Sashe 121
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Raziya wannan hutun zan coaching É—in ki akan basic Mathematics. With that ba za ki samu matsala ba Insha Allah. Kwana huÉ—u a sati ya mi ki?"
Raziya ta watsawa Zaytoonah harara ganin hankalin Justice yana kan waya.
"Kwana É—aya ya isa" ta faÉ—a fiskarta a haÉ—e
"5 days Raziya, and ban da rashin kunya"
"Daddy"
"Je ki adana result É—in a file É—in ki"
"Yes Dad" ta faɗa tareda karɓan result ɗin a hannun Zaytoonah.
Sai da ta fita Justice ya kamo hannun Zaytoonah ya ma ta kiss ya ce "Na gode" Zaytoonah ta yi murmushi ta ce "My prince kar ka damu Insha Allah zan yi ƙoƙarina a kan ta"...
***
"Hello" ta faɗa lokacin da ta amsa kiran baƙuwar number mai code ɗin ƙasar America
"Zaytoonah"
"Ya Allah! Muhsinah ya ki ke. Ya su Daddy"
"Mu na nan lafiya. Ina 'ya'ya na?"
"Sun tafi Islamiyya"
"Kwana biyu 'yar uwa, ya ki ke? hope kuna zune lafiya da kishiyar ki"
"To gamu nan dai, kin san mi ta yi kwanan nan. Wani sharri ta zo da shi wai tanada infection kuma daga wajena aka samu"
"Haba!"
"Wallahi. That crazy woman actually thinks i'm stupid fa"
"To ai ke ki ka ba ta dama"
"A da kenan yanzu na yi hankali"
Muhsinah ta kwashe da dariya. Sai da ta gama ba ta labarin yadda su ka wanye da Ghazala kafin ta sako ma ta tambayar da ta sa Muhsinar É—auke wuta.
"Maman Habib ki koma dan Allah. I know its not easy but forgive him please"
Sai da ta yi kusan 30 seconds kafin ta sauke numfashi ta ce "i cant Zaytoonah. Ba zan iya ba, its over"
"Kin zaɓi ki rabu da shi har abada kenan. What about your kids?"
"Ba zan iya ba" ta furta tareda kashe wayar.
Sosai Zaytoonah ta ke tausayawa Muhsinah. Rabuwa da Miji ba abu ne mai sauƙi ba especially idan kana son shi. Despite the fact AbdulHameed ya ƙi ya saketa, Muhsinah ta rantse ba za ta koma ba, bayan ta warke tattarewa ta yi ta koma America wajen Baban ta. Yaran kuma na nan wajen Kakannin su.
Shigowar Justice É—akin ne ya katse ma ta tunani.
"Ba dai fita za ka yi ba?"
"Za ki yi missing É—ina ko"
"Na ga ba ka jima da dawowa ba ne"
"Jiya ya kamata na je na yi yankan farce amma na manta, yau ma sai da na shigo na tuna"
Ta sa hannu a kafaÉ—un sa tana faÉ—in "wannan Tsoho ba dai mantuwa ba, anya idan ka fi haka ba da sanda za mu haÉ—a ka ba"
Ya ɗaura hannun sa a ƙugunta ya jawota jikinsa ya ce "idan ke ce 'yar jagorar i dont mind"
Dariya ta yi tana faÉ—in ba zai ma kai haka ba.
"Na iya yankan farce fa. If you dont mind i could do it for you"
"Ofcourse Sweetheart"
Ta kamo hannun sa ta zaunar da shi kan kujera sannan ta ɗauko kayan aiki tareda ƙaramar towel. Ta zauna ƙasa ta ɗaura ƙafarsa akan ƙafarta ta fara yanke ma sa farcen.
"Ka san a ina na koyi aikin nan?"
Ta tambaya lokacin da ta gama ƙafa ɗaya ta fara ɗaya ƙafar.
