Sashe 16
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tureshi ta yi ta yi hanyar fita ya jawota da ƙarfi.
"Okafor ka bar ni, ba na son ka, na ce ba na..."
Danneta yai da ƙarfi akan kujera yana shirin ɗaga mata skirt ta fara kuka tana roƙon sa amma bai saurareta ba sai ma rufe ma ta baki da yai yana ƙoƙarin kunce belt ɗin sa.
Mama Okafor ta sa key ta buɗe ƙofa dan dama ba ta ran za ta samu kowa a gidan ba. Sauran su na shago shi kuwa Okafor da ya zo gida wanka ta tabbata ya riga ya tafi dan ya jima da barin shagon.
"Okafor!" Ta faɗa da ƙarfi lokacin da ta ga abinda ɗan ta ke shirin aikatawa.
Da sauri ya miƙe jikinsa na rawa ya fara ƙoƙarin zuge zip ɗin wandon sa amma ya ka sa. Mama Okafor ta ƙaraso ta ɗauke shi da mari.
"Shame on you Okafor"
Ta faɗa ta koma kan Nkiru da ke ta kuka. Rarrashin ta ta farayi tana ba ta haƙuri, sai da ta tabbatar ta nitsu sannan ta ɗauko ma ta zani ta ɗaura saboda skirt ɗin ta ya yage. Ba dan ta zo da wuri ba da mai afkuwa ta afku. Ta so Nkiru ta zauna har Papa Okafor ya dawo amma ta ce gida za ta je dan haka dole da kanta ta raka Nkirun har gidan su T J, a hanya ta cigaba da ba ta haƙuri tana cewa ta gafartawa Okafor ba ta san a ina ya ɗauko banzan halin nan ba.
Da ta je gida kuwa zazzaɓi ya rufeta, kewan T J ya ƙara shigarta, ashe gaskiyar T J da ya ce ta yi hankali da Okafor ta dena keɓewa da shi. Yau ba dan Mama ta zo ba da shikenan, ita ko first kiss ba ta taɓa yi ba balle wani abun daban...
Tun daga wannan lokaci ta ɗaukewa gidan su Okafor ƙafa, magana ta je gaban Pastor aka kira ta aka ba ta haƙuri amma ita ta ƙi yarda ta koma gidan, wasa-wasa ma ta fara ja baya da zuwa church ɗin. Kuɗin da su ke ba ta duk wata kuwa ta ce ba ta so saboda kuɗin da ta ke samu a wajen aiki ya isheta. Haka dai ta fara nisanta kan ta da su. Daga makaranta sai gida. Ko kitso za ta yi sai dai ta je gidan su wata student ɗin ta Folake wacce mamanta ke kitso.
Wasa-wasa sai ga shi watanni uku sun shige ana irga kwanakin dawowan T J a lokacin ne kuwa aka fara Azumin Ramadan. A nan Nkiru ta ga abubuwan mamaki, domin tana mamakin yadda dukkan gidan su ke ɗaukan Azumi har ɗokin Azumin ake yi kafin zuwan sa. Ba abinda ke ƙara burgeta irin lokacin sallar Taraweeh, daga ɗaki tana jin yadda su ke daɗewa su na sallah ga karatun da ke burgeta. Abokanan ta Malamai kam sun sha tambayoyi akan Azumi saboda ko ta tambayi Pendo ba ta iya ba ta amsa saboda ƙarancin ilimi da ta ke da shi. Ranan Azumi na goma sha ɗaya ta ce bari ta gwada Azumi tunda har 'yar Pendo ma na yi, ta ƙi cin abinci tun safe har yamma da ta gayawa Pendo tana Azumi sai ta ringa ma ta dariya ta ce gara ta ci abinci dan ba ta da lada. Ita kuwa ta ƙi haka ta kai Azumin da ƙyar.
Haka ta cigaba da ɗaukan Azumin, Pendo da Yadikko su yi ta ma ta dariya, Goggo kuwa ta ce idan tana da rabon musulunci za ta karɓa a barta ta yi Azumin tunda da kan ta ta ji tana son yi.
