Sashe 37
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shekaru shabakwai da su ka wuce Muntari ya tafi Lagos. Aiki ya ke tuƙuru shi a ganin sa hakan zai sa ya samu kuɗi. Duk wani aikin wahala indai akwai kuɗi to yana nan. Shekaru biyu yai yaga bai wani tara abin a zo a gani ba, har yana son jona aikin wani abokin shi wato sata sai kuma labari ya chanja lokacin da ya haɗu da Madam Talatu.
Madam Talatu tsohuwar karuwa ce da ta yi tashe a zamaninta. 'Yar Kafanchang ne da ke Jihar Kaduna, auren dole za a ma ta ta gudu wai ta shiga duniya. A garin Lagos ta tsinci kan ta bayan doguwar tafiya da ta yi. Bayan ta samu masauki a gidan karuwai ta shiga karuwanci, ba ta da wani kyaun fiska amma akwai ta da kyaun diri, irin wanda ke ɗauke hankalin duk wanda yai tozali da ita. Cikin loƙaci kaɗan ta zama ɗaya daga cikin manya-manyan karuwai da ake ji da su a Lagos, wanda Turawa ke ɗauka, 'yan siyasa da manya manyan sojoji ke rububi. Daga gidan karuwai ta ɓalle ta samu gidan kanta ta zauna wanda cikin kuɗaɗen da ta tara ne ta siya da shi. Ta yi karuwanci na shekaru talatin kafin ta yi retire ta bazama kasuwanci, dama tana ɗan taɓa kasuwancin amma yanzu da ta dena karuwanci sai ta riƙe kasuwanci zallah.
To abu ne da ta jima tana tatsan kuɗi daga mazan da ba sa iya kama abun su, dan haka ba ƙaramin maƙudan kuɗi gareta ba. Tana da manya-manyan shaguna da kuma hannun jari.
Bayan ta bar karuwanci ta kan dai nemi yara ƙanana wanda za su biya ma ta buƙata lokaci zuwa lokaci ita kuma ta ba su kuɗi.
Lokacin da ta haÉ—u da Muntari tana shekaru Arba'in da takwas a duniya. Ta gan shi ne lokacin da su ka zo sauke ma ta kaya a É—aya daga cikin shagunan ta. Nan da nan É—an farin Bafulatanin ya burgeta. Bayan ta nemi ganin shi ta ce ya zo washegari za ta bashi aiki. Ganin kuÉ—in da za a dinga bashi a wata ya ninka wanda ya ke samu a da ya sa shi amincewa da aikin.
Yana aiki da Madam Talatu ita kuma tana daɗa lura da shi, bayan wata biyu ta fito ma sa da maitar ta fili, ya ce baya so. Ta sanar da shi kuɗin da za ta dinga bashi duk wata idan ya amince amma still bai amince ba. Da ta dameshi sai ya ajiye aikin da ya ke yi ya kama gaban sa. Bayan ya tafi ta kasa haƙuri da shi ta neme shi ya dawo tareda ma sa alkawarin aure ta ke so su yi kuma indai ya amince to za ta ba shi ɗaya daga cikin shagunan ta, da yai lissafi sai ya ga arziƙi ne ya zo ma sa cikin sauƙi. Auren shekara goma su ka yi alƙawarin za su yi da shi kafin nan zai saketa ya kama gaban sa.
Bayan sun yi Aure kuwa ta bashi ɗaya daga cikin shagunan ta ya zama shi ke sarrafa shi. Ta sa mishi ido sosai akan ko zai ci amanarta kaman sauran ƙananun samarin da ta ke yi sai taga shi Muntari ba ruwan sa da mata. Daga baya ta tambayeshi dalilin zuwansa Lagos ya ce ma ta ya zo neman kuɗi ne saboda matar da ya ke so.
A mafiya yawancin lokutan da ya ke saduwa da ita yana ambatun ta da Maryam hakan ya sa ta san ba ƙaramin so ya kewa wannan Maryam ɗin ba.
Shi kuwa Muntari saboda a dole ya ke tarayya da Madam Talatu ya sa ya fara shan giya da sigari saboda ya dinga É—auke ma sa hankali a duk lokacin da ya ke tarayya da ita, hakan ya sa ya ke ganin Maryam a tareda shi a lokacin da ya ke tare da Madam Talatu.
