Sashe 109
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maman Tope ke da aiki amma ta nemi uzuri saboda an kwantar da wata 'yarta a Asibiti. Shiyasa aikin yai wa Zaytoonah yawa dan girkin da za ta yi har da ma su aikin gidan gaba ɗaya. Baccin safe da ta yi ne ma ba ta farka da wuri ba, dan da ta tashi sai gani ta yi ƙarfe shabiyu har da minti tara.
Tana kitchen É—in yaran su ka dawo, duk cikin su Suhailah ce ta shigo ta ma ta oyoyo kafin ta wuce wajen yayyen ta da tuni su ka kunna TV suna kallon wani favourite show É—in su.
Tana gama soya nama ta kashe gas ɗin ta bar kitchen ɗin da sauri. Tun da ta tashi a bacci kitchen ta wuco saboda sauri to kuma yanzu wani fitsari ke cinta dole ta ajiye girkin ta kashe gas ɗin ta tafi ɗaki. Da ta je fitsarin ma sai da ta tsaya ta gyara jikin ta sosai saboda dama tana tareda baƙo. Ta fito daga banɗaki kenan ta ji ihun Suhailah a ƙasa, ba shiri ta fito a guje.
A kitchen ta samu yaran suna tsaye wajen Suhailah da ke zunduma ihu saboda man da ya tsartu ma ta a jiki.
Zaytoonah ta yi kan ta da sauri tana tambayar miya faru amma babu wanda ya kulata saboda Suhailan kuka kawai take yi.
Ta san dai idan mai ya tsartu wa mutum tun lokacin suna yara Mommy na amfani da gishiri ko kamu ta mutsutstsuka wajen, idan kuma akwai Zuma sai ta shafa mu su.
Da sauri ta buÉ—e roban gishiri ta É—ebo ta fara shafawa Suhailah a wuya da hannun ta.
Raziya na cewa ta barta a kai ta Asibiti. Sai da ta gama shafa ma ta ta É—auki Suhailah a kafaÉ—a su ka fito a kitchen É—in dai dai nan kuma Justice ya shigo gidan.
"Miya faru?" Ya faɗa yana karɓan Suhailah a hannun Zaytoonan. Yarinya kuma ganin Daddyn ta kawai sai ta ƙara sautin kuka.
Raziya ce ta yi saurin faÉ—in " Yunwa ta ke ji shine ta shiga kitchen wajen Anty ita kuma ba ta kitchen É—in kuma ta bar Mai mai zafi a wajen sai ya zubowa Suhailah a jiki"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun" kawai ya faÉ—a yai hanyar waje bayan ya yiwa Zaytoonah wani kallo.
Bayan fitar su da ƙyar Zaytoonah ta iya saita kan ta ta shiga kitchen ta goge wajen da man ya zuba ta ƙarisa girkin a gurguje.
Bayan ta gama girkin zama ta yi a falo ta yi tagumi tana jiran dawowar su.
Ta sani naman da ta soya ta ke son zubawa a miya yarinyar ta je ɗauka ta ga ƙaramar kujera a wajen alamar shi ta hau saboda tsayin ta ya kai wajen. By mistake ne ƙila hannunta ya bugi frying pan da ke gefen bowl ɗin da ta zuba naman shine Man ya tsirtu ma ta sauran kuma ya malale a ƙasa.
Kusan awa biyu da fitar su sai gashi sun dawo abin mamaki har da Hajia Ghazala dan ita ce ma ke riƙe da Suhailan wacce ke riƙe da ice cream tana sha hankali kwance an shafa ma ta magani a wajen da man ya zuba raɗaɗin da ta ke ji ya ragu.
Ko kallon Zaytoonah bai yi ba ya wuce sama.
Sai da ta sauke ajiyar zuciya kafin ta bi bayan sa ba tareda ta yiwa Hajia Ghazala magana ba.
Kai tsaye É—akin sa ta shiga dan ba ta gan shi a falon sa ba.
"Daddyn Raziya ka yi haƙuri, wallahi ban san za ta shiga kitchen ɗin ba i just..."
"Ƙarfe nawa Zaytoon ba a gama abincin rana ba?. Idan ke ba za ki iya girkin ba ina Atika? ina Silifat?. Aikin mi su ke yi da ba za su yiwa yara abinci ba"
"Ka yi haƙuri ranka shi daɗe. Maman Tope ta nemi uzuri kuma ni ne na ce kar Atika ta zo saboda..."
"Kar a sake barin Yaran nan da yunwa" ya katse ta.