A zaton sa sunan mijin ta za ta kira sai ya ji ta ce
"A ƙafar Daddy na" ta yi murmushi ta ce "Mommy ce ke ma sa, sai ranan su ka yi faɗa, dan ya ƙula ta sai ya kirani ya ce na ma sa. The truth is ya sha yanka a wajena ranan. But still bai haƙura ba, ya ce dole sai ni zan ƙarisa ma sa.
"Daga nan kuma ya maida shi permanent ni ke ma sa yankan farce, tun ban iya ba har na ƙware"
Hawaye ne ya fara zubo ma ta ta yi saurin gogewa amma ina tana gogewa wani na bin wani.
"I miss him" ta faÉ—a lokacin da ya jawota jikin sa.
Sun jima a haka kafin ta janye jikin ta ta ce bari ta ƙarisa ma sa yankan.
***
Wannan karan dukkan su suka je weekend Zaria. Tun ranan Alhamis su ka tafi, ranan Jummu'a akwai Public holiday da aka bayar na Maulidi shiyasa dukkan su su ka taho tunda ba aiki sai ran Talata.
Ranan Jummu'ah ya kama ranan kwanan Ghazala, da ke Galadima ya ba da umurnin ayi abincin sadaka gaba ɗaya aka haɗa hannu ake yi. Suna cikin aiki, sauran ma su aiki aka fara taɗi ana habaici ƙasa-ƙasa. Da farko Zaytoonah ba ta gane da ita ake ba sai da ta ji Baaba Nafy ta ce "ku ji tsoron Allah. A wajen mu matsayi ɗaya su ke da shi tunda dukkan su ƙarƙashin inuwar Yallaɓai su ke"
Baaba Nafy ba sa'ar su ba ce dan ko Ghazalar za ta ba ta kusan shekaru shatakwas zuwa ishirin.
Zaytoonah ta É—ago ido ta kalli Ghazala da ke yanka cabbage sai wani murmushi ta ke yi.
Kamar za ta yi magana sai kuma ta yi shiru dan biye mu su ma ɓata lokaci ne, dan ba girmanta ba ne.
"Ai ba mu san Yallaɓai ya yi aure ba sai da haske ta shigo gidan nan, tauraruwar Galadima Allah ya ja zamanin ki"
Wata mata ta faÉ—a wanda ko sunan ta Zaytoonah ba ta sani ba.
"Allah ya kawo Magajin gida nan da wata tara Amin"
Murmushin fiskar Ghazala ya É—auke É—if kamar É—aukewar wutan NEPA.
Zaytoonah ta kauda kan ta kamar ba ta ji abinda aka faÉ—a ba.
Abubuwa da dama su ka dinga yawo a kwanyar Ghazala. Maganar Magaji ya taɓa ta sosai, ba wai ta wuce shekarun haihuwa ba ne amma kuma propability ɗin samun ciki is very low compared to Zaytoonah wacce yanzu ne ma ta cika shekara ashirin da huɗu a duniya. Idan ba ta manta ba haihuwar ta na biyu ta yi allurar tazarar haihuwa saboda lokacin ba ta son cigaba da haihuwa da Alhaji Bashir. Shekara ɗaya da yin hakan ma ta rabu da shi.
Suma ma su yiwa Ghazala kirarin da su ka ga ta haÉ—e rai sai su ka yi shiru...
Yau tun safe ba su da wuta, kamar wutan anguwar ta su ne ta samu matsala. Tun ƙarfe biyar na yamma aka tada generator ya ke ta aiki.
Ƙarfe takwas na dare Zaytoonah ta shiga wanka. Yau kwanan ta ne, zuwa ƙarfe tara ta san Galadima zai dawo daga Fada.
Ta fito daga wanka tana shafa mai Generator ya mutu.
Da sauri ta fara laluben wayan ta dan ta haska ɗakin kawai wayar ta faɗi ƙasa, ta tsugunna ta lalubo wayar tana ƙoƙarin kunna shi kawai ta ji kamar an taɓa ma ta baya nan da nan ta ƙwalla ƙara, jikinta ya fara ƙyarma.
