Sashe 101
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A chan Ringim kuwa abin bai mu su daɗi ba kowa kuma gani ya ke laifin Maryam ce dan ita ce ba ta yiwa Zaytoonah tarbiyya mai kyau ba shiyasa har ta iya buɗe baki ta ce ba za ta auri Galadima ba, Galadiman Zazzau fa. Har da cewa da Tijjani na nan ai ba ta isa ta take maganar sa ba. Sun manta cewa duk wani ɗawainiyyar Zaytoonah babu hannun su a ciki sai yanzu dan sun ji Ɗan Sarki na neman ta shi ne hankalin su ya tashi kowa yana bugun ƙirji yana faɗin shima Baffan Zaytoonah ne.
Zaytoonah na kwance a ɗaki sai rawan sanyi ta ke yi, tun maganar su da Mommy ta fara zazzaɓi, Mommy ba ta san ma tana yi ba dan ko kulata ba ta sake yi ba. Sau ɗaya ta je asibiti wajen Salman amma ganin yadda Mommy ta ke ta shashshareta ya sa ta dawo gida ta kwanta ta fara kuka daga ƙarshe kuma sai zazzaɓi.
Wayar ta ne ya shiga ringing da ƙarfi, ta sa hannu ta jawo wayar ta sa a kunne ba tareda ta lura da wa ke kiran ba. Ta yi sallama a hankali.
"Gimbiya Hajiya Zainabu ke kan layi"
"Ok" Zaytoonah ta faɗa tana ƙoƙarin tashi zaune dan tunda ta ji ance Gimbiya ta san 'yar uwan Justice ne.
"Na bugo ne na ja miki kunne, kin yi kaÉ—an ki rena mana wayo. Sai da aka gama shirya komai za ki zo ki ce kin fasa saboda baki san darajan Mai Martaba ba.
" ko kaɗan ba na son auren nan saboda ba ki dace da babban gida ba. Amma yanzu da ki ka nuna ke 'yar iska ce to ni zan nuna miki duk iskancin ki ba ki isa ki walaƙanta babban gida ba. Aure ne kamar anyi an gama ki sawa ran ki wannan"
Daga haka aka katse kiran.
Jiya Hajia Abu ta dawo daga Dubai inda ta je ta haɗowa Galadima kayan aure sai kawai ta ke jin wai an fasa auren dan yarinyar ta ce ba ta so. Da farko ta share maganan tunda dama ba son Zaytoonah ta ke ba har ta ke cewa su ne 'ya'yan matsiyata ai kuma Justice zai auri 'ya'yan babban gida wanda su ka dace da shi. Amma daga baya sai girman kan su ka motsa, ta ga ai idan ba ayi auren nan ba kamar cin mutunci aka yiwa gidan su musamman Galadima. A ce mutum mai daraja irin sa wata banza ta ce ba za ta aure shi ba. Yadda yaken nan duk macen da ya nuna ba ta isa ta ƙi shi ba saboda martabar sa.
Zaytoonah ta yi murmushi tana faÉ—in lallai ma matar nan.
Muhsina ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo.
"Hajjaju lafiya ki ke ƙunshe a ɗaki tun da safe?"
Ta sa hannu ta taɓa goshinta ta ji zafi
"Zazzaɓi ki ke ji?"
"Na sha magani"
"Ban yarda ba, yaushe ma kika ci abinci da za ki ce kin sha magani. Ki shirya mu je asibiti a duba ki kawai"
"Da gaske na sha magani"
"Wani magani ki ka sha?"
"Paracetamol"
"Lallai kam, tashi ki shirya mu je Asibiti"
"Muhsina dan Allah ki yi haƙuri ba zan iya zuwa ba"
"Kun yi faÉ—a da Mommy ko?"
"Ban san ya zan yi ba, Mommy fishi ta ke yi dani akan maganar Justice. I dont know what to do, ba zan iya auren Justice ba" ta yi maganar tana kuka.
"Miyasa?" Muhsina ta yi maganar tana kallon ta
Zaytoonah ta yi shiru tana kallon ta cike da rashin fahimta.
"Miyasa ba za ki iya auren sa ba?"
"Haka kawai"
"Ba za ki iya auren sa ba saboda ya miki tsufa?"