A ranan Azumi na sha bakwai T J ya dira a gidan. Zo ka ga murna a wajen 'yan gidan, amma duk ciki babu wanda ya kai Nkiru murnan dawowan sa. Lokacin da ya shigo gaida Goggo haka ta tsura ma sa ido tana ji kamar ta je ta rungumeshi. Shi kam bayan ya kalleta sau É—aya bai sake waiwayarta ba, ba wai dan baya son kallonta ba ne sai dan saboda an cika É—akin Goggon kar a ma sa sa'ido. Bayan ya fita haka Nkiru ta rakashi da ido tana ganin ya rame ma ta ko dan Azumi da ake yi ne oho.
"I miss you" ta furta a hankali.
Wannan karan ko dan saboda Azumi ne T J ba ya ba ta lokaci kamar da, kwana uku yai ya koma masallaci Ittikafi saboda goman ƙarshe da aka shiga. Hakan ya sa Nkiru ta dena ganin sa, sau ɗaya su ka zauna su ka yi hira wanda shima sama-sama ne.
Ana washegari sallah aka kawo ma ta kaya kala huɗu, ɗaya Baffan su T J ne ya siya ma ta sauran kuma T J ne ya siya. Ta ji daɗin karramata da aka yi duk da kuwa ba ta san matsayin sallar da za ayi goben ba hakanan ba ta san ya ake yi ba. Ranan sallah kuwa ya banbanta da kowacce rana da ta zauna a gidan, babu wanda bai yi shiga mai kyau ba a gidan. Ga abinci da aka yi da nama dumu-dumu a ciki. Safiyar sallah ta ga T J wanda shima ya sha ado cikin shadda light blue, ba ƙaramin kyau ya yi ba. Da yammacin sallah kuwa T J ya ɗauketa su ka fita yawo a nan ne take gaya ma sa itama ta yi Azumi har goma shabiyu.
"Ya ki ka ji da ki ka yi Azumin?" Abinda ya tambaya kenan
"I feel good" ta amsa tana murmushi...
Washe gari sai ga Muntari wai ya zo É—aukan Nkiru wai za su tafi Kano ta ga hawan daushe. Ta ce ya tambayi T J shikuwa ya ce ba zai tambaya ba T J bai da hurumin hanata tafiya inda ta yi niyya. Ita kuwa ta ce ba inda za ta, yayi-yayi ta ce ba za ta je ba, haka yai fushi ya fita yana jin haushin T J a ran sa.
Shima T J ya so su je Kano É—in kawai wa su lissafi yai ya ga bai dace ba a wannan lokaci...
***
"Barkindo kana da niyyar aure kuwa?"
T J ya sunkuyar da kai yana jin tsananin kunyar mahaifin sa.
"Karatu daga wannan sai wannan, shi karatun ai ba zai hana aure ba. Duk sa'anninka fa suna da mata da 'ya'ya"
"Baffa wannan karan karatun ba zai yi tsawo ba, shekara É—aya ne zan yi na gama"
"Wallahi ana min surutu Shehu, ko dai ba ka da lafiya ne?"
T J yai saurin girgiza kai
"To dan Allah ka haƙura da batun karatun nan tukunna, ka yi aure. Idan da hali sai ka cigaba da karatun, a hakan ma ai kana cikin 'yan tsirarun da su ka kai matakin karatun ka a nan garin"
Bai san ya zai yi da ran sa ba idan ya amince da aure yanzu, bai shirya aure ba, baya tunanin zai iya zama da wata mace yanzu ko da ya zauna ba za ta samu kan sa ba.
Ya ɗan tausasa murya ya ce " Baffa idan da hali a ɗan ɗaga min ƙafa zuwa shekara ɗayan nan, Insha Allahu ina gama karatun nan zan yi aure"
"Ka yi alƙawarin bayan shekara ɗaya idan ba ka yi aure ba ni na maka?"
Ya É—ago ido da sauri ya kalli mahaifin na sa wanda ko kaÉ—an ba alamar wasa a tattare da shi.
"Na amince" ya furta a hankali...
Cikin watanni huɗu da T J yai kafin ya fara masters na shi ya jawo wata muguwar shaƙuwa tsakanin sa da Nkiru fiye da da. A ɓangaren Muntari ma duk wani dama da ya samu ƙoƙarin gwadawa Nkiru kulawa ya ke yi. Shi a yadda ya fara ji ma yana ga zai wa Baffa magana a aura ma sa Nkiru kawai tunda Malamai sun ce zai iya aurenta ko da ba ta musulunta ba. Hakan ya sa watarana da ya zo gida ya samu Baffa da maganar. Baffa da ya ji maganar sai da ya ƙware da ruwan da ya ke sha.
