Sashe 46
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba'a jima ba ta farfaɗo amma ba ta da ƙarfin jiki hakan ya sa su ka ma ta allura aka ɗaura ma ta ruwa nan da nan bacci ya ɗauketa.
Ko ta kan Sadiq da ya zo dubawa bai yi ba sai ya tsaya kula da Maryam. Ya tambayi likita miya ke damunta ya ce jininta ne ya hau amma sauran bayani sai an kawo result É—in gwajin da aka je yi ma ta bayan an É—eba jinin ta.
Bayan awa É—aya aka kirashi wajen Likita inda ya bayyana ma sa Maryam na É—auke da juna biyu kuma ta rage damuwa dan zai iya jawowa ta rasa cikin.
Muntari ya hangame baki yana jin bayanin Likita.
"Ciki fa ka ce? Har yanzu ba ta dena haihuwa ba ne? Kai a dai sake dubawa ko an jirkita result É—in, rabonta da samun ciki shekaru shida no shekaru bakwai kenan"
Likita da ya É—auka Muntari mijin Maryam ne ya ce "ai ba ta wuce shekarun haihuwa ba ma su shekaru hamsin ma suna haihuwa balle ita da na ke tunanin ba ta fi arba'in ba"
"Talatin da tara ne ma" ya gyara ma sa, kar ya ƙarawa Maryam ɗin sa tsufa.
"To ka gani, she's still very active ta samu ciki. Tana buƙatar hutu sosai, za mu riƙeta na kwana biyu kafin mu sallameta, kuma idan ta koma gida ma ta rage yawan ayyuka ta kuma cire damuwa a ranta"
Muntari ya gyaɗa kai kafin ya miƙe ya bar office ɗin bayan sun yi musabaha da Likita.
Yana shiga ɗaki ya ƙurawa Maryam ido wani kishi da haushi na turnuƙe shi. A fili ya furta "shege Tijjani sai da yai yadda ya ƙunsa ma ta ciki kafin ya tafi"
Daga baya ne ya kira Hajjo ya je ya duba Sadiq ya kuma gaya ma ta Maryam ma an ba ta gado saboda ta faÉ—i lokacin suna shigowa.
"Miya sameta?" Hajjo ta tambaya tana mamakin abun
"Likita ya ce damuwa ce ta ma ta yawa"
"Ai dole, ta fi kowa damuwa da rashin Hamma amma kuma ta ke daurewa tana nuna ba komai".
Sa'ilin da Maryam ta tashi ta so a barta ta tashi ta tafi saboda ta ɗan ji ƙarfin jikinta amma Likita ya ƙi Muntari ma na gefe yana ba ta baki.
Tana son yiwa Likitan bayanin jinyar Sadiq sai maganar likitan ya katse ta.
"Hajiya kina buƙatan hutu fa, dan rashin samun nutsuwa ka iya sa ki rasa abinda ke cikin ki"
"Ciki?" Ta furta da mamaki
"Yes, inaga Maigidan bai riga ya faÉ—a miki ba kenan?"
Muntari yai saurin cewa "tana tashi na zo na kira ka" nan kuwa sai da ta yi kusan 15mins da tashi kafin ya je ya gayawa Likitan bayan da ta ce mi shi ya je ya ce a cire ma ta Canula da ke hannunta za ta tafi É—akin Sadiq.
Shafa ƙasan cikinta ta yi sai ga hawaye. Ciki a lokacin da ta cire rai da sake haihuwa, ciki a lokacin da ake tsaka da neman T J. Ba za ta yi abinda zai sa ta rasa cikin nan ba, not after 'yan biyun ta da ta rasa.
Washegari Maryam ta sa aka Sallameta bayan ta bawa Likita tabbacin za ta kiyaye dokokin sa saboda lafiyar ta. Muntari dai haushin cikin ya cika shi amma kuma soyayyar Maryam ya shafe haushin.
Sadiq kam sai da yai kwana tara a Asibitin aka sallameshi su ka dawo gida, yawan jinya da ya ke yi ma ya sa makarantar sa ma lilo ta ke yi, ya kasa wani yin nisa a karatun.
Addu'a da sadaƙa kam ba wanda aka fasa yiwa T J dan a gano inda ya ke. Tun suna sa ran za'a ji labarin sa har kuma su ka fara fidda rai amma ga Maryam kam kowacce rana da ta fito da hope ɗin ganin T J ta ke musamman yanzu da ta gano tana ɗauke da cikin sa.
