Sashe 129
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da Zaytoonah ta tashi ba ta manta abinda ta gani ba amma kasancewa Justice bai yarda ba ya sa ta yi shiru ta fara tunanin kodai da gasken ne mafarki ta yi. Wunin ranan dai ta yi shi a tsorace ne dan sau ɗaya kawai ta sauƙa ƙasa.
Kwana biyu ba abinda ya kuma faruwa dan haka ta share abin kamar bai faru ba.
Yau kwana huÉ—u da faruwan wancan abin. Tana kitchen tana aikin abinci. Ita kaÉ—ai ne a gidan sai Atika wacce ba ta san ma inda ta shiga ba, duk da dai tun sanda Justice ya ma ta faÉ—a ta ke kaffa-kaffa da Zaytoonah amma ita Zaytoonan ba ta sake jiki da ita ba, aiki idan ba ya zama dole ba ba ta sakata.
Bayan ta gama komai ta ɗauka tray da ta jera kayan abinci ta wuce da shi sama, bayan ta gama shirya mu su abincin ne ta wuce ɗakinta dan ta yi wanka. Any moment from now Galadima zai iya dawowa. Bayan ta shiga banɗaki mamaki ya kamata ganin ba ta ga komai ba. 'Har yanzu' ta furta a ƙasan ranta. Bai cika ma ta latti ba, sai dai wannan kwana huɗu kenan tana zuba ido amma ba ta ga alamar sa ba.
Ta gama wanka ta fito sanye da bathrobe dogo kalar Madara.
A stool da ke gaban dressing mirror ɗin ta ta zauna tana ƙoƙarin shafa mai. Kallon kanta ta yi jikin madubi ta yi murmushi gaskiyar Mommy ne da ta ce ma ta tana glowing kwana biyun nan.
Ƙirjinta ne ya buga yayinda numfashin ta ya fara fita da sauri-sauri jikinta na rawa ta fara juyawa a hankali dan ta tabbatar da abinda ta ke gani a jikin madubi ko dai da gaske ɗin yana bayanta ne. Ihu ta saka ganin Ben tsaye a ta bayanta.
"Zuhayr, Zuhayr help, help..." ta ke ta faɗa bayan ta takure jikin bango, jikinta sai ƙyarma ya ke.
Da gudu Justice ya hauro sama dai dai ya iso ƙofar ɗakin ya ga Atika ma ta fito daga ɗakin Ghazala.
"Yallaɓai"
Bai kulata ba ya shige É—akin.
Har lokacin Zaytoonah sai sunbatu kawai ta ke yi a waje É—aya.
Yana zuwa rungumeta yai ya na kiran sunan ta.
Jin muryan sa ya sa ta ƙara ƙanƙameshi tana kiran "Zuhayr i know you'll come. Na san ba za ka taɓa bari Ben ya kashe ni ba"
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke yana tunanin akwai babbar matsala...
Maganar dai irin ta ranan ce wai Ben ta gani a cikin É—akinta, Abinda ta gaya ma sa kenan bayan ta samu nitsuwa. Shi dai ya shigo bai ga komai ba amma ita ta dage Ben ya shigo É—akinta har da nuna ma sa inda ya tsaya.
Ƙoƙarin kwantar ma ta da hankali yai amma ina ta ƙi sauraren sa ita wai dole sai ya yadda da abinda ta gani.
Abin har ya so ba shi haushi amma da ya tuna cewa ita ɗin ba cikakkiyar lafiya gareta ba sai ya cigaba da lallashinta har ta haƙura akan ba ta ga Ben ba...
Washegari da safe ya É—auketa su ka je ganin wani Psychiatrist Doctor. Galadima ne ya ma sa bayanin gameda ciwon na ta da kuma yadda ya ke tashi idan ta tsinci kan ta a cikin duhu amma yanzu kwana biyun nan ba a duhu ma ya ke tashi ba.
Wasu tambayoyi yai wa Zaytoonah tareda cewa yana so ya ga result na test da diagnosis da aka ma ta a chan Madina da kuma America lokacin da ciwon ya fara. Da ke ba su taho da shi ba Galadima ne ya koma gida bayan Zaytoonah ta gaya ma sa inda ta ajiye su.
A É—an tambayoyin da Likitan yai wa Zaytoonah ya fahimci tabbas idan da duhu ke tada ciwon to yanzu akwai abinda ta ke gani da ke tunzura ta har ciwon ya tashi.