"Baffa ina son ta, ka ga idan na aure ko shekara ba za ayi ba na tabbata za ta musulunta ka ga na yi jihadi kenan"
"Tashi ka bani waje"
"Baffa.."
"Tashi na ce" haka Muntari ya tashi simi-simi ya fita yana ƙunƙuni.
Ganin bai samu kan Baffa ba ne ya sa shi komawa kan Goggo akan ta taimaka ta yiwa Baffa magana.
Haka dai Goggo ta ji maganganun sa banbaraƙwai. Amma ta san halin Muntarin na taurin kai dan haka ta ce "yo kai Muntari yarinyar nan fa ba wanda ya isa ya ma ta auren dole a gidan nan ko da kuwa musulunta ta yi. Ka cigaba da jawota zuwa musulunci ƙila idan da rabo sai ta amsa ka ga sai a zo ayi maganar aure amma yanzu kam na san ba wanda zai yarda ma ka, kuma ina tabbatar ma ka da idan Iya ta ji maganar nan sai kashin Mary ya bushe a gidan nan"
Da wannan ya sa ya chanja tunani ya ajiye maganar. Ya cigaba da kyautatawa Nkiru shi a ganin sa hakan zai sa ta ji son musulunci.
Duk abunda ake yi T J bai sani ba dan ko da ya dawo ba wanda ya ma sa maganar abinda Muntari ya faɗa. Duk sati biyu ya ke zuwa Ringim ba dan komai ba kuwa sai dan Nkiru. Shi kam yanzu ya amince da maganar Eze, ko da kuwa a da yana son ƙaryata hakan to yanzu kam duk jikinsa ya amsa da soyayyar Nkiru. Kullum addu'ar shi Allah ya kawo ma sa mafita kafin ya ƙare masters ɗin sa Baffah ya tuntuɓeshi da maganar aure. Baya ganin zai iya juran auren wata mace idan ba Nkiru ba duk da kuwa ya san hakan ba mai yiwuwa ba ne...
"Okafor ka bar ni, ba na son ka, na ce ba na..."
Danneta yai da ƙarfi akan kujera yana shirin ɗaga mata skirt ta fara kuka tana roƙon sa amma bai saurareta ba sai ma rufe ma ta baki da yai yana ƙoƙarin kunce belt ɗin sa.
Mama Okafor ta sa key ta buɗe ƙofa dan dama ba ta ran za ta samu kowa a gidan ba. Sauran su na shago shi kuwa Okafor da ya zo gida wanka ta tabbata ya riga ya tafi dan ya jima da barin shagon.
"Okafor!" Ta faɗa da ƙarfi lokacin da ta ga abinda ɗan ta ke shirin aikatawa.
Da sauri ya miƙe jikinsa na rawa ya fara ƙoƙarin zuge zip ɗin wandon sa amma ya ka sa. Mama Okafor ta ƙaraso ta ɗauke shi da mari.
"Shame on you Okafor"
Ta faɗa ta koma kan Nkiru da ke ta kuka. Rarrashin ta ta farayi tana ba ta haƙuri, sai da ta tabbatar ta nitsu sannan ta ɗauko ma ta zani ta ɗaura saboda skirt ɗin ta ya yage. Ba dan ta zo da wuri ba da mai afkuwa ta afku. Ta so Nkiru ta zauna har Papa Okafor ya dawo amma ta ce gida za ta je dan haka dole da kanta ta raka Nkirun har gidan su T J, a hanya ta cigaba da ba ta haƙuri tana cewa ta gafartawa Okafor ba ta san a ina ya ɗauko banzan halin nan ba.
Da ta je gida kuwa zazzaɓi ya rufeta, kewan T J ya ƙara shigarta, ashe gaskiyar T J da ya ce ta yi hankali da Okafor ta dena keɓewa da shi. Yau ba dan Mama ta zo ba da shikenan, ita ko first kiss ba ta taɓa yi ba balle wani abun daban...