Zaytoonah ta girgiza kai
"Saboda yana da 'ya'ya har uku?"
Nan ma ta girgiza kai.
"Saboda ba kya son shi akwai wanda kike so?"
Nan ma ta girgiza kai.
Muhsina ta gyara zamanta sosai kusa da Zaytoonah ta ce " na san yadda maganar auren Justice ya zo miki ba a bi tsarin da ya dace ba amma still ko da ya bi ta hanyar da ya dace ne the same response za ki bashi, kin san saboda me?.
"Saboda ba kya son aure Zaytoonah, ba kya son sake wani auren. Bari ki ji abu biyu za ki yi ki muzgunawa kan ki da 'ya'yan ki. Na farko ki ƙi aure ki ƙare rayuwar ki a haka, ya zamana kin denying 'ya'yan ki samun Uba kenan. Na biyu ki yi aure ki auri mutumin da ba zai riƙe 'ya'yan ki da amana ba.
"See, ko Zuhayr da ke ƙabari ba zai so ace kina zaune haka ke kaɗai ba, he'll want you to be happy, to be with someone that makes you happy. Zaytoonah you need a companion, your children needs a father ba zai yiwu ki cigaba da zama a haka ba. And idan har ba wai ɗaya daga cikin dalilin da na irgo ba ne to ni banga aibu a auren Galadima ba, he's a good man, kuma na tabbata idan kika aure shi 'yan biyu ba za suyi kukan rashin Uba ba"...
"Uncle Salman tush tush tush" Hadid ya faÉ—a yana harba bindigar roba wa Salman É—in da ke kishingiÉ—e yana shan tea.
Mommy na riƙe da Hashir tana saka ma sa takalmi, daga zuwa ya cire su ya watsar bayan ga sanyin tiles.
Sallamar Justice su ka ji wanda har yau bai fasa zuwa duba Salman ba.
"Hadid miƙowa Daddyn ku kujera ya zauna" ta yi maganar ne zuciyar ta ɗaya saboda ɗaya kujeran zaman na gefen Hadid ɗin. Ba ta ankara ba ta ji ya ce "GrandMa wannan ne Daddyn mu?"
Sai lokacin Hashir ya kalli fiskar Justice ya ce "Lah! GrandMa dama idan aka je Aljannah ana samun gemu ne?"
Sai kuma dukkan su biyu su ka zo gaban Justice suna kallon sa. Sun fi minti É—aya suna kallon sa suna nemo kamannin mutumin da ke tsaye da kuma kamannin mutumin da ke jikin hotunan da Mom ta ke nuna mu su.
Salman ne ya katse shirun da cewa " Daddyn ku yana Aljannah, wannan Daddy Babba ne"
Hadid ya riƙo hannun Justice yana faɗin "i like you Daddy Babba"
Hashir kuma ya ce "ina kai ba ka bulala kaman É—aya Daddy Babban na Zaria?"
Justice ya shafa kumatunsa yana faÉ—in " ba na bulala amma ba na shiri da wanda ba sa jin magana".
Da kan sa ya jawo kujeran ya zauna ya É—aura su kan cinyarsa yana sauraron surutun su. Duk da bai san yaran waye ba ne amma yaran sun burgeshi, wani zuciya na bashi cewa yaran Zaytoonah ne amma bai tabbatar ba tunda da Mommy da Salman babu wanda ya ma sa bayani.
Cikin ƙanƙanin lokaci wani bond mai ƙarfi ya shiga tsakanin sa da yaran. Dama yaran akwai saurin sabo musamman idan za ka biyewa surutun su. Saboda yaran ya jima a wajen dan ya fi minti talatin bai yi niyyar tafiya ba ma sai da Mommy ta ce su Hadid su bar shi hakanan zai tafi gobe idan ya zo sai su ƙarisa bashi labarin.
Duk yadda ta ke jin rashin ƙarfin jiki tunda Muhsina ta ce ma ta 'ya'yan ta sun zo suna Asibiti ta ji ta warke kawai, ta tashi ta shirya ta fito za ta je Asibitin, Muhsina ta ce ta jira su tafi tare dan itama ta kwana biyu ba ta leƙa Salman ɗin ba.
A motar Muhsina su ka tafi bayan Azma ta miƙo mu su abincin da za su kai.