Cikin shekaru tara da su ka yi tare yana aika kaya Kano ana sayar ma sa da shi hakan ya sa kasuwancin sa ya haɓaka sosai ga shi ba shi da matsalar komai, cin sa da shan sa da suturan sa duk Madam Talatu ce.
Bayan shekara tara da auren su MadamTalata ta fara jinya ashe cervical cancer ne. Ana magani ana jigilar asibiti amma abin ya mata mugun kamu saboda ba a gane shi ke damunta ba da wuri. Ganin fa kullum jigilar Asibiti ake ya sa Madam Talatu ta fara tunanin iyayenta da 'yan uwanta da ta baro shekaru ma su yawa da su ka wuce. A da ƙasar waje Muntari zai fita da ita ta ce ta fasa ya kaita Kafanchang za ta nemi iyayenta su gafarta ma ta. Da su ka je ta samu mahaifinta yana nan amma mahaifiyarta ta jima da rasuwa. Yayyenta da ƙannenta da ba ta san su ba kafin ta tafi duk sun girma suna da iyali. Anyi koke-koke kafin daga baya aka karɓeta hannu bibbiyu.
Saura wata biyar shekara goman auren su ta cika Madam Talatu ta ce Muntari ya saketa saboda tana son zama da 'yan uwanta zuwa lokacin da za ta mutu.
Cikin kaso ɗari na dukiyarta kusan kashi talatin ta ba wa Muntari wanda shima a lokacin side business ɗin sa ya haɓaka sosai. Sauran dukiyarta kuwa 'yan uwanta ta rabawa sannan aka gina Makaranta da Asibiti a ƙauyen su da ke Kafanchang. Shekara ɗaya bayan rabuwar su da Muntari ta rasu.
Shi kuwa Muntari tunda su ka rabu da Madam Talatu ya fara ƙoƙarin yadda zai dawo da kasuwancin sa Kano saboda ya kasance kusa da masoyiyar sa. A shekaran ne kuma ya tafi Umara dan ya fito a Alhaji ya bawa kowa mamaki.
Tunda kuÉ—i su ka fara zama ma sa ya fara bibiyan labarin É—an uwansa Tijjani da kuma halin da masoyiyar sa ke ciki. Bai sha wahalar samun information da ya ke so ba. Nan ta ke ya sayi fili a anguwar ya fara gini, ya so ace kusa da gidan Maryam yai ginin amma bai samu fili a wajen ba, duk da haka tunda anguwa É—aya ne ba shi da matsala.
Wannan kenan
***
Assembly ake yi da sassafiyar ranan Litinin. Kowa da ka gani a cikin uniform za ka gan shi tsaf-tsaf da shi.
Kamar kullum a layin na su ita ce ƙarshe saboda ba ta son tsayiwa a gaba ko a tsakiya 'yan ajin na su su dinga tsokalar ta.
"Zaytu Mama kin yi assignment É—in Maths kuwa?" wata yarinya da ke gaban Zaytoonah ta faÉ—a.
Nuratu kenan wacce duk cikin 'yan matan ajin na su ita ce su ke É—an mutunci, itama ayi faÉ—a a shirya ne.
Anguwar su ɗaya ne kuma Islamiyya ɗaya su ke zuwa hakan ya sa su ka ɗan shaƙu.
Sai da ta haɗiyi baƙin cikin da ya taso ma ta sannan ta ce " na yi" ta tsani kalmar Maman nan da su ke alaƙantata da shi. Duk cikin sunannakin da su ke kiranta ba wanda ya fi tsaya ma ta a rai irin Maman aji ko Zaytu Mama da su ke ce ma ta.
"Za ki bani na kwafa dan Allah"
Shiru ta yi ba ta amsa ma ta ba.
Bayan an gama assembly su ka wuce aji. Tana zuwa kuwa Nuratu ta tsareta sai da ta bata notebook É—in ta na Maths.
Nuratu na cikin kwafa sai ga Zaliha ma ta leƙo kai ta fara kwafa. Kan kace me duk waɗanda ba su yi assignment ɗin ba sun yiwa desk ɗin su Zaytoonah rumfa. Zaytoonah na gefe ta cika ta yi fam, ba dama ta yi assignment ita ɗaya musamman ma dai idan Maths ne.
A haka za su kwafi assignment É—in ta amma hakan ba zai hana su dinga tsokanarta ba.
Wasu ba su gama kwafa ba ma Mr Isaac Maths teacher É—in su ya shigo saboda shi su ke da shi darasin farko.