Tun daga wannan lokaci ta ɗaukewa gidan su Okafor ƙafa, magana ta je gaban Pastor aka kira ta aka ba ta haƙuri amma ita ta ƙi yarda ta koma gidan, wasa-wasa ma ta fara ja baya da zuwa church ɗin. Kuɗin da su ke ba ta duk wata kuwa ta ce ba ta so saboda kuɗin da ta ke samu a wajen aiki ya isheta. Haka dai ta fara nisanta kan ta da su. Daga makaranta sai gida. Ko kitso za ta yi sai dai ta je gidan su wata student ɗin ta Folake wacce mamanta ke kitso.
Wasa-wasa sai ga shi watanni uku sun shige ana irga kwanakin dawowan T J a lokacin ne kuwa aka fara Azumin Ramadan. A nan Nkiru ta ga abubuwan mamaki, domin tana mamakin yadda dukkan gidan su ke ɗaukan Azumi har ɗokin Azumin ake yi kafin zuwan sa. Ba abinda ke ƙara burgeta irin lokacin sallar Taraweeh, daga ɗaki tana jin yadda su ke daɗewa su na sallah ga karatun da ke burgeta. Abokanan ta Malamai kam sun sha tambayoyi akan Azumi saboda ko ta tambayi Pendo ba ta iya ba ta amsa saboda ƙarancin ilimi da ta ke da shi. Ranan Azumi na goma sha ɗaya ta ce bari ta gwada Azumi tunda har 'yar Pendo ma na yi, ta ƙi cin abinci tun safe har yamma da ta gayawa Pendo tana Azumi sai ta ringa ma ta dariya ta ce gara ta ci abinci dan ba ta da lada. Ita kuwa ta ƙi haka ta kai Azumin da ƙyar.
Haka ta cigaba da ɗaukan Azumin, Pendo da Yadikko su yi ta ma ta dariya, Goggo kuwa ta ce idan tana da rabon musulunci za ta karɓa a barta ta yi Azumin tunda da kan ta ta ji tana son yi.
A ranan Azumi na sha bakwai T J ya dira a gidan. Zo ka ga murna a wajen 'yan gidan, amma duk ciki babu wanda ya kai Nkiru murnan dawowan sa. Lokacin da ya shigo gaida Goggo haka ta tsura ma sa ido tana ji kamar ta je ta rungumeshi. Shi kam bayan ya kalleta sau É—aya bai sake waiwayarta ba, ba wai dan baya son kallonta ba ne sai dan saboda an cika É—akin Goggon kar a ma sa sa'ido. Bayan ya fita haka Nkiru ta rakashi da ido tana ganin ya rame ma ta ko dan Azumi da ake yi ne oho.
"I miss you" ta furta a hankali.
Wannan karan ko dan saboda Azumi ne T J ba ya ba ta lokaci kamar da, kwana uku yai ya koma masallaci Ittikafi saboda goman ƙarshe da aka shiga. Hakan ya sa Nkiru ta dena ganin sa, sau ɗaya su ka zauna su ka yi hira wanda shima sama-sama ne.
Ana washegari sallah aka kawo ma ta kaya kala huɗu, ɗaya Baffan su T J ne ya siya ma ta sauran kuma T J ne ya siya. Ta ji daɗin karramata da aka yi duk da kuwa ba ta san matsayin sallar da za ayi goben ba hakanan ba ta san ya ake yi ba. Ranan sallah kuwa ya banbanta da kowacce rana da ta zauna a gidan, babu wanda bai yi shiga mai kyau ba a gidan. Ga abinci da aka yi da nama dumu-dumu a ciki. Safiyar sallah ta ga T J wanda shima ya sha ado cikin shadda light blue, ba ƙaramin kyau ya yi ba. Da yammacin sallah kuwa T J ya ɗauketa su ka fita yawo a nan ne take gaya ma sa itama ta yi Azumi har goma shabiyu.
"Ya ki ka ji da ki ka yi Azumin?" Abinda ya tambaya kenan
"I feel good" ta amsa tana murmushi...
Washe gari sai ga Muntari wai ya zo É—aukan Nkiru wai za su tafi Kano ta ga hawan daushe. Ta ce ya tambayi T J shikuwa ya ce ba zai tambaya ba T J bai da hurumin hanata tafiya inda ta yi niyya. Ita kuwa ta ce ba inda za ta, yayi-yayi ta ce ba za ta je ba, haka yai fushi ya fita yana jin haushin T J a ran sa.