Suna fitowa daga mota ta hango Justice riƙe da hannun 'yan biyu sun nufi wajen motar sa tareda Junior. Suna tafiya suna hira.
"Hadid, Hashir" ta ƙwala mu su kira dan a tunanin ta bin Justice za su yi.
Dukkan su suka juyo suna kallon ta. Sake hannun Justice su ka yi su ka nufi wajen Zaytoonah da gudu.
Yaran ta ne abinda zuciyar sa ta ambata kenan.
"Mom zo ku gaisa da Daddy Babba, yana da kirki"
Yadda su ke jan hannun ta ya sa dole ta ƙarisa wajen Justice ɗin. Kallon ta ya ke with full admiration.
"Daddy ga Mom É—in mu nan" Hashir ya faÉ—a yana nuna Zaytoonah.
"Ina wuni Sir" ta faÉ—a cike da kunyar sa, sau É—aya ta kalle shi ta kauda kai gefe tana kallon Junior da ke wasa da wayan da ta ke tunanin na Justice É—in ne.
"Daddy ina dai ba ka manta ba gobe za ka kaimu shan ice cream?"
Zaytoonah ta zarewa Hadid ido.
"Insha Allah za mu je" ya faÉ—a yana murmushi.
Tana tsaye a wajen yai wa yaran na ta musabaha tareda kissing goshin su sannan ya karɓi wayar sa a wajen Junior ya shige mota.
Tunda su ka shigo kuwa 'yan biyu kaman haÉ—in baki sai su ka kama taÉ—in Justice, Daddy Babban ma sun dena kira sai dai Daddy kawai.
Kallo É—aya Mommy ta ma ta ta kau da kai, irin kallon 'gashi dai kin gani da idon ki'.
Ba su bar Asibitin ba sai bayan sallar Isha.
Yaran na bacci ta zuba mu su ido tana kallon su, har su ka yi bacci ba su dena taÉ—in Justice ba 'Daddy yayi kaza, Daddy ya ce kaza, gemun Daddy kaman na kaza, maganan Daddy kaza...'
Ko ba dan ita ba, za ta nemawa yaranta farinciki. Idan har aurenta da Justice yana haÉ—e da farin cikin yaran ta to za ta aure shi.
Wayar ta ta ɗauko ta rubuta saƙo sannan ta tura, tana ganin ya tafi ta kashe wayan ta kwanta tana jin zuciyarta na bugawa da sauri-sauri...
2/11/21, 10:04 PM - ****: 50
Bismillahir Rahmanir Rahim
*Married again*
Zaytoonah na kwance a ɗaki sai rawan sanyi ta ke yi, tun maganar su da Mommy ta fara zazzaɓi, Mommy ba ta san ma tana yi ba dan ko kulata ba ta sake yi ba. Sau ɗaya ta je asibiti wajen Salman amma ganin yadda Mommy ta ke ta shashshareta ya sa ta dawo gida ta kwanta ta fara kuka daga ƙarshe kuma sai zazzaɓi.
Wayar ta ne ya shiga ringing da ƙarfi, ta sa hannu ta jawo wayar ta sa a kunne ba tareda ta lura da wa ke kiran ba. Ta yi sallama a hankali.
"Gimbiya Hajiya Zainabu ke kan layi"
"Ok" Zaytoonah ta faɗa tana ƙoƙarin tashi zaune dan tunda ta ji ance Gimbiya ta san 'yar uwan Justice ne.
"Na bugo ne na ja miki kunne, kin yi kaÉ—an ki rena mana wayo. Sai da aka gama shirya komai za ki zo ki ce kin fasa saboda baki san darajan Mai Martaba ba.
" ko kaɗan ba na son auren nan saboda ba ki dace da babban gida ba. Amma yanzu da ki ka nuna ke 'yar iska ce to ni zan nuna miki duk iskancin ki ba ki isa ki walaƙanta babban gida ba. Aure ne kamar anyi an gama ki sawa ran ki wannan"
Daga haka aka katse kiran.