"Ben dont kill me, please dont kill me"
Ta faɗa tana yin baya-baya saboda Ben kawai ta ke gani a idonta yana riƙe da bindiga.
Raziya da Hajiya Ghazala ne su ka shigo É—akin da gudu.
"Zaytoonah" Ghazala ta kira tana haskata da wayarta.
"Zuhayr help me, save me D, save me" abinda ta ke faɗi kenan har lokacin jikinta na ɓari.
"Anty Zaytoonah" Raziya ta faÉ—a tana matsawa kusa da ita.
"Raziya ki matsa ƙila Aljanu gareta. Je ki kira Baba Maigadi a zo ma ta ruƙiyya"
Ta faÉ—a tana janye Raziya daga wajen. Dukkan su fita su ka yi daga É—akin su ka bar Zaytoonah a wajen tana cigaba da sunbatu.
Raziya ta yi ƙasa da gudu yayinda Ghazala ta shiga kiran numbar Justice.
ÆŠaya daga cikin dogarai ma su tsaron gidan Raziya ta samu ta gaya ma sa ya zo inji Ghazala, Aljanun Zaytoonah sun tashi.
Da farko ya so ƙin shiga dan iyakar sa tsakar gidan sai kuma falon Justice da ke ƙasa idan ya buƙaci ganin su. Sai dai yadda Raziyan ta ke magiya ya sa shi bin bayanta da sauri.
Yana shiga ya tadda Ghazala a falon ƙasa tana waya.
"Wallahi hauka tuburan ta ke yi Hajiya. Yanzu dai na sa an kira dogari zai ma ta ruƙiyya"
Daga ɓangaren Hajiya Abu ta ce "Kul, banda wannan ganganci. Kar namijin da ya shiga wajen ta. Ku dai bar ta a ɗakin zuwa Galadima ya iso"
Ghazala ta amsa da toh.
Cewa dogarin ta yi ya tsaya a wajen zuwa Galadima ya iso saboda kar Zaytoonah ta fito ta mu su wani abin.
"Hajiya su Falaq na É—aki"
"Na tura Baaba Nafy wajen su"
Ai ba ta tsaya jin maganar ba ta haura saman.
Ganin É—akin Zaytoonah a buÉ—e kuma tana jin muryan su Hadid ya sa ta wuce wajen.
"Mom its me Hadid"
"Mom please ba kowa a nan mu ne kawai. Ni da Hadid ne"
Zuwa lokacin É—akin ya É—au haske saboda torchlight da kuma wayar da Baaba Nafy ta kunna. Tana haurowa sama ta samu 'yan biyu da Falaq a É—akin.
A hankali Zaytoonah ta fara sauke numfashi ganin da gaske dai 'ya'yanta ne a gaban ta...
Da sauri-sauri Galadima ya shigo gidan har lokacin Ghazala na zaune a falon ƙasa.
"Ina ta ke?" Ya faɗa da ƙarfi.
ÆŠakin ta.
Yana wucewa itama ta bi bayan shi da sauri.
Lokacin Zaytoonah ta samu nitsuwa, tana zaune a kan gado sun sata a tsakiya.
Shigowar sa É—akin ya sa Baaba Nafy ta ja hannun Falaq da Raziya su ka bar É—akin.
"Are you Ok"
"I'm sorry" ta furta a hankali.
"Sannu ya jikin?Baaba Nafy ne ta miki ruƙiyya?"
Irin kallon da Justice ya watsa ma ta ne ya sa ta yi shiru. Ta juya ta fice daga É—akin...
Bayan ya lallaɓa Zaytoonah ta yi bacci tukunna ya fito ya hau ma su aiki da masifa kan ta ya za a bari generator ya mutu, duk da zuwa lokacin an gyara amma a hakan sai da yai ta faɗa. Su kan su sun yi mamakin wannan faɗan dan ba halin Galadima ba ne.