Bayan Galadima ya kawo takardun Likitan ya kai kusan minti talatin yana dubawa kafin daga baya yai wa Galadima bayani bayan ya ce Zaytoonah ta basu waje.
"Ranka shi daɗe gaskiya matar ka na buƙatar kulawa sosai. Dole a gano mi ta ke gani ya ke sa ta tunanin ta ga shi wancan Ben ɗin, ko dai tana ganin hoton sa ko kuma wani abu mai kama da shi ko kuma wani abu dai da ya ke da nasaba da shi. Idan aka kawar da wannan zai kawo ma ta sauƙi amma idan ta cigaba da haka ina tsoron za a koma gidan jiya"
Galadima ya kalleshi cikin rashin fahimta.
"Report É—in da na karanta ya nuna cewa Zaytoonah ta yi hauka a baya"
"Hauka!"
"Ka kwantar da hankalin ka Yallaɓai ba irin hauka ta yawo a titi ana tsince-tsince ba, ina nufin hauka saboda damuwa, a yadda su ka rubuta alokacin ba ta iya tuna cewa ta haihu balle ma ta kula da 'ya'yanta. Tana kallon duk wani bature saurayi marar gashin baki ko gemu a matsayin Ben. Ta taɓa attacking wani nurse namiji a Asibiti akan saita kashe shi saboda kallon Ben ta ke ma sa. Ko da ya ke ta samu lafiya daga baya amma har yanzu da saura. Idan ta cigaba da tsorata haka ina tsoron za a koma gidan jiya, za ta dinga kallon kowa a matsayin Ben"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun" Galadima ya furta yana sauke ajiyar zuciya.
"Insha Allah za ta samu lafiya" Likitan ya faÉ—a...
***
"Zaytoonah ki saurareni Dan Allah..."
"Farha ba wanda ya yarda da ni a nan kema ba za ki yarda ba. Ben na gani, Ben. He wanted to kill me, kin manta sau nawa yai yunƙurin kashe ni. Believe me Farha"
Idon Farha ya ciko da hawaye saboda tausayin ƙawarta.
"Zaytoonah Ben is dead. An halbeshi ya mutu, babu ghost a musulunci you of all people should know that"
"Kina cewa na haukace kenan, haka Ghazala ma ta faÉ—a wai na fara hauka"
"Zan zo Nigeria, zan zo na duba ki, Zaytoonah kin ji"
Ba tare da ta katse kiran ba ta rufe Laptop É—in da su ke video call É—in da shi.
Ba wanda ya yarda da ita, har Mommy ma ba ta yarda ba. 'Nan gaba idan na ganshi kashe shi zan yi kafin ya kashe ni' ta furta a fili...
Mommy da Galadima sun tsaida magana akan za a sake kai Zaytoonah wajen Likitan ta. Tun rana na uku da Zaytoonah ta sake firgita saboda Ben da ta gani Galadima ya kama hanya ya tafi Zaria inda ya sanar ma Mommy duk abinda ke faruwa. Bayan ya dawo, Mommy da kanta ta zo Abujan ta yi kwana biyu inda ta yi ta ƙoƙarin fahimtar da Zaytoonah cewa Ben ya mutu, ba shi ta ke gani ba, sai dai har ta tafi ba wai Zaytoonan ta yarda ba ne.
Wannan ya sa Mommy ta yiwa Galadima magana akan tana so ta kai Zaytoonah wajen Likitan da ya duba ta da farko, shima kuma ya amince da hakan...
**
Ghazala ce ta shigo ɗakin Zaytoonah ta ajiye mutum-mutumin Ben a tsakiyar ɗakin, za ta fita kenan ta ji kamar za a buɗe ƙofa, da sauri ta yi hanyar banɗaki saboda ba ta yi tunanin Zaytoonan za ta shigo yanzu ba.
Zaytoonah na buɗe ɗakin ta kalli Ben a tsakiyar ɗakinta, irin shigar da ta ke ganin sa da shi kullum ne ta gani yanzu. Ta ɗan tsorata kam amma da ke bayansa ta gani ba fiskarsa ba sai ba ta firgita sosai ba. Kulle ƙofar ta yi ta fita da gudu dan ta kira su Maman Tope da su Raziya da ke ƙasa, wannan karan so ta ke kowa ya ga Ben ɗin da ta ke gani a ɗakinta kullum. Sai dai ba ta ankara ba ta ture Falaq da ke bakin stairs.
Tsayawa ta yi chak ganin Falaq tana gangarawa ƙasa.
Raziya da Suhailah su ka yi wajen da gudu jin ihun Falaq É—in.