Jiya Hajia Abu ta dawo daga Dubai inda ta je ta haɗowa Galadima kayan aure sai kawai ta ke jin wai an fasa auren dan yarinyar ta ce ba ta so. Da farko ta share maganan tunda dama ba son Zaytoonah ta ke ba har ta ke cewa su ne 'ya'yan matsiyata ai kuma Justice zai auri 'ya'yan babban gida wanda su ka dace da shi. Amma daga baya sai girman kan su ka motsa, ta ga ai idan ba ayi auren nan ba kamar cin mutunci aka yiwa gidan su musamman Galadima. A ce mutum mai daraja irin sa wata banza ta ce ba za ta aure shi ba. Yadda yaken nan duk macen da ya nuna ba ta isa ta ƙi shi ba saboda martabar sa.
Zaytoonah ta yi murmushi tana faÉ—in lallai ma matar nan.
Muhsina ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo.
"Hajjaju lafiya ki ke ƙunshe a ɗaki tun da safe?"
Ta sa hannu ta taɓa goshinta ta ji zafi
"Zazzaɓi ki ke ji?"
"Na sha magani"
"Ban yarda ba, yaushe ma kika ci abinci da za ki ce kin sha magani. Ki shirya mu je asibiti a duba ki kawai"
"Da gaske na sha magani"
"Wani magani ki ka sha?"
"Paracetamol"
"Lallai kam, tashi ki shirya mu je Asibiti"
"Muhsina dan Allah ki yi haƙuri ba zan iya zuwa ba"
"Kun yi faÉ—a da Mommy ko?"
"Ban san ya zan yi ba, Mommy fishi ta ke yi dani akan maganar Justice. I dont know what to do, ba zan iya auren Justice ba" ta yi maganar tana kuka.
"Miyasa?" Muhsina ta yi maganar tana kallon ta
Zaytoonah ta yi shiru tana kallon ta cike da rashin fahimta.
"Miyasa ba za ki iya auren sa ba?"
"Haka kawai"
"Ba za ki iya auren sa ba saboda ya miki tsufa?"
Zaytoonah ta girgiza kai
"Saboda yana da 'ya'ya har uku?"
Nan ma ta girgiza kai.
"Saboda ba kya son shi akwai wanda kike so?"
Nan ma ta girgiza kai.
Muhsina ta gyara zamanta sosai kusa da Zaytoonah ta ce " na san yadda maganar auren Justice ya zo miki ba a bi tsarin da ya dace ba amma still ko da ya bi ta hanyar da ya dace ne the same response za ki bashi, kin san saboda me?.
"Saboda ba kya son aure Zaytoonah, ba kya son sake wani auren. Bari ki ji abu biyu za ki yi ki muzgunawa kan ki da 'ya'yan ki. Na farko ki ƙi aure ki ƙare rayuwar ki a haka, ya zamana kin denying 'ya'yan ki samun Uba kenan. Na biyu ki yi aure ki auri mutumin da ba zai riƙe 'ya'yan ki da amana ba.
"See, ko Zuhayr da ke ƙabari ba zai so ace kina zaune haka ke kaɗai ba, he'll want you to be happy, to be with someone that makes you happy. Zaytoonah you need a companion, your children needs a father ba zai yiwu ki cigaba da zama a haka ba. And idan har ba wai ɗaya daga cikin dalilin da na irgo ba ne to ni banga aibu a auren Galadima ba, he's a good man, kuma na tabbata idan kika aure shi 'yan biyu ba za suyi kukan rashin Uba ba"...
"Uncle Salman tush tush tush" Hadid ya faÉ—a yana harba bindigar roba wa Salman É—in da ke kishingiÉ—e yana shan tea.
Mommy na riƙe da Hashir tana saka ma sa takalmi, daga zuwa ya cire su ya watsar bayan ga sanyin tiles.
Sallamar Justice su ka ji wanda har yau bai fasa zuwa duba Salman ba.
"Hadid miƙowa Daddyn ku kujera ya zauna" ta yi maganar ne zuciyar ta ɗaya saboda ɗaya kujeran zaman na gefen Hadid ɗin. Ba ta ankara ba ta ji ya ce "GrandMa wannan ne Daddyn mu?"
Sai lokacin Hashir ya kalli fiskar Justice ya ce "Lah! GrandMa dama idan aka je Aljannah ana samun gemu ne?"
Sai kuma dukkan su biyu su ka zo gaban Justice suna kallon sa. Sun fi minti É—aya suna kallon sa suna nemo kamannin mutumin da ke tsaye da kuma kamannin mutumin da ke jikin hotunan da Mom ta ke nuna mu su.
