suna hira da Hajiya Ni'ima ya ce "Hajiya Ni'ima a tambaye su nawa ne kuɗin su" daga haka ya fice a falon, tana ma shirin gaishe shi ne amma jin abinda ya faɗa ya sa ta ja bakin ta tayi shiru. Tsabar haushi ma ranan ƙin ba da account number ɗin ta tayi sai kawai ta bada business account na kamfanin Alhaji Ibrahim. Kuɗin ma yafewa ta yi, dan da su ka yi magana da Alhaji Ibrahim ce ma sa tayi payment ɗin kaya ne dana sauran ma'aikatan da su ka tayata aiki ita ta cire na ta.
"Sarauta my foot" ta faÉ—i a zuciyarta haÉ—eda yin tsaki.
Tun tana sa ran zai yi magana har ta gaji, ta yi yunƙurin magana for the last time dan ta yi Alƙawarin daga wannan kam tafiyarta za ta yi ta fasa koyon aiki a wajen sa. Ita kam yadda Mommy ta yi ta yabon wannan mutumin exactly opposite ɗin sa ta gani. A hakan wai Mommy ta yi aiki ƙarƙashin sa lokacin yana Judge of High court Kaduna.
"Sir ni ce wacce Barrister Maryam Nkiru ta maka magana akan za..."
"Idan kin koyi zuwa da wuri sai mu É—aura daga nan" abinda ya faÉ—a kenan still idon sa na kan littafi. Yadda yai maganar kamar ma ba da ita ya ke ba...
"Mommy Allah yana da girman kai, ko fa amsa gaisuwata bai yi ba"
Daga ɓangaren Mommy ta ce " ke ma laifin ki ne ai da ki ka je a makare. Barin gaya miki shi mutum ne mai tsari bai yadda da wasa da lokaci ba"
"Duk tsarin sa ai ba zai hana ya amsa common gaisuwa ba. Mommy ko kallona fa bai yi ba"
Mommy ta yi dariya ta ce "to Zaytoonah ya kalleki na me kenan?"
"Allah ni kam ki chanja min wani ba abinda zan koya a wajen sa sai girman kai"
"Idan ki ka nitsu ki ka fahimce shi Wallahi shi mutum ne mai sauƙin sha'ani"
"Ina ga dai shekarun baya kenan da kika yi aiki da shi, yanzu kam ya chanja"
"Galadima ba shi da girman kai Zaytoonah, wannan kam zan ma sa shaida akai"
Duk da Mommy ta faÉ—a ma ta haka itakam ba ta yarda ba tunda ta ga zahiri ba sau É—aya ba har sau biyu...
***
Bai koma gida da wuri ba sai bayan sallar Maghriba. Da sallama ya shigo falon yayinda fiskar sa ke É—auke da Murmushi. Falaq da Suhailah su ka yo wajen sa da gudu su ka rungume shi.
Sai da ya kissing goshin su kafin ya kama hannun su duka biyu su ka ƙariso wajen da Hajia Ghazala da Raziya ke zaune.
"Ranka shi daÉ—e, barka da dawowa"
"Sannu da ƙoƙari" yai maganar yana tambayar Raziya ya jiki ta ce ma sa da sauƙi. Daren jiya bai samu yayi bacci ba saboda ciwon cikin da Raziya ta tashi da shi tsakar dare. Da su ka je Asibiti ne ake faɗa ma sa ai ciwon cikin period ne. Ashe 'yar ta sa an zama budurwa.
Tunda safe kuwa da Hajia Ghazala ta ji labari ta zo ta tare a gidan. Tuntuni take son tafiya amma kuma ba ta saka Galadima a ido ba ba abinda zai sa ta tafi dan haka ta cigaba da zama da yaran.
Wanka yai ya chanja kaya zuwa baƙar Jallabiya sannan ya fito dan ya wuce masallaci sai a lokacin ne Hajia Ghazala ke shirin tafiya. Bayan Allah ya kiyaye hanya da ya ma ta bai kuma cewa komai ba.
"Yi haƙuri Dan Allah, sanda kika kira ina wanke Machine ɗina ne da na gama na fito kuma na haɗu da friend ɗina a bakin layi..."
"Ya wuce ai, da ban san hali ba ne sai na yi ƙorafi"
"Da gaske na chanja" yai maganar yana murmushi.
Sai da ya nitsu sosai kafin ta sanar da shi maganar da su ka yi da Mommy.
"CabÉ—i!" Abinda ya furta kenan bayan ya gama sauraron ta.
"CabÉ—i kuma?"
"To mi zan ce, abin ne na ji banbaraƙwai. Yanzu Mommy ta ina ma take so ki fara?"
"Wallahi ban sani ba Ya Auwal. Ita gani take abu ne mai sauƙi kuma case ɗin nan babban sauƙi ne"
"Gaskiya kam. Duk ban san dalilin ta na cewa ki jagoranci case ɗin nan ba amma gaskiyar magana shine indai ki ka ɗau case ɗin nan ba inda za aje za a kori ƙarar nan"
Zaytoonan ta haÉ—e rai ta ce "irin ka rena ni É—in nan"
"Sorry Dear, kin san ke É—in JJC ce"
Zaytoonah ta murguÉ—a ma sa baki...