***
Raziya ta watsawa Zaytoonah harara ganin hankalin Justice yana kan waya.
"Kwana É—aya ya isa" ta faÉ—a fiskarta a haÉ—e
"5 days Raziya, and ban da rashin kunya"
"Daddy"
"Je ki adana result É—in a file É—in ki"
"Yes Dad" ta faɗa tareda karɓan result ɗin a hannun Zaytoonah.
Sai da ta fita Justice ya kamo hannun Zaytoonah ya ma ta kiss ya ce "Na gode" Zaytoonah ta yi murmushi ta ce "My prince kar ka damu Insha Allah zan yi ƙoƙarina a kan ta"...
***
"Hello" ta faɗa lokacin da ta amsa kiran baƙuwar number mai code ɗin ƙasar America
"Zaytoonah"
"Ya Allah! Muhsinah ya ki ke. Ya su Daddy"
"Mu na nan lafiya. Ina 'ya'ya na?"
"Sun tafi Islamiyya"
"Kwana biyu 'yar uwa, ya ki ke? hope kuna zune lafiya da kishiyar ki"
"To gamu nan dai, kin san mi ta yi kwanan nan. Wani sharri ta zo da shi wai tanada infection kuma daga wajena aka samu"
"Haba!"
"Wallahi. That crazy woman actually thinks i'm stupid fa"
"To ai ke ki ka ba ta dama"
"A da kenan yanzu na yi hankali"
Muhsinah ta kwashe da dariya. Sai da ta gama ba ta labarin yadda su ka wanye da Ghazala kafin ta sako ma ta tambayar da ta sa Muhsinar É—auke wuta.
"Maman Habib ki koma dan Allah. I know its not easy but forgive him please"
Sai da ta yi kusan 30 seconds kafin ta sauke numfashi ta ce "i cant Zaytoonah. Ba zan iya ba, its over"
"Kin zaɓi ki rabu da shi har abada kenan. What about your kids?"
"Ba zan iya ba" ta furta tareda kashe wayar.
Sosai Zaytoonah ta ke tausayawa Muhsinah. Rabuwa da Miji ba abu ne mai sauƙi ba especially idan kana son shi. Despite the fact AbdulHameed ya ƙi ya saketa, Muhsinah ta rantse ba za ta koma ba, bayan ta warke tattarewa ta yi ta koma America wajen Baban ta. Yaran kuma na nan wajen Kakannin su.
Shigowar Justice É—akin ne ya katse ma ta tunani.
"Ba dai fita za ka yi ba?"
"Za ki yi missing É—ina ko"
"Na ga ba ka jima da dawowa ba ne"
"Jiya ya kamata na je na yi yankan farce amma na manta, yau ma sai da na shigo na tuna"
Ta sa hannu a kafaÉ—un sa tana faÉ—in "wannan Tsoho ba dai mantuwa ba, anya idan ka fi haka ba da sanda za mu haÉ—a ka ba"
Ya ɗaura hannun sa a ƙugunta ya jawota jikinsa ya ce "idan ke ce 'yar jagorar i dont mind"
Dariya ta yi tana faÉ—in ba zai ma kai haka ba.
"Na iya yankan farce fa. If you dont mind i could do it for you"
"Ofcourse Sweetheart"
Ta kamo hannun sa ta zaunar da shi kan kujera sannan ta ɗauko kayan aiki tareda ƙaramar towel. Ta zauna ƙasa ta ɗaura ƙafarsa akan ƙafarta ta fara yanke ma sa farcen.
"Ka san a ina na koyi aikin nan?"
Ta tambaya lokacin da ta gama ƙafa ɗaya ta fara ɗaya ƙafar.