Salman ne ya katse shirun da cewa " Daddyn ku yana Aljannah, wannan Daddy Babba ne"
Hadid ya riƙo hannun Justice yana faɗin "i like you Daddy Babba"
Hashir kuma ya ce "ina kai ba ka bulala kaman É—aya Daddy Babban na Zaria?"
Justice ya shafa kumatunsa yana faÉ—in " ba na bulala amma ba na shiri da wanda ba sa jin magana".
Da kan sa ya jawo kujeran ya zauna ya É—aura su kan cinyarsa yana sauraron surutun su. Duk da bai san yaran waye ba ne amma yaran sun burgeshi, wani zuciya na bashi cewa yaran Zaytoonah ne amma bai tabbatar ba tunda da Mommy da Salman babu wanda ya ma sa bayani.
Cikin ƙanƙanin lokaci wani bond mai ƙarfi ya shiga tsakanin sa da yaran. Dama yaran akwai saurin sabo musamman idan za ka biyewa surutun su. Saboda yaran ya jima a wajen dan ya fi minti talatin bai yi niyyar tafiya ba ma sai da Mommy ta ce su Hadid su bar shi hakanan zai tafi gobe idan ya zo sai su ƙarisa bashi labarin.
Duk yadda ta ke jin rashin ƙarfin jiki tunda Muhsina ta ce ma ta 'ya'yan ta sun zo suna Asibiti ta ji ta warke kawai, ta tashi ta shirya ta fito za ta je Asibitin, Muhsina ta ce ta jira su tafi tare dan itama ta kwana biyu ba ta leƙa Salman ɗin ba.
A motar Muhsina su ka tafi bayan Azma ta miƙo mu su abincin da za su kai.
Suna fitowa daga mota ta hango Justice riƙe da hannun 'yan biyu sun nufi wajen motar sa tareda Junior. Suna tafiya suna hira.
"Hadid, Hashir" ta ƙwala mu su kira dan a tunanin ta bin Justice za su yi.
Dukkan su suka juyo suna kallon ta. Sake hannun Justice su ka yi su ka nufi wajen Zaytoonah da gudu.
Yaran ta ne abinda zuciyar sa ta ambata kenan.
"Mom zo ku gaisa da Daddy Babba, yana da kirki"
Yadda su ke jan hannun ta ya sa dole ta ƙarisa wajen Justice ɗin. Kallon ta ya ke with full admiration.
"Daddy ga Mom É—in mu nan" Hashir ya faÉ—a yana nuna Zaytoonah.
"Ina wuni Sir" ta faÉ—a cike da kunyar sa, sau É—aya ta kalle shi ta kauda kai gefe tana kallon Junior da ke wasa da wayan da ta ke tunanin na Justice É—in ne.
"Daddy ina dai ba ka manta ba gobe za ka kaimu shan ice cream?"
Zaytoonah ta zarewa Hadid ido.
"Insha Allah za mu je" ya faÉ—a yana murmushi.
Tana tsaye a wajen yai wa yaran na ta musabaha tareda kissing goshin su sannan ya karɓi wayar sa a wajen Junior ya shige mota.
Tunda su ka shigo kuwa 'yan biyu kaman haÉ—in baki sai su ka kama taÉ—in Justice, Daddy Babban ma sun dena kira sai dai Daddy kawai.
Kallo É—aya Mommy ta ma ta ta kau da kai, irin kallon 'gashi dai kin gani da idon ki'.
Ba su bar Asibitin ba sai bayan sallar Isha.
Yaran na bacci ta zuba mu su ido tana kallon su, har su ka yi bacci ba su dena taÉ—in Justice ba 'Daddy yayi kaza, Daddy ya ce kaza, gemun Daddy kaman na kaza, maganan Daddy kaza...'
Ko ba dan ita ba, za ta nemawa yaranta farinciki. Idan har aurenta da Justice yana haÉ—e da farin cikin yaran ta to za ta aure shi.
Wayar ta ta ɗauko ta rubuta saƙo sannan ta tura, tana ganin ya tafi ta kashe wayan ta kwanta tana jin zuciyarta na bugawa da sauri-sauri...
2/11/21, 10:04 PM - ****: 50
Bismillahir Rahmanir Rahim
*Married again*