Sashe 18
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Sai ki yi kuma ai 'yar baƙin ciki. To ni dai ba zan ci soyayyen ƙwai ba ki min wani abun mai ɗan romo-romo"
Ta wuce É—akinta tana tura ciki.
Wani abu ya daki zuciyar Maryam. "Ciki" ta furta a fili. Da ƙyar ta samu ta ƙarisa soya doyan da ta ke ta kwashe ko tattara wajen ba ta yi ba ta wuce ɗakinta. Gado kawai ta hau ta kwanta.
"Kenan ni ne ba na haihuwa" ta furta hawaye na gangaro ma ta.
T J ya buɗe ƙofa ya shigo, tuntuni ya shirya yana ɗakinsa yana marking assignment ɗin ɗalibai. Daya gama ne ya fito dan ya karya kafin ya wuce school, rashin ganin Maryam a falo da kitchen ya sa shi shigowa ɗakinta.
"Dear are you Ok?" Ya tambaya yana taɓa goshinta.
"Hajjo na da ciki" ta faÉ—a tana kallon sa
"Ya Ilahi! Ashe ban faÉ—a miki ba. About three weeks ago ta ce min ba ta da lafiya shine na raka ta asibiti aka ce ciki gareta. Ni dai Addu'a na Allah ya sa ba SS ba ne, ba na son 'ya'ya na su yi wahala kaman na Sadiq"
Ido kawai ta zuba mishi tana kallon yadda yake koro bayanai.
"Indai ta haihu aka samu AS inaga planning za ta yi mu raini abin da ta haifa"
"Saboda kar na cinye muku baby tun bai zo duniya ba shine ake ɓoye min cikin?"
"Subhanallahi! Maryam wani irin magana ne wannan? You know that's not true. Wallahi mantawa na yi"
"Mantuwa? Barkindo Mantuwa? For three weeks ka san cewa matarka tana da ciki amma ka manta ba ka gaya min ba. You are not good at lying dan haka kar ka fara. Ba ka son gaya min saboda ni mayya ce zan kama kurwan É—an ku"
"Innalillahi. Maryam please..."
Ranan kam duk yadda ya so ya fahimtar da Maryam mantuwa yai ba ta saurareshi ba. Da shi da ita ɗin ba wanda ya yi breakfast. Da rana da ya dawo ma dai abun duk ɗaya ne. Kusan sati tayi tana fushi dashi. Abunda ya lura shine ba wai dan bai faɗa ma ta bane kaɗai dalilin fushin na ta har da stigma na rashin haihuwa da ba ta yi ba har yanzu. A haka dai yai ta lallaɓata har su ka shirya gaba ɗaya. Ranan da su ka shirya ma saboda albishir daya kawo ma ta ne na form daya siya ma ta na Law school da ke Abuja. Yana ma ta Albishir ɗin ta yi tsalle ta rungumeshi har da bashi sweet kiss a lips ɗin sa, daga ranan kuma faɗan su ya zo ƙarshe...
Ana gobe Maryam za ta je Abuja yin registration aka turowa T J letter cewa ƙanin Kakan sa wato Alhaji Isa ya rasu. Wannan ya sa Maryam ce kaɗai ta tafi Abuja shi kuma ya wuce Ringim. Kwana ɗaya yai Washegari ya dawo saboda ayyuka da su ke gaban shi.
Bayan komai ya kammala Maryam ta fara karatu a Abuja, ɗaki T J ya kama ma ta ya biya hayan shekara ɗaya har ta gama Law school ɗin. Sunyi akan zai dinga zuwa ma ta duk weekend idan ya samu sarari ko ba weekend ba ya ce zai dinga leƙo ta.
Cikin Hajjo na wata takwas Inna Saratu ta zo ta É—auketa wai za ta yi haihuwan gida. Ita anata nufin wai za ayiwa Hajjo da abunda za ta haifa maganin Mayu saboda kar Maryam ta kama kurwan su.
Shi dai T J tunda ta ce Iya ma ta amince da tafiyar ya ce Allah ya kai su gida lafiya. Da ya san abinda ake shirin yi kenan da ko Iyan ce ta zo da kanta ba zai bari Hajjo ta bi ta ba. Shi dai tunda ta tafi ya ke addu'ar Allah ya sa ta haihu lafiya kuma a samu AS ba SS ba.