Zaytoonah ta tsaya chak ta kasa motsawa tana hango su Raziya na kuka suna jijjiga Falaq.
Maman Tope ta fito daga kitchen jin kukan Yaran. Ta kama salati ganin Falaq a sume. Har Ghazala ta zo ta wuceta ba ta iya motsawa ba tana kallon yadda su ke ta kuka...
Suna zuwa Asibiti aka admitting Falaq wacce har lokacin ba ta farfaÉ—o ba. Tuni Ghazala ta kira Galadima ta faÉ—a mishi ai Zaytoonah ta turo Falaq daga stairs gatanan kwance a Asibiti rai a hannun Allah. A rikice Justice ya baro office ya taho Asibitin inda ya samesu sun yi jugum suna jiran Likita ya fito. A nan ne kuma Ghazala ta sake tabbatar ma sa da cewa Zaytoonah ne ta turota. Ganin Raziya ba ta ce a'a ba ya sa jikinsa yai sanyi dan tunanin sa abinda Likita ya faÉ—a ne ya ke shirin faruwa.
Bayan Likita ya fito ne ya gaya mu su halin da Falaq ke ciki ta samu karaya a hannu sannan kanta ya bugu sosai kuma suna tunanin kunnen ta ɗaya ya taɓu dan haka ba lallai ta dinga ji sosai ba, amma sai ta farfaɗo kafin su tabbatar. Allah ma ya taimaka ba bu wani bleeding ta cikin kan ta.
Kusan ƙarfe bakwai na dare ya maida Raziya gida tareda son duba halin da Zaytoonah ke ciki. Abin mamaki da su ka je a falon ƙasa su ka tadda Zaytoonah tana jiran Galadima yana zuwa ta fara ma sa maganar ai yau kam za ta tabbatar ma sa da gaskiyarta dan Ben na ɗakin ta. Bai musa ba ya bita har ɗakin sai dai tana buɗe ƙofa sai wayam ba komai.
"Ina Ben É—in ya ke?"
"Na gan shi fa, ina ga guduwa yai. Believe me"
"Falaq na Asibiti, Raziya sun ce ke kika turota, miyasa?"
"Ina son gaya mu su cewa Ben na É—akina ne, ni ban san tana wajen ba. Ka yarda da ni"
Girgiza kai kawai yai ya wuce É—akin sa dan ya san ba laifinta ba ne, dole ya ma ta uzuri...
Kwana biyu ba abinda ya kuma faruwa dan haka ta share abin kamar bai faru ba.
Yau kwana huÉ—u da faruwan wancan abin. Tana kitchen tana aikin abinci. Ita kaÉ—ai ne a gidan sai Atika wacce ba ta san ma inda ta shiga ba, duk da dai tun sanda Justice ya ma ta faÉ—a ta ke kaffa-kaffa da Zaytoonah amma ita Zaytoonan ba ta sake jiki da ita ba, aiki idan ba ya zama dole ba ba ta sakata.
Bayan ta gama komai ta ɗauka tray da ta jera kayan abinci ta wuce da shi sama, bayan ta gama shirya mu su abincin ne ta wuce ɗakinta dan ta yi wanka. Any moment from now Galadima zai iya dawowa. Bayan ta shiga banɗaki mamaki ya kamata ganin ba ta ga komai ba. 'Har yanzu' ta furta a ƙasan ranta. Bai cika ma ta latti ba, sai dai wannan kwana huɗu kenan tana zuba ido amma ba ta ga alamar sa ba.
Ta gama wanka ta fito sanye da bathrobe dogo kalar Madara.
A stool da ke gaban dressing mirror ɗin ta ta zauna tana ƙoƙarin shafa mai. Kallon kanta ta yi jikin madubi ta yi murmushi gaskiyar Mommy ne da ta ce ma ta tana glowing kwana biyun nan.
Ƙirjinta ne ya buga yayinda numfashin ta ya fara fita da sauri-sauri jikinta na rawa ta fara juyawa a hankali dan ta tabbatar da abinda ta ke gani a jikin madubi ko dai da gaske ɗin yana bayanta ne. Ihu ta saka ganin Ben tsaye a ta bayanta.
"Zuhayr, Zuhayr help, help..." ta ke ta faɗa bayan ta takure jikin bango, jikinta sai ƙyarma ya ke.
Da gudu Justice ya hauro sama dai dai ya iso ƙofar ɗakin ya ga Atika ma ta fito daga ɗakin Ghazala.