Duk da Auwal ya sa baki Mommy ba ta chanja magana ba, abu ɗaya ta jaddada mu su. Ko dai Zaytoonah ta jagoranci case ɗin ko kuma ta haƙura da case ɗin har abada. Wannan ya sa jikin Zaytoonah yai sanyi, ta kuma ɗaura aniyar bin umurnin Mommy duk da tana hango mu su rashin nasara a case ɗin.
"Mommy na amince" ta faÉ—i maganar lokacin da Mommyn ke shirin kwanciya. Jin ba ta tanka ma ta ba ne ya sa ta sake maimaita maganar "Mommy na amince zan jagoranci case É—in nan"
Wannan karan Mommy ta kalleta briefly kafin ta É—auke ido ta ce "Allah ya shige mana gaba"
Zaytoonah ta amsa da Amin.
Washegari Mommy ta sanar da ita details É—in yadda take son komai ya tafi. It wasnt easy kamar yadda tayi hasashe É—in.
"Mommy gani da ke a gida amma sai kin tura ni wajen wani yayi coaching ɗina" ta yi maganar tana flipping ƙwan da ke cikin Pan yayinda Mommy ke juye ruwan tea cikin flask.
"Yaushe rabon na yi zaman kotu, ni yanzu ai Malama ce"
Zaytoonah ta sa dariya " Malama Mommy kenan"
"Ki faÉ—a da kyau dan hakan ta ke"
"GrandMa! Hashir is not brushing his teeth very well" muryan Hadid ya katse mu su hiran.
Mommy ta ce "to kinga É—alibai na nan"
Zaytoonah ta sa dariya...
***
Ta kai minti biyar tana tuƙa da warwara kan yadda za ta tura text message. Ba za ta iya kiran sa ba gaskiya dan tsoron harka da manyan mutane ta ke yi musamman ma shi da aka ce ma ta mai sarauta ne. Daga ƙarshe kawai ta tura ma sa *fatan an wuni lafiya, Bar. Zaytoonah ce wacce za ta zo wajen ka ranan Monday* ko yayi ko bai yi ba ita dai ta riga ta tura. Kamar yadda ba ta tsammanci reply ba hakanan har rana ta faɗi ba ta ga reply ɗinsa ba duk da kuwa tanada yaƙinin cewa ya ga message ɗin.
Haka dai ta shirya ta wuce Abuja yammacin ranan Lahdi kuma har lokacin ba ta ji daga gareshi ba. A gidan Muhsina ta sauka duk da kuwa akwai wasu 'yan uwan Zuhayr a Abujan amma gidan Muhsina ya fi mata saboda tafi sakewa a gidan. Mijin ta yanzu baya ƙasar ya je yin Phd ɗin sa a South Africa. Gidan daga ita sai 'ya'yan ta guda biyu Nabil da Aysha sai kuma Azma ƙanwar mijinta da ke tayata kwana.
Ba ta san ya aka yi baccin ta yai nauyi har haka ba, dan ko bugawar alarm ba ta ji ba. Sanda ta tashi har ƙarfe bakwai na safe ta shige da 'yan mintuna.
"Shine ba ki tasheni ba" ta faÉ—awa Muhsina da ke shirin kai yara Makaranta.
"Au ni fa har na manta yau za ki fara fita"
"Wannan yawan mantuwa na ki anya????"
"Rufa min asiri yaushe Abban Nabil ya zo gida"
"Na sani ko lokacin da ki ka je ma sa ziyara kin taho da tsaraba" Zaytoonah ta yi maganar tana dariya.
"Ki dai ƙaraci gulman ki ni banida komai".
Tare su ka karya da Azma dan itama sai lokacin ta ke tashi. Ba ta zuwa ko'ina dan tun lokacin da ta yi jarrabawan WAEC ta dawo Abuja da zama, ko jarrabawar JAMB da ta yi ma a nan É—in ta yi.
Lokacin da Zaytoonah ta isa Chamber ɗin ƙarfe goma har da rabi. Ita kanta ta san ba ta kyauta ba balle kuma wanda za ta je wajen na sa. Gaskiya wajen ya tsaru iya tsaruwa sai dai taste ɗin su wajen furnitures bai ma ta ba.
A wajen Sakatare ta zauna tana jiran tsammanin man Rabbuka bayan ya shaida ma ta ta jira Honorable yana aiki. Tun tana duba agogo har ta haƙura kawai ta cigaba da buga game a wayarta.
Minti talatin da biyu cur ta yi a wajen kafin Sakataren ya ce ta shiga office É—in.