A zaton sa sunan mijin ta za ta kira sai ya ji ta ce
"A ƙafar Daddy na" ta yi murmushi ta ce "Mommy ce ke ma sa, sai ranan su ka yi faɗa, dan ya ƙula ta sai ya kirani ya ce na ma sa. The truth is ya sha yanka a wajena ranan. But still bai haƙura ba, ya ce dole sai ni zan ƙarisa ma sa.
"Daga nan kuma ya maida shi permanent ni ke ma sa yankan farce, tun ban iya ba har na ƙware"
Hawaye ne ya fara zubo ma ta ta yi saurin gogewa amma ina tana gogewa wani na bin wani.
"I miss him" ta faÉ—a lokacin da ya jawota jikin sa.
Sun jima a haka kafin ta janye jikin ta ta ce bari ta ƙarisa ma sa yankan.
***
Wannan karan dukkan su suka je weekend Zaria. Tun ranan Alhamis su ka tafi, ranan Jummu'a akwai Public holiday da aka bayar na Maulidi shiyasa dukkan su su ka taho tunda ba aiki sai ran Talata.
Ranan Jummu'ah ya kama ranan kwanan Ghazala, da ke Galadima ya ba da umurnin ayi abincin sadaka gaba ɗaya aka haɗa hannu ake yi. Suna cikin aiki, sauran ma su aiki aka fara taɗi ana habaici ƙasa-ƙasa. Da farko Zaytoonah ba ta gane da ita ake ba sai da ta ji Baaba Nafy ta ce "ku ji tsoron Allah. A wajen mu matsayi ɗaya su ke da shi tunda dukkan su ƙarƙashin inuwar Yallaɓai su ke"
Baaba Nafy ba sa'ar su ba ce dan ko Ghazalar za ta ba ta kusan shekaru shatakwas zuwa ishirin.
Zaytoonah ta É—ago ido ta kalli Ghazala da ke yanka cabbage sai wani murmushi ta ke yi.
Kamar za ta yi magana sai kuma ta yi shiru dan biye mu su ma ɓata lokaci ne, dan ba girmanta ba ne.
"Ai ba mu san Yallaɓai ya yi aure ba sai da haske ta shigo gidan nan, tauraruwar Galadima Allah ya ja zamanin ki"
Wata mata ta faÉ—a wanda ko sunan ta Zaytoonah ba ta sani ba.
"Allah ya kawo Magajin gida nan da wata tara Amin"
Murmushin fiskar Ghazala ya É—auke É—if kamar É—aukewar wutan NEPA.
Zaytoonah ta kauda kan ta kamar ba ta ji abinda aka faÉ—a ba.
Abubuwa da dama su ka dinga yawo a kwanyar Ghazala. Maganar Magaji ya taɓa ta sosai, ba wai ta wuce shekarun haihuwa ba ne amma kuma propability ɗin samun ciki is very low compared to Zaytoonah wacce yanzu ne ma ta cika shekara ashirin da huɗu a duniya. Idan ba ta manta ba haihuwar ta na biyu ta yi allurar tazarar haihuwa saboda lokacin ba ta son cigaba da haihuwa da Alhaji Bashir. Shekara ɗaya da yin hakan ma ta rabu da shi.
Suma ma su yiwa Ghazala kirarin da su ka ga ta haÉ—e rai sai su ka yi shiru...
Yau tun safe ba su da wuta, kamar wutan anguwar ta su ne ta samu matsala. Tun ƙarfe biyar na yamma aka tada generator ya ke ta aiki.
Ƙarfe takwas na dare Zaytoonah ta shiga wanka. Yau kwanan ta ne, zuwa ƙarfe tara ta san Galadima zai dawo daga Fada.
Ta fito daga wanka tana shafa mai Generator ya mutu.
Da sauri ta fara laluben wayan ta dan ta haska ɗakin kawai wayar ta faɗi ƙasa, ta tsugunna ta lalubo wayar tana ƙoƙarin kunna shi kawai ta ji kamar an taɓa ma ta baya nan da nan ta ƙwalla ƙara, jikinta ya fara ƙyarma.