Hajjo kam tunda su ka tafi ƙauyen su ake ta ɗura ma ta jiƙe-jiƙe ana ma ta hayaƙi. Da farko ta nuna ba ta so amma Innarta ta ce ba ta isa ba dan ba zai yiwu ta dinga haihuwa Maryam na cinye 'ya'yan ba. Yadda T J ke da dukiya ya kamata ace ta haifa ma sa 'ya'ya dayawa, idan kuma duk su ka mutu ai ta tashi a tutar babu kenan. Da haka Hajjo ta yi shiru aka cigaba da magani.
Ta dawo daga class a gajiye sai taga ƙofar ɗakinta a buɗe ta shiga da sauri dan jiya-jiya T J ya bar Abuja ya koma Zaria.
"Lafiya ka zo?" Ta faÉ—a a É—an tsorace bayan ta ganshi zaune yana rubutu.
Ya taso ya rungumeta ya ce "jiya na yi mafarki mai daɗi shine na ka sa haƙuri na ce dole na zo na baki labari, kinga kema sai ki sa cikin addu'ar ki"
"My Love za ka sa heart attack ya kama ni. You should've waited zuwa wani weekend É—in idan ka zo sai ka gaya min mafarkin ai"
Ya girgiza kai yana ƙoƙarin cire ma ta gyalenta
"Baby Idan mafarkin nan ya tabbata i'll be the happiest man on earth"
Jin hannunsa a ƙugunta yana shirin since zaninta ya sa ta yi dariya ta sa hannunta ta zagaye wuyansa ta ce " gaya min gaskiya. Labarin mafarki ne ya kawoka ko kuma wani abun daban?"
"Labarin mafarki mana, amma zan fi jin daÉ—in ba da labarin idan na..."
Ya kai baki zai kissing É—inta ta sa hannu ta tare bakin " Love za ka barni na yi karatun nan kuwa. Karatun fa akwai wahala and you're not helping"
Ya janye hannunta ya manna ma ta light kiss ya ce "mu je na baki laƙanin riƙe karatu"
Ta yi dariya ta ce " I love you Shehu Tijjani"
"Wayyo zuciyata" ya faɗi yana dafe ƙirjinsa ta kai ma sa dundu ya riƙe hannun ya jawota ta faɗa jikinsa.
"Allah ya sa mafarkin da na yi ya tabbata"
"Wani irin mafarki ne wannan?"
"Wai kin haifa min Cute Princess mai kamar ki"
Ta yi murmushi dan harga Allah ta ji daÉ—in maganar da ya ce.
"Amin" ta furta ƙasa-ƙasa.
Kan katifar ɗakin ya mu su masauki yana faɗin ƙila Allah ya basu Princess yau...
Kwana tara da fara magani wata yammacin ranan Talata Hajjo ta fara ciwon ciki bayan ta sha jiƙon da aka ba ta. Wasa-wasa ciwon cikin ya tsanan ta daga baya sai naƙuda gadan-gadan aka kira wata Tsohuwa ungozoma. Ba ƙaramin wahala Hajjo ta sha ba kafin nan ta haihu amma ɗan ba rai dan har kaman ya fara ruɓewa alaman ya kwana biyu da mutuwa. Tun kwana uku da su ka wuce ta dena jin motsin cikinta amma ba ta faɗa ba.
Hajjo ta yi kuka sosai dan ko rasuwan Sadiq iya kaci. Ita kan ta yarda magungunan da ta ke ta ɗirkawa ne ya kashe ma ta ɗanta tunda lafiya-lafiya ta bar Zaria. A ranan aka aika Ringim su kuma su ka tura wasiƙa zuwa Zaria. Wasiƙar ba ta isa ga T J ba sai washegari.
Shima ya ji mutuwar a jikinsa sosai. A ranan da ya je Ringim ya ke jin labarin komai dan an taho da Hajjo Ringim, ya kuwa zage ya zuzzubawa Hajjo da Innarta masifa. Ya kuma furta kalmar da ta girgiza Hajjon da Innar na ta
"Duk ranan da aka ƙara kawo maganin Maita ko aka kira wani mai Magani wa Hajjo a bakin aurenta. Idan ba za ta iya zama da ni ba ta karɓi ƙaddararta zan iya sawwaƙa ma ta tun yanzu" yadda yai ta faɗa sai da Goggo ta sa baki yai shiru.
Abun takaicin ma ko gawar É—an sa bai gani ba. Daga Ringim straight Abuja ya wuce ko da wuni É—aya ne gara ya je ya ga Maryam dan ya san yadda ya ke jin sa ita kaÉ—ai ce za ta iya kwantar ma sa da hankali.