Office ne mai girma da ya wadatu da shelves wanda ke cike da manyan litattafai. Ta kai duban ta ga mamallakin office ɗin wanda ke zaune akan kujera yana nazarin wasu litattafai guda uku da ke gaban sa. Mutumin da aka kira da Justice Yunus Muhammad Abbas fari ne sosai, yanayin farin sa yana zubi da Larabawa, furfura daya wadaci sajen sa da gemun sa shi zai sa ka ma sa tunanin shekaru irin sittin ɗin nan amma a zahiri shekarun sa Arba'in da shida ne. Allah dai ya bashi baiwar furfuran ne, hatta gashin kan sa kusan rabi da furfuran. Sanye ya ke da baƙin suit, da ke a buɗe ta ke kana ganin farin shirt ɗin da ke ciki. Ko bai sa tie ba ne ko dai ya cire dan ba ta ga tie a wuyan sa ba.
"Good morning Sir" ta bashi 'yan sakanni amma ta ga shiru bai amsa ba, ta ɗan ƙara ɗaga murya ta ce "Barrister Zaytoonah Tijjani Abubakar Sir"
Still shiru bai yi magana ba bai kuma É—ago ya kalleta ba.
Tsaki ta yi a ranta tana faÉ—in Girman kai rawanin tsiya.
Ba za ta manta walaƙanci da ya mu su ba ranan da su ka haɗu a gidan sa, bai yaba aikin su ba, bai ma nuna ya ji daɗin aikin ba. Yana gama dubawa da ya sauko ƙasa lokacin suna hira da Hajiya Ni'ima ya ce "Hajiya Ni'ima a tambaye su nawa ne kuɗin su" daga haka ya fice a falon, tana ma shirin gaishe shi ne amma jin abinda ya faɗa ya sa ta ja bakin ta tayi shiru. Tsabar haushi ma ranan ƙin ba da account number ɗin ta tayi sai kawai ta bada business account na kamfanin Alhaji Ibrahim. Kuɗin ma yafewa ta yi, dan da su ka yi magana da Alhaji Ibrahim ce ma sa tayi payment ɗin kaya ne dana sauran ma'aikatan da su ka tayata aiki ita ta cire na ta.
"Sarauta my foot" ta faÉ—i a zuciyarta haÉ—eda yin tsaki.
Tun tana sa ran zai yi magana har ta gaji, ta yi yunƙurin magana for the last time dan ta yi Alƙawarin daga wannan kam tafiyarta za ta yi ta fasa koyon aiki a wajen sa. Ita kam yadda Mommy ta yi ta yabon wannan mutumin exactly opposite ɗin sa ta gani. A hakan wai Mommy ta yi aiki ƙarƙashin sa lokacin yana Judge of High court Kaduna.
"Sir ni ce wacce Barrister Maryam Nkiru ta maka magana akan za..."
"Idan kin koyi zuwa da wuri sai mu É—aura daga nan" abinda ya faÉ—a kenan still idon sa na kan littafi. Yadda yai maganar kamar ma ba da ita ya ke ba...
"Mommy Allah yana da girman kai, ko fa amsa gaisuwata bai yi ba"
Daga ɓangaren Mommy ta ce " ke ma laifin ki ne ai da ki ka je a makare. Barin gaya miki shi mutum ne mai tsari bai yadda da wasa da lokaci ba"
"Duk tsarin sa ai ba zai hana ya amsa common gaisuwa ba. Mommy ko kallona fa bai yi ba"
Mommy ta yi dariya ta ce "to Zaytoonah ya kalleki na me kenan?"
"Allah ni kam ki chanja min wani ba abinda zan koya a wajen sa sai girman kai"
"Idan ki ka nitsu ki ka fahimce shi Wallahi shi mutum ne mai sauƙin sha'ani"
"Ina ga dai shekarun baya kenan da kika yi aiki da shi, yanzu kam ya chanja"
"Galadima ba shi da girman kai Zaytoonah, wannan kam zan ma sa shaida akai"
Duk da Mommy ta faÉ—a ma ta haka itakam ba ta yarda ba tunda ta ga zahiri ba sau É—aya ba har sau biyu...
***
Bai koma gida da wuri ba sai bayan sallar Maghriba. Da sallama ya shigo falon yayinda fiskar sa ke É—auke da Murmushi. Falaq da Suhailah su ka yo wajen sa da gudu su ka rungume shi.
Sai da ya kissing goshin su kafin ya kama hannun su duka biyu su ka ƙariso wajen da Hajia Ghazala da Raziya ke zaune.
"Ranka shi daÉ—e, barka da dawowa"
"Sannu da ƙoƙari" yai maganar yana tambayar Raziya ya jiki ta ce ma sa da sauƙi. Daren jiya bai samu yayi bacci ba saboda ciwon cikin da Raziya ta tashi da shi tsakar dare. Da su ka je Asibiti ne ake faɗa ma sa ai ciwon cikin period ne. Ashe 'yar ta sa an zama budurwa.
Tunda safe kuwa da Hajia Ghazala ta ji labari ta zo ta tare a gidan. Tuntuni take son tafiya amma kuma ba ta saka Galadima a ido ba ba abinda zai sa ta tafi dan haka ta cigaba da zama da yaran.
Wanka yai ya chanja kaya zuwa baƙar Jallabiya sannan ya fito dan ya wuce masallaci sai a lokacin ne Hajia Ghazala ke shirin tafiya. Bayan Allah ya kiyaye hanya da ya ma ta bai kuma cewa komai ba.