Bayan ya gama darasin ranan ya tattara Assignment É—in ya tafi da shi dan ya yi marking a staff room.
Ko da ya je sai ya ga kusan duk matan class É—in sun cinye Assignment É—in bayan ya san acikin matan Ajin Zaytoonah, Kabirat da Felicia su kaÉ—ai ne su ka iya Maths sosai, su ke kuma fahimtar darussan sa. Bayan ya gama marking É—in ne ya je class ya nemi izinin Malamin English É—in su a kan yana son ganin Tijjani Zaytoonah.
A staff room ta sameshi. Faɗa Mr Isaac ya fara ma ta akan ta ya za ta ba da assignment ɗin ta a kwafa. Ba ta da ta cewa tunda ba iya magana ta ke mu su ba. Daga ƙarshe ya ce duk lokacin da ta yi assignment ya ga irin na ta a wajen wata sai ya ma ta bulala. Bayan ya gama faɗan ne ya ba ta books ɗin ya ce ta je ta raba a class.
Tafiya ta ke yi É—auke da litattafan 'yan ajin su idon ta cike da hawaye.
She wasnt like this before, tana da rigima tanada ƙiriniya amma kuma cikin ƙanƙanin lokaci ta chanja. Ba komai ne ya chanja ta ba face yadda mutane ke ma ta magana akan ƙibanta. There are days da ta ke cewa ba za ta kuma zuwa school ba amma Mommy sai ta korata dole ta je. There are days da ta ke raba dare tana kuka duk dan saboda wata kalma da wani ko wata ya ma ta. A da ba ta ɗaukan abun da zafi amma a hankali-a hankali abun ya fara damunta. Ta kai ko kallonta ka yi sai ta ga kamar kana judging ɗin ƙibanta ne.
Ta sani ƙiba halittanta ne tunda mommyn ta ma na da ƙiba, but kamar yadda Mommy ke yawan faɗa shine ta bari ciye-ciyen ta ya sa ƙiban ya zama unhealthy.
"Shikenan dan inada ƙiba ba zan ci kayan daɗi ba" amsar ta kenan a mafiya yawancin lokutan da Mommyn ta ma ta magana akan ta rage ciye-ciye.
Da karfin hali ta ke zuwa makaranta saboda yadda kowacce rana ke zuwa ma ta da sabbin salo. Suna kam da su na tabo a jikin mutum da duk jikinta ya nuna.
Madam Talatu tsohuwar karuwa ce da ta yi tashe a zamaninta. 'Yar Kafanchang ne da ke Jihar Kaduna, auren dole za a ma ta ta gudu wai ta shiga duniya. A garin Lagos ta tsinci kan ta bayan doguwar tafiya da ta yi. Bayan ta samu masauki a gidan karuwai ta shiga karuwanci, ba ta da wani kyaun fiska amma akwai ta da kyaun diri, irin wanda ke ɗauke hankalin duk wanda yai tozali da ita. Cikin loƙaci kaɗan ta zama ɗaya daga cikin manya-manyan karuwai da ake ji da su a Lagos, wanda Turawa ke ɗauka, 'yan siyasa da manya manyan sojoji ke rububi. Daga gidan karuwai ta ɓalle ta samu gidan kanta ta zauna wanda cikin kuɗaɗen da ta tara ne ta siya da shi. Ta yi karuwanci na shekaru talatin kafin ta yi retire ta bazama kasuwanci, dama tana ɗan taɓa kasuwancin amma yanzu da ta dena karuwanci sai ta riƙe kasuwanci zallah.
To abu ne da ta jima tana tatsan kuɗi daga mazan da ba sa iya kama abun su, dan haka ba ƙaramin maƙudan kuɗi gareta ba. Tana da manya-manyan shaguna da kuma hannun jari.
Bayan ta bar karuwanci ta kan dai nemi yara ƙanana wanda za su biya ma ta buƙata lokaci zuwa lokaci ita kuma ta ba su kuɗi.
Lokacin da ta haÉ—u da Muntari tana shekaru Arba'in da takwas a duniya. Ta gan shi ne lokacin da su ka zo sauke ma ta kaya a É—aya daga cikin shagunan ta. Nan da nan É—an farin Bafulatanin ya burgeta. Bayan ta nemi ganin shi ta ce ya zo washegari za ta bashi aiki. Ganin kuÉ—in da za a dinga bashi a wata ya ninka wanda ya ke samu a da ya sa shi amincewa da aikin.