Itama ba ta ji daɗin mutuwar ɗan Hajjo ba, ta kuma ƙara tabbatarwa kan ta lallai ba ƙaramin Jahilci ke damun Hajjo da mahaifiyarta ba. Sun Jahilci zamani kuma sun Jahilci addini...
A wasu lokutan da Inna ta kawowa Iya ziyara ne ta zugata akan ta je ta zauna a gidan T J dan ta rinƙa kula da Hajjo idan ba haka ba kuwa Yadda Maryam ta shanye T J ba za ta bari ya haihu da kowa ba tunda gashi har sau biyu tana kashewa Hajjo 'ya'ya.
Iya ta san ba Maryam ce ke kashe 'ya'yan Hajjo ba amma kuma tsanar Maryam ya sa ta hau kan maganar.
Sati biyar da Hajjo ta yi a gida da za ta koma Zaria sai gashi Iya ta tattara kaya itama su ka yi tafiyar tare.
T J ya shiga ruÉ—u lokacin da Iya ta ce za ta zauna da su na wani lokaci. Ba yadda ya iya haka ya tattara kayan É—akin sa ya kai É—akin Maryam ya bar wa Iya É—akin sa.
Bayan kwana biyu da Iya ba ta ga Maryam a gidan ba ne ta tambayi Hajjo ina Maryam ta ke Hajjo ta ce ma ta wai karatu ta ke yi a Habuja.
T J na dawowa ta haushi da faÉ—a wai ya É—aurewa Maryam gindi ta tafi yawon karuwanci.
"Karatu ta tafi Iya kuma na shekara É—aya ne kawai"
"Karatun Uwar ka. Mata ta tafi karuwanci ka ce ta je karatu. Wani irin karatune daya ƙi ci ya ƙi cinyewa shekara da shekaru. Daɗin abin ma ba ta haihuwa balle aje a ɗauko ɗan shege a kawo maka gida. Allah dai ya shirya"
Ransa ya sosu da maganar Iya amma ba abinda zai ce haka yai shiru ya barta ta yi ta masifa har ta gaji ta yi shiru.
Zuwan su Iya ya sa ya rage kaiwa Maryam Ziyara. Maryam ba ta kawo komai ba dan ta É—auka yana ba ta space ne dan ta samu ta yi karatu sosai.
Bai gaya ma ta Iya ta dawo gidan sa da zama ba dan baya so hankalinta ya tashi , yana jiran perfect time ne da zai gaya ma ta wanda ba za ta É—aga hankalinta sosai ba.
Ta wuce É—akinta tana tura ciki.
Wani abu ya daki zuciyar Maryam. "Ciki" ta furta a fili. Da ƙyar ta samu ta ƙarisa soya doyan da ta ke ta kwashe ko tattara wajen ba ta yi ba ta wuce ɗakinta. Gado kawai ta hau ta kwanta.
"Kenan ni ne ba na haihuwa" ta furta hawaye na gangaro ma ta.
T J ya buɗe ƙofa ya shigo, tuntuni ya shirya yana ɗakinsa yana marking assignment ɗin ɗalibai. Daya gama ne ya fito dan ya karya kafin ya wuce school, rashin ganin Maryam a falo da kitchen ya sa shi shigowa ɗakinta.
"Dear are you Ok?" Ya tambaya yana taɓa goshinta.
"Hajjo na da ciki" ta faÉ—a tana kallon sa
"Ya Ilahi! Ashe ban faÉ—a miki ba. About three weeks ago ta ce min ba ta da lafiya shine na raka ta asibiti aka ce ciki gareta. Ni dai Addu'a na Allah ya sa ba SS ba ne, ba na son 'ya'ya na su yi wahala kaman na Sadiq"
Ido kawai ta zuba mishi tana kallon yadda yake koro bayanai.
"Indai ta haihu aka samu AS inaga planning za ta yi mu raini abin da ta haifa"
"Saboda kar na cinye muku baby tun bai zo duniya ba shine ake ɓoye min cikin?"
"Subhanallahi! Maryam wani irin magana ne wannan? You know that's not true. Wallahi mantawa na yi"
"Mantuwa? Barkindo Mantuwa? For three weeks ka san cewa matarka tana da ciki amma ka manta ba ka gaya min ba. You are not good at lying dan haka kar ka fara. Ba ka son gaya min saboda ni mayya ce zan kama kurwan É—an ku"
"Innalillahi. Maryam please..."