HaÉ—iye sauran bayanin da ta yi niyyan yi ta yi tareda faÉ—in " Insha Allahu hakan ba zai kuma faruwa ba"
Fita ta yi daga É—akin jikin ta a sanyaye.
Ba za ta ba shi laifi ba dan ta san kowanni Uba 'ya'yan sa ke zuwa farko sama da kowa amma at least ya kamata ya ba ta damar kare kan ta, watan ta É—aya kenan a gidan kuma yau ne na farko da aka samu akasi irin wannan dan miyasa ba zai ma ta uzuri ba? Dan miyasa zai ba ta laifi ba tareda ya saurareta ba...
2/11/21, 10:04 PM - ****: 53
Bismillahir Rahmanir Rahim
*Raziya*
"Yaran nan dai kin san marayu ne. Tsakani da Allah Zainan ki ke ko Zaytoonah ya za ki mu su horo da yunwa?. Yunwa fa!
" Idan ki ka muzguna mu su ma dai kin san makomar ki a wajen Allah wuta ne.
"Gaba da baya yaran nan 'yan gata ne ya kamata ki san wannan, dududu yaushe ki ka zo gidan nan amma har kin fara carelessness akan yara ƙanana kamar ba ki san zafin haihuwa ba"
Duk maganar da Hajia Ghazala ta ke yi Zaytoonah ba ta tanka ma ta ba, amma furucin ƙarshe ya sosa ma ta rai.
"Ba na tunanin kina da hurumin shigo min ɗaki ba tareda izini ba. Tunda ban gayyace ki ba ki ɗau zawarawan ƙafafuwanki ki bar min ɗaki kafin na yi abinda ranki zai ɓaci"
"Ba laifin ki ba ne ai, laifin wanda ya ajiye ki a gidan ne. Amma ki sani duk lokacin da kika walaƙanta min 'ya'ya jikin ki ne zai gaya miki"
"Out!" Ta faɗa tana nuna ma ta ƙofa.
Hajia Ghala ta buÉ—e baki za ta yi magana sai kuma ta fasa ta ja dogon tsaki ta bar É—akin.
Sai da Hajia Ghazala ta fita daga É—aki hawayen da ta ke tarewa su ka zubo.
Ba ta san zafin haihuwa ba? Ai ko ba ta taɓa haihuwa ba ba za a gaya ma ta wannan maganar banzan ba, balle kuma ta haihu, ta san wahalan ɗaukan ciki, haihuwa da reno.
Sai da ta share hawayen ta sannan ta É—au waya ta kira Mommy suna gaisawa ta ce Dan Allah Mommy ta sa Salman ya kawo ma ta yaran gobe.
"Zaytoonah Lafiya dai ko"
"Lafiya Mommy kawai na missing É—in su ne, dan Allah ki sa Salman ya kawo su ko kwana biyu ne su min"
Ta so ta yi jayayya amma yanayin da Zaytoonan ta yi magana ya karya ma ta zuciya. Al'amarin uwa da É—a sai a hankali. Ita kan ta ma kewar Zaytoonan ta ke yi duk da kuwa kullum sai sun yi waya.
"Shi kenan gobe Salman zai kawo mi ki su"
"Na gode Mommy"
"Adaeze sai dai ki cigaba da haƙuri fa. Sha'anin aure sai ka yi haƙuri sosai da kuma addu'a kafin ka samu nasara. Ki dage da addu'a dan Allah kuma ki rage saurin fushi kin ji"
"Yes Mommy"...
Hajiya Ghazala na barin É—akin Zaytoonah falon Justice ta shiga luckily kuma ta same shi yana zaune yana shan kankana.
"Sannu da aiki"
"Abu Razz ni da 'ya'ya na kuma sai ka min godiya"
"Ki kira Atika ta zo aiki kafin Silifan ta dawo"
"Na riga na kira ta ma tana hanya yanzu haka"
"Na gode" ya faÉ—a yana maida hankalin sa ga TV da ke falon.
Shiru ya ɗan ratsa madaidaicin falon na sa na lokaci kaɗan kafin Hajia Ghazala ta fara magana " na ce Ranka shi daɗe sai dai ka ƙara haƙuri fa, ka san Antyn na su akwai shiririta, akwai yarinta a tattare da ita. Na ma mata magana kuma ta gane kuskurenta gaskiya, ta ce na ƙara ba ka haƙuri dan ta ga ranka ya ɓaci sosai"
"Jazakillahu khairan"
"Amin" ta faÉ—a tana faÉ—aÉ—a murmushin ta.