Yana aiki da Madam Talatu ita kuma tana daɗa lura da shi, bayan wata biyu ta fito ma sa da maitar ta fili, ya ce baya so. Ta sanar da shi kuɗin da za ta dinga bashi duk wata idan ya amince amma still bai amince ba. Da ta dameshi sai ya ajiye aikin da ya ke yi ya kama gaban sa. Bayan ya tafi ta kasa haƙuri da shi ta neme shi ya dawo tareda ma sa alkawarin aure ta ke so su yi kuma indai ya amince to za ta ba shi ɗaya daga cikin shagunan ta, da yai lissafi sai ya ga arziƙi ne ya zo ma sa cikin sauƙi. Auren shekara goma su ka yi alƙawarin za su yi da shi kafin nan zai saketa ya kama gaban sa.
Bayan sun yi Aure kuwa ta bashi ɗaya daga cikin shagunan ta ya zama shi ke sarrafa shi. Ta sa mishi ido sosai akan ko zai ci amanarta kaman sauran ƙananun samarin da ta ke yi sai taga shi Muntari ba ruwan sa da mata. Daga baya ta tambayeshi dalilin zuwansa Lagos ya ce ma ta ya zo neman kuɗi ne saboda matar da ya ke so.
A mafiya yawancin lokutan da ya ke saduwa da ita yana ambatun ta da Maryam hakan ya sa ta san ba ƙaramin so ya kewa wannan Maryam ɗin ba.
Shi kuwa Muntari saboda a dole ya ke tarayya da Madam Talatu ya sa ya fara shan giya da sigari saboda ya dinga É—auke ma sa hankali a duk lokacin da ya ke tarayya da ita, hakan ya sa ya ke ganin Maryam a tareda shi a lokacin da ya ke tare da Madam Talatu.
Cikin shekaru tara da su ka yi tare yana aika kaya Kano ana sayar ma sa da shi hakan ya sa kasuwancin sa ya haɓaka sosai ga shi ba shi da matsalar komai, cin sa da shan sa da suturan sa duk Madam Talatu ce.
Bayan shekara tara da auren su MadamTalata ta fara jinya ashe cervical cancer ne. Ana magani ana jigilar asibiti amma abin ya mata mugun kamu saboda ba a gane shi ke damunta ba da wuri. Ganin fa kullum jigilar Asibiti ake ya sa Madam Talatu ta fara tunanin iyayenta da 'yan uwanta da ta baro shekaru ma su yawa da su ka wuce. A da ƙasar waje Muntari zai fita da ita ta ce ta fasa ya kaita Kafanchang za ta nemi iyayenta su gafarta ma ta. Da su ka je ta samu mahaifinta yana nan amma mahaifiyarta ta jima da rasuwa. Yayyenta da ƙannenta da ba ta san su ba kafin ta tafi duk sun girma suna da iyali. Anyi koke-koke kafin daga baya aka karɓeta hannu bibbiyu.
Saura wata biyar shekara goman auren su ta cika Madam Talatu ta ce Muntari ya saketa saboda tana son zama da 'yan uwanta zuwa lokacin da za ta mutu.
Cikin kaso ɗari na dukiyarta kusan kashi talatin ta ba wa Muntari wanda shima a lokacin side business ɗin sa ya haɓaka sosai. Sauran dukiyarta kuwa 'yan uwanta ta rabawa sannan aka gina Makaranta da Asibiti a ƙauyen su da ke Kafanchang. Shekara ɗaya bayan rabuwar su da Muntari ta rasu.
Shi kuwa Muntari tunda su ka rabu da Madam Talatu ya fara ƙoƙarin yadda zai dawo da kasuwancin sa Kano saboda ya kasance kusa da masoyiyar sa. A shekaran ne kuma ya tafi Umara dan ya fito a Alhaji ya bawa kowa mamaki.
Tunda kuÉ—i su ka fara zama ma sa ya fara bibiyan labarin É—an uwansa Tijjani da kuma halin da masoyiyar sa ke ciki. Bai sha wahalar samun information da ya ke so ba. Nan ta ke ya sayi fili a anguwar ya fara gini, ya so ace kusa da gidan Maryam yai ginin amma bai samu fili a wajen ba, duk da haka tunda anguwa É—aya ne ba shi da matsala.