"Ben dont kill me, please dont kill me"
Ta faɗa tana yin baya-baya saboda Ben kawai ta ke gani a idonta yana riƙe da bindiga.
Raziya da Hajiya Ghazala ne su ka shigo É—akin da gudu.
"Zaytoonah" Ghazala ta kira tana haskata da wayarta.
"Zuhayr help me, save me D, save me" abinda ta ke faɗi kenan har lokacin jikinta na ɓari.
"Anty Zaytoonah" Raziya ta faÉ—a tana matsawa kusa da ita.
"Raziya ki matsa ƙila Aljanu gareta. Je ki kira Baba Maigadi a zo ma ta ruƙiyya"
Ta faÉ—a tana janye Raziya daga wajen. Dukkan su fita su ka yi daga É—akin su ka bar Zaytoonah a wajen tana cigaba da sunbatu.
Raziya ta yi ƙasa da gudu yayinda Ghazala ta shiga kiran numbar Justice.
ÆŠaya daga cikin dogarai ma su tsaron gidan Raziya ta samu ta gaya ma sa ya zo inji Ghazala, Aljanun Zaytoonah sun tashi.
Da farko ya so ƙin shiga dan iyakar sa tsakar gidan sai kuma falon Justice da ke ƙasa idan ya buƙaci ganin su. Sai dai yadda Raziyan ta ke magiya ya sa shi bin bayanta da sauri.
Yana shiga ya tadda Ghazala a falon ƙasa tana waya.
"Wallahi hauka tuburan ta ke yi Hajiya. Yanzu dai na sa an kira dogari zai ma ta ruƙiyya"
Daga ɓangaren Hajiya Abu ta ce "Kul, banda wannan ganganci. Kar namijin da ya shiga wajen ta. Ku dai bar ta a ɗakin zuwa Galadima ya iso"
Ghazala ta amsa da toh.
Cewa dogarin ta yi ya tsaya a wajen zuwa Galadima ya iso saboda kar Zaytoonah ta fito ta mu su wani abin.
"Hajiya su Falaq na É—aki"
"Na tura Baaba Nafy wajen su"
Ai ba ta tsaya jin maganar ba ta haura saman.
Ganin É—akin Zaytoonah a buÉ—e kuma tana jin muryan su Hadid ya sa ta wuce wajen.
"Mom its me Hadid"
"Mom please ba kowa a nan mu ne kawai. Ni da Hadid ne"
Zuwa lokacin É—akin ya É—au haske saboda torchlight da kuma wayar da Baaba Nafy ta kunna. Tana haurowa sama ta samu 'yan biyu da Falaq a É—akin.
A hankali Zaytoonah ta fara sauke numfashi ganin da gaske dai 'ya'yanta ne a gaban ta...
Da sauri-sauri Galadima ya shigo gidan har lokacin Ghazala na zaune a falon ƙasa.
"Ina ta ke?" Ya faɗa da ƙarfi.
ÆŠakin ta.
Yana wucewa itama ta bi bayan shi da sauri.
Lokacin Zaytoonah ta samu nitsuwa, tana zaune a kan gado sun sata a tsakiya.
Shigowar sa É—akin ya sa Baaba Nafy ta ja hannun Falaq da Raziya su ka bar É—akin.
"Are you Ok"
"I'm sorry" ta furta a hankali.
"Sannu ya jikin?Baaba Nafy ne ta miki ruƙiyya?"
Irin kallon da Justice ya watsa ma ta ne ya sa ta yi shiru. Ta juya ta fice daga É—akin...
Bayan ya lallaɓa Zaytoonah ta yi bacci tukunna ya fito ya hau ma su aiki da masifa kan ta ya za a bari generator ya mutu, duk da zuwa lokacin an gyara amma a hakan sai da yai ta faɗa. Su kan su sun yi mamakin wannan faɗan dan ba halin Galadima ba ne.
***