Sai da ta É—an zauna na wasu mintuna kafin ta bar falon fiskarta wasai dan ta samu abinda ta ke so.
Ba ta bar gidan ba sai da Atika ta iso. Lokacin ma ta gama girka abincin dare wa yaran.
Tana isa gidan ta ko hutawa ba ta yi ba ta kira Hajia Abu ta labarta ma ta ƙarya da gaskiya na abinda ya faru. Tuni Hajia Abu ta hau faɗa kamar Ghazalar ce Zaytoonah sai da ta gama faɗan ta ce tabbas za ta ɗau mataki akan Zaytoonah.
Hajia Ghazala ta haɗa da cewa " Wallahi Hajia Galadima bai yi dacen mata ba kwata-kwata idan ba ayi da gaske ba yaran nan ba ƙaramin wahala za su sha ba a wajen ta, tunfa ba a je ko'ina ba kenan. Shi kuma kin san Galadima sanyin shi yayi yawa ba komai ya ke iya magana akai ba"
Hajia Abu ta cika ta yi fam tana faÉ—in koma mi Zaytoonah ta zo da shi za ta taka ma ta birki...
Zaytoonah tunda ta gama waya da Mommy ta tashi ta sawa ƙofarta key. Da Hajiya Ghazalar da Justice da ma yaran duk haushin su ta ke ji. Ba ta sake fitowa ba har sai washegari ko abinci ba ta ci ba.
Washegari sai kusan ƙarfe goma ta fito ta nemi abin karyawa.
Bayan ta cika cikin ta tukunna ta koma sama ta shiga ɗakin Justice ta gyara ma sa. Da ke akwai ƙaramin lambu a ta bayan gidan duk weekend da safe Justice a nan ya ke zama ya yiwa flowers bayi ya gyara wajen.
Da ta gama ta koma ɗaki ta kira Salman a waya wanda ya ce ma ta suna hanya zuwa ƙarfe shabiyu za su iya isowa.
A ranta ta yi alƙawarin ba za ta kuma karambani yiwa kowa girki ba har kuwa da shi mai gidan. Ai kafin zuwanta abincin su Atika ya ke ci dan haka ya cigaba. Tunda ya nuna baya so ta dinga barin ma sa yara a yunwa gara ta tsame hannun ta daga lamarin girkin gidan tunda dai ita ba ta kai a ma ta uzuri ba.
Ta zo saukowa ta hango Justice yana shigowa dan haka ta fasa ta koma É—akin ta. She just cant stand him bayan abinda ya ma ta jiya.
Tana kitchen É—in yaran su ka dawo, duk cikin su Suhailah ce ta shigo ta ma ta oyoyo kafin ta wuce wajen yayyen ta da tuni su ka kunna TV suna kallon wani favourite show É—in su.
Tana gama soya nama ta kashe gas ɗin ta bar kitchen ɗin da sauri. Tun da ta tashi a bacci kitchen ta wuco saboda sauri to kuma yanzu wani fitsari ke cinta dole ta ajiye girkin ta kashe gas ɗin ta tafi ɗaki. Da ta je fitsarin ma sai da ta tsaya ta gyara jikin ta sosai saboda dama tana tareda baƙo. Ta fito daga banɗaki kenan ta ji ihun Suhailah a ƙasa, ba shiri ta fito a guje.
A kitchen ta samu yaran suna tsaye wajen Suhailah da ke zunduma ihu saboda man da ya tsartu ma ta a jiki.
Zaytoonah ta yi kan ta da sauri tana tambayar miya faru amma babu wanda ya kulata saboda Suhailan kuka kawai take yi.
Ta san dai idan mai ya tsartu wa mutum tun lokacin suna yara Mommy na amfani da gishiri ko kamu ta mutsutstsuka wajen, idan kuma akwai Zuma sai ta shafa mu su.
Da sauri ta buÉ—e roban gishiri ta É—ebo ta fara shafawa Suhailah a wuya da hannun ta.
Raziya na cewa ta barta a kai ta Asibiti. Sai da ta gama shafa ma ta ta É—auki Suhailah a kafaÉ—a su ka fito a kitchen É—in dai dai nan kuma Justice ya shigo gidan.
"Miya faru?" Ya faɗa yana karɓan Suhailah a hannun Zaytoonan. Yarinya kuma ganin Daddyn ta kawai sai ta ƙara sautin kuka.
Raziya ce ta yi saurin faÉ—in " Yunwa ta ke ji shine ta shiga kitchen wajen Anty ita kuma ba ta kitchen É—in kuma ta bar Mai mai zafi a wajen sai ya zubowa Suhailah a jiki"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun" kawai ya faÉ—a yai hanyar waje bayan ya yiwa Zaytoonah wani kallo.