Wannan kenan
***
Assembly ake yi da sassafiyar ranan Litinin. Kowa da ka gani a cikin uniform za ka gan shi tsaf-tsaf da shi.
Kamar kullum a layin na su ita ce ƙarshe saboda ba ta son tsayiwa a gaba ko a tsakiya 'yan ajin na su su dinga tsokalar ta.
"Zaytu Mama kin yi assignment É—in Maths kuwa?" wata yarinya da ke gaban Zaytoonah ta faÉ—a.
Nuratu kenan wacce duk cikin 'yan matan ajin na su ita ce su ke É—an mutunci, itama ayi faÉ—a a shirya ne.
Anguwar su ɗaya ne kuma Islamiyya ɗaya su ke zuwa hakan ya sa su ka ɗan shaƙu.
Sai da ta haɗiyi baƙin cikin da ya taso ma ta sannan ta ce " na yi" ta tsani kalmar Maman nan da su ke alaƙantata da shi. Duk cikin sunannakin da su ke kiranta ba wanda ya fi tsaya ma ta a rai irin Maman aji ko Zaytu Mama da su ke ce ma ta.
"Za ki bani na kwafa dan Allah"
Shiru ta yi ba ta amsa ma ta ba.
Bayan an gama assembly su ka wuce aji. Tana zuwa kuwa Nuratu ta tsareta sai da ta bata notebook É—in ta na Maths.
Nuratu na cikin kwafa sai ga Zaliha ma ta leƙo kai ta fara kwafa. Kan kace me duk waɗanda ba su yi assignment ɗin ba sun yiwa desk ɗin su Zaytoonah rumfa. Zaytoonah na gefe ta cika ta yi fam, ba dama ta yi assignment ita ɗaya musamman ma dai idan Maths ne.
A haka za su kwafi assignment É—in ta amma hakan ba zai hana su dinga tsokanarta ba.
Wasu ba su gama kwafa ba ma Mr Isaac Maths teacher É—in su ya shigo saboda shi su ke da shi darasin farko.
Bayan ya gama darasin ranan ya tattara Assignment É—in ya tafi da shi dan ya yi marking a staff room.
Ko da ya je sai ya ga kusan duk matan class É—in sun cinye Assignment É—in bayan ya san acikin matan Ajin Zaytoonah, Kabirat da Felicia su kaÉ—ai ne su ka iya Maths sosai, su ke kuma fahimtar darussan sa. Bayan ya gama marking É—in ne ya je class ya nemi izinin Malamin English É—in su a kan yana son ganin Tijjani Zaytoonah.
A staff room ta sameshi. Faɗa Mr Isaac ya fara ma ta akan ta ya za ta ba da assignment ɗin ta a kwafa. Ba ta da ta cewa tunda ba iya magana ta ke mu su ba. Daga ƙarshe ya ce duk lokacin da ta yi assignment ya ga irin na ta a wajen wata sai ya ma ta bulala. Bayan ya gama faɗan ne ya ba ta books ɗin ya ce ta je ta raba a class.
Tafiya ta ke yi É—auke da litattafan 'yan ajin su idon ta cike da hawaye.
She wasnt like this before, tana da rigima tanada ƙiriniya amma kuma cikin ƙanƙanin lokaci ta chanja. Ba komai ne ya chanja ta ba face yadda mutane ke ma ta magana akan ƙibanta. There are days da ta ke cewa ba za ta kuma zuwa school ba amma Mommy sai ta korata dole ta je. There are days da ta ke raba dare tana kuka duk dan saboda wata kalma da wani ko wata ya ma ta. A da ba ta ɗaukan abun da zafi amma a hankali-a hankali abun ya fara damunta. Ta kai ko kallonta ka yi sai ta ga kamar kana judging ɗin ƙibanta ne.
Ta sani ƙiba halittanta ne tunda mommyn ta ma na da ƙiba, but kamar yadda Mommy ke yawan faɗa shine ta bari ciye-ciyen ta ya sa ƙiban ya zama unhealthy.
"Shikenan dan inada ƙiba ba zan ci kayan daɗi ba" amsar ta kenan a mafiya yawancin lokutan da Mommyn ta ma ta magana akan ta rage ciye-ciye.
Da karfin hali ta ke zuwa makaranta saboda yadda kowacce rana ke zuwa ma ta da sabbin salo. Suna kam da su na tabo a jikin mutum da duk jikinta ya nuna.