Shima T J ya so su je Kano É—in kawai wa su lissafi yai ya ga bai dace ba a wannan lokaci...
***
"Barkindo kana da niyyar aure kuwa?"
T J ya sunkuyar da kai yana jin tsananin kunyar mahaifin sa.
"Karatu daga wannan sai wannan, shi karatun ai ba zai hana aure ba. Duk sa'anninka fa suna da mata da 'ya'ya"
"Baffa wannan karan karatun ba zai yi tsawo ba, shekara É—aya ne zan yi na gama"
"Wallahi ana min surutu Shehu, ko dai ba ka da lafiya ne?"
T J yai saurin girgiza kai
"To dan Allah ka haƙura da batun karatun nan tukunna, ka yi aure. Idan da hali sai ka cigaba da karatun, a hakan ma ai kana cikin 'yan tsirarun da su ka kai matakin karatun ka a nan garin"
Bai san ya zai yi da ran sa ba idan ya amince da aure yanzu, bai shirya aure ba, baya tunanin zai iya zama da wata mace yanzu ko da ya zauna ba za ta samu kan sa ba.
Ya ɗan tausasa murya ya ce " Baffa idan da hali a ɗan ɗaga min ƙafa zuwa shekara ɗayan nan, Insha Allahu ina gama karatun nan zan yi aure"
"Ka yi alƙawarin bayan shekara ɗaya idan ba ka yi aure ba ni na maka?"
Ya É—ago ido da sauri ya kalli mahaifin na sa wanda ko kaÉ—an ba alamar wasa a tattare da shi.
"Na amince" ya furta a hankali...
Cikin watanni huɗu da T J yai kafin ya fara masters na shi ya jawo wata muguwar shaƙuwa tsakanin sa da Nkiru fiye da da. A ɓangaren Muntari ma duk wani dama da ya samu ƙoƙarin gwadawa Nkiru kulawa ya ke yi. Shi a yadda ya fara ji ma yana ga zai wa Baffa magana a aura ma sa Nkiru kawai tunda Malamai sun ce zai iya aurenta ko da ba ta musulunta ba. Hakan ya sa watarana da ya zo gida ya samu Baffa da maganar. Baffa da ya ji maganar sai da ya ƙware da ruwan da ya ke sha.
"Baffa ina son ta, ka ga idan na aure ko shekara ba za ayi ba na tabbata za ta musulunta ka ga na yi jihadi kenan"
"Tashi ka bani waje"
"Baffa.."
"Tashi na ce" haka Muntari ya tashi simi-simi ya fita yana ƙunƙuni.
Ganin bai samu kan Baffa ba ne ya sa shi komawa kan Goggo akan ta taimaka ta yiwa Baffa magana.
Haka dai Goggo ta ji maganganun sa banbaraƙwai. Amma ta san halin Muntarin na taurin kai dan haka ta ce "yo kai Muntari yarinyar nan fa ba wanda ya isa ya ma ta auren dole a gidan nan ko da kuwa musulunta ta yi. Ka cigaba da jawota zuwa musulunci ƙila idan da rabo sai ta amsa ka ga sai a zo ayi maganar aure amma yanzu kam na san ba wanda zai yarda ma ka, kuma ina tabbatar ma ka da idan Iya ta ji maganar nan sai kashin Mary ya bushe a gidan nan"
Da wannan ya sa ya chanja tunani ya ajiye maganar. Ya cigaba da kyautatawa Nkiru shi a ganin sa hakan zai sa ta ji son musulunci.
Duk abunda ake yi T J bai sani ba dan ko da ya dawo ba wanda ya ma sa maganar abinda Muntari ya faɗa. Duk sati biyu ya ke zuwa Ringim ba dan komai ba kuwa sai dan Nkiru. Shi kam yanzu ya amince da maganar Eze, ko da kuwa a da yana son ƙaryata hakan to yanzu kam duk jikinsa ya amsa da soyayyar Nkiru. Kullum addu'ar shi Allah ya kawo ma sa mafita kafin ya ƙare masters ɗin sa Baffah ya tuntuɓeshi da maganar aure. Baya ganin zai iya juran auren wata mace idan ba Nkiru ba duk da kuwa ya san hakan ba mai yiwuwa ba ne...