Ranan kam duk yadda ya so ya fahimtar da Maryam mantuwa yai ba ta saurareshi ba. Da shi da ita ɗin ba wanda ya yi breakfast. Da rana da ya dawo ma dai abun duk ɗaya ne. Kusan sati tayi tana fushi dashi. Abunda ya lura shine ba wai dan bai faɗa ma ta bane kaɗai dalilin fushin na ta har da stigma na rashin haihuwa da ba ta yi ba har yanzu. A haka dai yai ta lallaɓata har su ka shirya gaba ɗaya. Ranan da su ka shirya ma saboda albishir daya kawo ma ta ne na form daya siya ma ta na Law school da ke Abuja. Yana ma ta Albishir ɗin ta yi tsalle ta rungumeshi har da bashi sweet kiss a lips ɗin sa, daga ranan kuma faɗan su ya zo ƙarshe...
Ana gobe Maryam za ta je Abuja yin registration aka turowa T J letter cewa ƙanin Kakan sa wato Alhaji Isa ya rasu. Wannan ya sa Maryam ce kaɗai ta tafi Abuja shi kuma ya wuce Ringim. Kwana ɗaya yai Washegari ya dawo saboda ayyuka da su ke gaban shi.
Bayan komai ya kammala Maryam ta fara karatu a Abuja, ɗaki T J ya kama ma ta ya biya hayan shekara ɗaya har ta gama Law school ɗin. Sunyi akan zai dinga zuwa ma ta duk weekend idan ya samu sarari ko ba weekend ba ya ce zai dinga leƙo ta.
Cikin Hajjo na wata takwas Inna Saratu ta zo ta É—auketa wai za ta yi haihuwan gida. Ita anata nufin wai za ayiwa Hajjo da abunda za ta haifa maganin Mayu saboda kar Maryam ta kama kurwan su.
Shi dai T J tunda ta ce Iya ma ta amince da tafiyar ya ce Allah ya kai su gida lafiya. Da ya san abinda ake shirin yi kenan da ko Iyan ce ta zo da kanta ba zai bari Hajjo ta bi ta ba. Shi dai tunda ta tafi ya ke addu'ar Allah ya sa ta haihu lafiya kuma a samu AS ba SS ba.
Hajjo kam tunda su ka tafi ƙauyen su ake ta ɗura ma ta jiƙe-jiƙe ana ma ta hayaƙi. Da farko ta nuna ba ta so amma Innarta ta ce ba ta isa ba dan ba zai yiwu ta dinga haihuwa Maryam na cinye 'ya'yan ba. Yadda T J ke da dukiya ya kamata ace ta haifa ma sa 'ya'ya dayawa, idan kuma duk su ka mutu ai ta tashi a tutar babu kenan. Da haka Hajjo ta yi shiru aka cigaba da magani.
Ta dawo daga class a gajiye sai taga ƙofar ɗakinta a buɗe ta shiga da sauri dan jiya-jiya T J ya bar Abuja ya koma Zaria.
"Lafiya ka zo?" Ta faÉ—a a É—an tsorace bayan ta ganshi zaune yana rubutu.
Ya taso ya rungumeta ya ce "jiya na yi mafarki mai daɗi shine na ka sa haƙuri na ce dole na zo na baki labari, kinga kema sai ki sa cikin addu'ar ki"
"My Love za ka sa heart attack ya kama ni. You should've waited zuwa wani weekend É—in idan ka zo sai ka gaya min mafarkin ai"
Ya girgiza kai yana ƙoƙarin cire ma ta gyalenta
"Baby Idan mafarkin nan ya tabbata i'll be the happiest man on earth"
Jin hannunsa a ƙugunta yana shirin since zaninta ya sa ta yi dariya ta sa hannunta ta zagaye wuyansa ta ce " gaya min gaskiya. Labarin mafarki ne ya kawoka ko kuma wani abun daban?"
"Labarin mafarki mana, amma zan fi jin daÉ—in ba da labarin idan na..."
Ya kai baki zai kissing É—inta ta sa hannu ta tare bakin " Love za ka barni na yi karatun nan kuwa. Karatun fa akwai wahala and you're not helping"
Ya janye hannunta ya manna ma ta light kiss ya ce "mu je na baki laƙanin riƙe karatu"
Ta yi dariya ta ce " I love you Shehu Tijjani"
"Wayyo zuciyata" ya faɗi yana dafe ƙirjinsa ta kai ma sa dundu ya riƙe hannun ya jawota ta faɗa jikinsa.
"Allah ya sa mafarkin da na yi ya tabbata"
"Wani irin mafarki ne wannan?"
"Wai kin haifa min Cute Princess mai kamar ki"
Ta yi murmushi dan harga Allah ta ji daÉ—in maganar da ya ce.
"Amin" ta furta ƙasa-ƙasa.