Bayan fitar su da ƙyar Zaytoonah ta iya saita kan ta ta shiga kitchen ta goge wajen da man ya zuba ta ƙarisa girkin a gurguje.
Bayan ta gama girkin zama ta yi a falo ta yi tagumi tana jiran dawowar su.
Ta sani naman da ta soya ta ke son zubawa a miya yarinyar ta je ɗauka ta ga ƙaramar kujera a wajen alamar shi ta hau saboda tsayin ta ya kai wajen. By mistake ne ƙila hannunta ya bugi frying pan da ke gefen bowl ɗin da ta zuba naman shine Man ya tsirtu ma ta sauran kuma ya malale a ƙasa.
Kusan awa biyu da fitar su sai gashi sun dawo abin mamaki har da Hajia Ghazala dan ita ce ma ke riƙe da Suhailan wacce ke riƙe da ice cream tana sha hankali kwance an shafa ma ta magani a wajen da man ya zuba raɗaɗin da ta ke ji ya ragu.
Ko kallon Zaytoonah bai yi ba ya wuce sama.
Sai da ta sauke ajiyar zuciya kafin ta bi bayan sa ba tareda ta yiwa Hajia Ghazala magana ba.
Kai tsaye É—akin sa ta shiga dan ba ta gan shi a falon sa ba.
"Daddyn Raziya ka yi haƙuri, wallahi ban san za ta shiga kitchen ɗin ba i just..."
"Ƙarfe nawa Zaytoon ba a gama abincin rana ba?. Idan ke ba za ki iya girkin ba ina Atika? ina Silifat?. Aikin mi su ke yi da ba za su yiwa yara abinci ba"
"Ka yi haƙuri ranka shi daɗe. Maman Tope ta nemi uzuri kuma ni ne na ce kar Atika ta zo saboda..."
"Kar a sake barin Yaran nan da yunwa" ya katse ta.
HaÉ—iye sauran bayanin da ta yi niyyan yi ta yi tareda faÉ—in " Insha Allahu hakan ba zai kuma faruwa ba"
Fita ta yi daga É—akin jikin ta a sanyaye.
Ba za ta ba shi laifi ba dan ta san kowanni Uba 'ya'yan sa ke zuwa farko sama da kowa amma at least ya kamata ya ba ta damar kare kan ta, watan ta É—aya kenan a gidan kuma yau ne na farko da aka samu akasi irin wannan dan miyasa ba zai ma ta uzuri ba? Dan miyasa zai ba ta laifi ba tareda ya saurareta ba...
2/11/21, 10:04 PM - ****: 53
Bismillahir Rahmanir Rahim
*Raziya*
"Yaran nan dai kin san marayu ne. Tsakani da Allah Zainan ki ke ko Zaytoonah ya za ki mu su horo da yunwa?. Yunwa fa!
" Idan ki ka muzguna mu su ma dai kin san makomar ki a wajen Allah wuta ne.
"Gaba da baya yaran nan 'yan gata ne ya kamata ki san wannan, dududu yaushe ki ka zo gidan nan amma har kin fara carelessness akan yara ƙanana kamar ba ki san zafin haihuwa ba"
Duk maganar da Hajia Ghazala ta ke yi Zaytoonah ba ta tanka ma ta ba, amma furucin ƙarshe ya sosa ma ta rai.
"Ba na tunanin kina da hurumin shigo min ɗaki ba tareda izini ba. Tunda ban gayyace ki ba ki ɗau zawarawan ƙafafuwanki ki bar min ɗaki kafin na yi abinda ranki zai ɓaci"
"Ba laifin ki ba ne ai, laifin wanda ya ajiye ki a gidan ne. Amma ki sani duk lokacin da kika walaƙanta min 'ya'ya jikin ki ne zai gaya miki"
"Out!" Ta faɗa tana nuna ma ta ƙofa.
Hajia Ghala ta buÉ—e baki za ta yi magana sai kuma ta fasa ta ja dogon tsaki ta bar É—akin.
Sai da Hajia Ghazala ta fita daga É—aki hawayen da ta ke tarewa su ka zubo.
Ba ta san zafin haihuwa ba? Ai ko ba ta taɓa haihuwa ba ba za a gaya ma ta wannan maganar banzan ba, balle kuma ta haihu, ta san wahalan ɗaukan ciki, haihuwa da reno.