"Yallaɓai"
Bai kulata ba ya shige É—akin.
Har lokacin Zaytoonah sai sunbatu kawai ta ke yi a waje É—aya.
Yana zuwa rungumeta yai ya na kiran sunan ta.
Jin muryan sa ya sa ta ƙara ƙanƙameshi tana kiran "Zuhayr i know you'll come. Na san ba za ka taɓa bari Ben ya kashe ni ba"
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke yana tunanin akwai babbar matsala...
Maganar dai irin ta ranan ce wai Ben ta gani a cikin É—akinta, Abinda ta gaya ma sa kenan bayan ta samu nitsuwa. Shi dai ya shigo bai ga komai ba amma ita ta dage Ben ya shigo É—akinta har da nuna ma sa inda ya tsaya.
Ƙoƙarin kwantar ma ta da hankali yai amma ina ta ƙi sauraren sa ita wai dole sai ya yadda da abinda ta gani.
Abin har ya so ba shi haushi amma da ya tuna cewa ita ɗin ba cikakkiyar lafiya gareta ba sai ya cigaba da lallashinta har ta haƙura akan ba ta ga Ben ba...
Washegari da safe ya É—auketa su ka je ganin wani Psychiatrist Doctor. Galadima ne ya ma sa bayanin gameda ciwon na ta da kuma yadda ya ke tashi idan ta tsinci kan ta a cikin duhu amma yanzu kwana biyun nan ba a duhu ma ya ke tashi ba.
Wasu tambayoyi yai wa Zaytoonah tareda cewa yana so ya ga result na test da diagnosis da aka ma ta a chan Madina da kuma America lokacin da ciwon ya fara. Da ke ba su taho da shi ba Galadima ne ya koma gida bayan Zaytoonah ta gaya ma sa inda ta ajiye su.
A É—an tambayoyin da Likitan yai wa Zaytoonah ya fahimci tabbas idan da duhu ke tada ciwon to yanzu akwai abinda ta ke gani da ke tunzura ta har ciwon ya tashi.
Bayan Galadima ya kawo takardun Likitan ya kai kusan minti talatin yana dubawa kafin daga baya yai wa Galadima bayani bayan ya ce Zaytoonah ta basu waje.
"Ranka shi daɗe gaskiya matar ka na buƙatar kulawa sosai. Dole a gano mi ta ke gani ya ke sa ta tunanin ta ga shi wancan Ben ɗin, ko dai tana ganin hoton sa ko kuma wani abu mai kama da shi ko kuma wani abu dai da ya ke da nasaba da shi. Idan aka kawar da wannan zai kawo ma ta sauƙi amma idan ta cigaba da haka ina tsoron za a koma gidan jiya"
Galadima ya kalleshi cikin rashin fahimta.
"Report É—in da na karanta ya nuna cewa Zaytoonah ta yi hauka a baya"
"Hauka!"
"Ka kwantar da hankalin ka Yallaɓai ba irin hauka ta yawo a titi ana tsince-tsince ba, ina nufin hauka saboda damuwa, a yadda su ka rubuta alokacin ba ta iya tuna cewa ta haihu balle ma ta kula da 'ya'yanta. Tana kallon duk wani bature saurayi marar gashin baki ko gemu a matsayin Ben. Ta taɓa attacking wani nurse namiji a Asibiti akan saita kashe shi saboda kallon Ben ta ke ma sa. Ko da ya ke ta samu lafiya daga baya amma har yanzu da saura. Idan ta cigaba da tsorata haka ina tsoron za a koma gidan jiya, za ta dinga kallon kowa a matsayin Ben"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun" Galadima ya furta yana sauke ajiyar zuciya.
"Insha Allah za ta samu lafiya" Likitan ya faÉ—a...
***
"Zaytoonah ki saurareni Dan Allah..."
"Farha ba wanda ya yarda da ni a nan kema ba za ki yarda ba. Ben na gani, Ben. He wanted to kill me, kin manta sau nawa yai yunƙurin kashe ni. Believe me Farha"
Idon Farha ya ciko da hawaye saboda tausayin ƙawarta.
"Zaytoonah Ben is dead. An halbeshi ya mutu, babu ghost a musulunci you of all people should know that"
"Kina cewa na haukace kenan, haka Ghazala ma ta faÉ—a wai na fara hauka"
"Zan zo Nigeria, zan zo na duba ki, Zaytoonah kin ji"
Ba tare da ta katse kiran ba ta rufe Laptop É—in da su ke video call É—in da shi.