Kan katifar ɗakin ya mu su masauki yana faɗin ƙila Allah ya basu Princess yau...
Kwana tara da fara magani wata yammacin ranan Talata Hajjo ta fara ciwon ciki bayan ta sha jiƙon da aka ba ta. Wasa-wasa ciwon cikin ya tsanan ta daga baya sai naƙuda gadan-gadan aka kira wata Tsohuwa ungozoma. Ba ƙaramin wahala Hajjo ta sha ba kafin nan ta haihu amma ɗan ba rai dan har kaman ya fara ruɓewa alaman ya kwana biyu da mutuwa. Tun kwana uku da su ka wuce ta dena jin motsin cikinta amma ba ta faɗa ba.
Hajjo ta yi kuka sosai dan ko rasuwan Sadiq iya kaci. Ita kan ta yarda magungunan da ta ke ta ɗirkawa ne ya kashe ma ta ɗanta tunda lafiya-lafiya ta bar Zaria. A ranan aka aika Ringim su kuma su ka tura wasiƙa zuwa Zaria. Wasiƙar ba ta isa ga T J ba sai washegari.
Shima ya ji mutuwar a jikinsa sosai. A ranan da ya je Ringim ya ke jin labarin komai dan an taho da Hajjo Ringim, ya kuwa zage ya zuzzubawa Hajjo da Innarta masifa. Ya kuma furta kalmar da ta girgiza Hajjon da Innar na ta
"Duk ranan da aka ƙara kawo maganin Maita ko aka kira wani mai Magani wa Hajjo a bakin aurenta. Idan ba za ta iya zama da ni ba ta karɓi ƙaddararta zan iya sawwaƙa ma ta tun yanzu" yadda yai ta faɗa sai da Goggo ta sa baki yai shiru.
Abun takaicin ma ko gawar É—an sa bai gani ba. Daga Ringim straight Abuja ya wuce ko da wuni É—aya ne gara ya je ya ga Maryam dan ya san yadda ya ke jin sa ita kaÉ—ai ce za ta iya kwantar ma sa da hankali.
Itama ba ta ji daɗin mutuwar ɗan Hajjo ba, ta kuma ƙara tabbatarwa kan ta lallai ba ƙaramin Jahilci ke damun Hajjo da mahaifiyarta ba. Sun Jahilci zamani kuma sun Jahilci addini...
A wasu lokutan da Inna ta kawowa Iya ziyara ne ta zugata akan ta je ta zauna a gidan T J dan ta rinƙa kula da Hajjo idan ba haka ba kuwa Yadda Maryam ta shanye T J ba za ta bari ya haihu da kowa ba tunda gashi har sau biyu tana kashewa Hajjo 'ya'ya.
Iya ta san ba Maryam ce ke kashe 'ya'yan Hajjo ba amma kuma tsanar Maryam ya sa ta hau kan maganar.
Sati biyar da Hajjo ta yi a gida da za ta koma Zaria sai gashi Iya ta tattara kaya itama su ka yi tafiyar tare.
T J ya shiga ruÉ—u lokacin da Iya ta ce za ta zauna da su na wani lokaci. Ba yadda ya iya haka ya tattara kayan É—akin sa ya kai É—akin Maryam ya bar wa Iya É—akin sa.
Bayan kwana biyu da Iya ba ta ga Maryam a gidan ba ne ta tambayi Hajjo ina Maryam ta ke Hajjo ta ce ma ta wai karatu ta ke yi a Habuja.
T J na dawowa ta haushi da faÉ—a wai ya É—aurewa Maryam gindi ta tafi yawon karuwanci.
"Karatu ta tafi Iya kuma na shekara É—aya ne kawai"
"Karatun Uwar ka. Mata ta tafi karuwanci ka ce ta je karatu. Wani irin karatune daya ƙi ci ya ƙi cinyewa shekara da shekaru. Daɗin abin ma ba ta haihuwa balle aje a ɗauko ɗan shege a kawo maka gida. Allah dai ya shirya"
Ransa ya sosu da maganar Iya amma ba abinda zai ce haka yai shiru ya barta ta yi ta masifa har ta gaji ta yi shiru.
Zuwan su Iya ya sa ya rage kaiwa Maryam Ziyara. Maryam ba ta kawo komai ba dan ta É—auka yana ba ta space ne dan ta samu ta yi karatu sosai.
Bai gaya ma ta Iya ta dawo gidan sa da zama ba dan baya so hankalinta ya tashi , yana jiran perfect time ne da zai gaya ma ta wanda ba za ta É—aga hankalinta sosai ba.