Sai da ta share hawayen ta sannan ta É—au waya ta kira Mommy suna gaisawa ta ce Dan Allah Mommy ta sa Salman ya kawo ma ta yaran gobe.
"Zaytoonah Lafiya dai ko"
"Lafiya Mommy kawai na missing É—in su ne, dan Allah ki sa Salman ya kawo su ko kwana biyu ne su min"
Ta so ta yi jayayya amma yanayin da Zaytoonan ta yi magana ya karya ma ta zuciya. Al'amarin uwa da É—a sai a hankali. Ita kan ta ma kewar Zaytoonan ta ke yi duk da kuwa kullum sai sun yi waya.
"Shi kenan gobe Salman zai kawo mi ki su"
"Na gode Mommy"
"Adaeze sai dai ki cigaba da haƙuri fa. Sha'anin aure sai ka yi haƙuri sosai da kuma addu'a kafin ka samu nasara. Ki dage da addu'a dan Allah kuma ki rage saurin fushi kin ji"
"Yes Mommy"...
Hajiya Ghazala na barin É—akin Zaytoonah falon Justice ta shiga luckily kuma ta same shi yana zaune yana shan kankana.
"Sannu da aiki"
"Abu Razz ni da 'ya'ya na kuma sai ka min godiya"
"Ki kira Atika ta zo aiki kafin Silifan ta dawo"
"Na riga na kira ta ma tana hanya yanzu haka"
"Na gode" ya faÉ—a yana maida hankalin sa ga TV da ke falon.
Shiru ya ɗan ratsa madaidaicin falon na sa na lokaci kaɗan kafin Hajia Ghazala ta fara magana " na ce Ranka shi daɗe sai dai ka ƙara haƙuri fa, ka san Antyn na su akwai shiririta, akwai yarinta a tattare da ita. Na ma mata magana kuma ta gane kuskurenta gaskiya, ta ce na ƙara ba ka haƙuri dan ta ga ranka ya ɓaci sosai"
"Jazakillahu khairan"
"Amin" ta faÉ—a tana faÉ—aÉ—a murmushin ta.
Sai da ta É—an zauna na wasu mintuna kafin ta bar falon fiskarta wasai dan ta samu abinda ta ke so.
Ba ta bar gidan ba sai da Atika ta iso. Lokacin ma ta gama girka abincin dare wa yaran.
Tana isa gidan ta ko hutawa ba ta yi ba ta kira Hajia Abu ta labarta ma ta ƙarya da gaskiya na abinda ya faru. Tuni Hajia Abu ta hau faɗa kamar Ghazalar ce Zaytoonah sai da ta gama faɗan ta ce tabbas za ta ɗau mataki akan Zaytoonah.
Hajia Ghazala ta haɗa da cewa " Wallahi Hajia Galadima bai yi dacen mata ba kwata-kwata idan ba ayi da gaske ba yaran nan ba ƙaramin wahala za su sha ba a wajen ta, tunfa ba a je ko'ina ba kenan. Shi kuma kin san Galadima sanyin shi yayi yawa ba komai ya ke iya magana akai ba"
Hajia Abu ta cika ta yi fam tana faÉ—in koma mi Zaytoonah ta zo da shi za ta taka ma ta birki...
Zaytoonah tunda ta gama waya da Mommy ta tashi ta sawa ƙofarta key. Da Hajiya Ghazalar da Justice da ma yaran duk haushin su ta ke ji. Ba ta sake fitowa ba har sai washegari ko abinci ba ta ci ba.
Washegari sai kusan ƙarfe goma ta fito ta nemi abin karyawa.
Bayan ta cika cikin ta tukunna ta koma sama ta shiga ɗakin Justice ta gyara ma sa. Da ke akwai ƙaramin lambu a ta bayan gidan duk weekend da safe Justice a nan ya ke zama ya yiwa flowers bayi ya gyara wajen.
Da ta gama ta koma ɗaki ta kira Salman a waya wanda ya ce ma ta suna hanya zuwa ƙarfe shabiyu za su iya isowa.
A ranta ta yi alƙawarin ba za ta kuma karambani yiwa kowa girki ba har kuwa da shi mai gidan. Ai kafin zuwanta abincin su Atika ya ke ci dan haka ya cigaba. Tunda ya nuna baya so ta dinga barin ma sa yara a yunwa gara ta tsame hannun ta daga lamarin girkin gidan tunda dai ita ba ta kai a ma ta uzuri ba.
Ta zo saukowa ta hango Justice yana shigowa dan haka ta fasa ta koma É—akin ta. She just cant stand him bayan abinda ya ma ta jiya.