Ba wanda ya yarda da ita, har Mommy ma ba ta yarda ba. 'Nan gaba idan na ganshi kashe shi zan yi kafin ya kashe ni' ta furta a fili...
Mommy da Galadima sun tsaida magana akan za a sake kai Zaytoonah wajen Likitan ta. Tun rana na uku da Zaytoonah ta sake firgita saboda Ben da ta gani Galadima ya kama hanya ya tafi Zaria inda ya sanar ma Mommy duk abinda ke faruwa. Bayan ya dawo, Mommy da kanta ta zo Abujan ta yi kwana biyu inda ta yi ta ƙoƙarin fahimtar da Zaytoonah cewa Ben ya mutu, ba shi ta ke gani ba, sai dai har ta tafi ba wai Zaytoonan ta yarda ba ne.
Wannan ya sa Mommy ta yiwa Galadima magana akan tana so ta kai Zaytoonah wajen Likitan da ya duba ta da farko, shima kuma ya amince da hakan...
**
Ghazala ce ta shigo ɗakin Zaytoonah ta ajiye mutum-mutumin Ben a tsakiyar ɗakin, za ta fita kenan ta ji kamar za a buɗe ƙofa, da sauri ta yi hanyar banɗaki saboda ba ta yi tunanin Zaytoonan za ta shigo yanzu ba.
Zaytoonah na buɗe ɗakin ta kalli Ben a tsakiyar ɗakinta, irin shigar da ta ke ganin sa da shi kullum ne ta gani yanzu. Ta ɗan tsorata kam amma da ke bayansa ta gani ba fiskarsa ba sai ba ta firgita sosai ba. Kulle ƙofar ta yi ta fita da gudu dan ta kira su Maman Tope da su Raziya da ke ƙasa, wannan karan so ta ke kowa ya ga Ben ɗin da ta ke gani a ɗakinta kullum. Sai dai ba ta ankara ba ta ture Falaq da ke bakin stairs.
Tsayawa ta yi chak ganin Falaq tana gangarawa ƙasa.
Raziya da Suhailah su ka yi wajen da gudu jin ihun Falaq É—in.
Zaytoonah ta tsaya chak ta kasa motsawa tana hango su Raziya na kuka suna jijjiga Falaq.
Maman Tope ta fito daga kitchen jin kukan Yaran. Ta kama salati ganin Falaq a sume. Har Ghazala ta zo ta wuceta ba ta iya motsawa ba tana kallon yadda su ke ta kuka...
Suna zuwa Asibiti aka admitting Falaq wacce har lokacin ba ta farfaÉ—o ba. Tuni Ghazala ta kira Galadima ta faÉ—a mishi ai Zaytoonah ta turo Falaq daga stairs gatanan kwance a Asibiti rai a hannun Allah. A rikice Justice ya baro office ya taho Asibitin inda ya samesu sun yi jugum suna jiran Likita ya fito. A nan ne kuma Ghazala ta sake tabbatar ma sa da cewa Zaytoonah ne ta turota. Ganin Raziya ba ta ce a'a ba ya sa jikinsa yai sanyi dan tunanin sa abinda Likita ya faÉ—a ne ya ke shirin faruwa.
Bayan Likita ya fito ne ya gaya mu su halin da Falaq ke ciki ta samu karaya a hannu sannan kanta ya bugu sosai kuma suna tunanin kunnen ta ɗaya ya taɓu dan haka ba lallai ta dinga ji sosai ba, amma sai ta farfaɗo kafin su tabbatar. Allah ma ya taimaka ba bu wani bleeding ta cikin kan ta.
Kusan ƙarfe bakwai na dare ya maida Raziya gida tareda son duba halin da Zaytoonah ke ciki. Abin mamaki da su ka je a falon ƙasa su ka tadda Zaytoonah tana jiran Galadima yana zuwa ta fara ma sa maganar ai yau kam za ta tabbatar ma sa da gaskiyarta dan Ben na ɗakin ta. Bai musa ba ya bita har ɗakin sai dai tana buɗe ƙofa sai wayam ba komai.
"Ina Ben É—in ya ke?"
"Na gan shi fa, ina ga guduwa yai. Believe me"
"Falaq na Asibiti, Raziya sun ce ke kika turota, miyasa?"
"Ina son gaya mu su cewa Ben na É—akina ne, ni ban san tana wajen ba. Ka yarda da ni"
Girgiza kai kawai yai ya wuce É—akin sa dan ya san ba laifinta ba ne, dole ya ma ta uzuri...