Sai da cikin ma ya kai wata biyar ma yawancin mutane su ka gane tana ɗauke da cikin, ciki kuwa har da Iya. Hanne ce ba lafiya ta je gaisheta shine ta haɗu da Iya ashe Hannen laulayi ta ke yi, duk da damuwar ɓatar T J da Iyan ke ciki samun cikin Hanne ya sa ta kwantar da hankalin ta.
Ba laifi da Maryam ta gaisheta ta amsa, haka ta bita da kallo lokacin da za ta tafi tana ƙara tabbatarwa kanta cewa ciki ne a jikin Maryam ɗin...
***
"Zaytoonah miye wannan?"
Ta faÉ—i tana nuna takardan da Zaytoonan ta ba ta.
"Mommy report card ma na" ta amsa tana tura baki
"Sai yaushe za ki maida hankali a karatu ne. Second term 21st a cikin ku 35 yanzu third term kuma 28th. I'm not happy, from 3rd position a first term sai ki koma ƙarshe-ƙarshe"
"Mommy first term Daddy yana nan, yanzu kuma bayanan, ni daga yanzu ma ba zan je school ɗin ba" ta ƙarisa maganar tana tashi za ta bar ɗakin.
"Come back here Zaytoonah. Kar ki sake tashi a gabana ba tareda mun gama maganan ba"
Ta zo ta zauna tana zumɓura baki. Maryam na fara ma ta maganan maida hankali a karatu ta fashe da kuka.
"Mommy ba zan yi karatun ba, ba zan yi ba. Just leave me alone"
"Zan mugun saɓa miki kuwa, ke kaɗai ce kika rasa Uba? Su Salman, Sadiq da Humairah su mutu kenan saboda kin fi su son Daddyn ku?. Haba Zaytoonah sai kin kasheni hankalin ki zai kwanta? Ke ce Babba amma kin fi kowa wauta. Da wanne zan ji Dan Allah"
"Mommy dan Allah ki yi haƙuri" Auwal da shigowar sa ɗakin kenan ya faɗa.
"Ita za ka bawa haƙuri kar ta kashe ni. Na gaji da matsalarta a gidan nan"
Zaytoonah ta fice daga É—akin da gudu.
Ya sani ba halin Mommy ba ne ƙorafi amma duba da abubuwan da su ka faru da kuma cikinta da ya girma gaba ɗaya ta chanja. Abu kaɗan yanzu faɗa ta ke yi. Akwai ranan da tana yiwa Zaytoonah magana sai da ta haɗa da mari, ba dan ya shiga tsakani ba ma da ba ƙaramin duka za ta yiwa Zaytoonan ba. Ya sani Mommy na fama da depression ne.
ÆŠakin Zaytoonah ya wuce ya samu ta kifa kai akan gado sai kuka ta ke yi.
Bai ce ma ta komai ba sai ya zauna bakin gado yana sake duba report card ɗin Zaytoonan. Kusan minti biyar da shigowar sa bai ce komai ba hakan ya sa Zaytoonah ta tsaida kukan ta ɗago tana kallon sa, suna haɗa ido ta harareshi ta cigaba da sheshsheƙar kuka.
"Ki cigaba da harara ta, idan idonki ya faÉ—o na Kare za a sa miki"
Ta murguÉ—a ma sa baki ta ce "ina ruwan ka"
"Da ruwa na mana tunda ni za a nuna a gari ace ga Yayan Zaytoonah dog eyes"
Ta É—au pillow ta buga ma sa a ka.
"Ashe dai ba Mommy kawai za ki kashe ba har da ni" ya faÉ—a yana dariya
Zaytoonah ta ja tsaki.
Kusan 5 seconds kafin ya kira sunan ta a hankali "Zaytoonah"
Ba ta amsa ba amma ta zuba ma sa idanun ta.
"Abinda ki ke yi ba shi zai sa a ga Daddy ba. Infact abinda ki ke yi zai sawa Mommy ɓacin rai ne ƙarshe watarana ta samu heart attack ta mutu"
Zaytoonah ta zaro ido
"Ki na so Mommy ta mutu ne?"
Ta yi saurin girgiza kai
"To ki dena sa ma ta ɓacin rai. Na sha gaya miki addu'a za ki dinga yiwa Daddy ba wai kuka ko taurin kai ba. Ki na so Daddy ya dawo ya samu ba kya karatu ran sa ya ɓaci da ke?"
Nan ma ta girgiza ma sa kai.
"To ki dage da karatu, ban da rashin kunya da taurin kai kin ji"
Jikinta ne ya sanyi ta sunkuyar da kai tana zubda ƙwalla. She's trying to accept the fact that Daddy ya ɓata, ɓata kamar yadda ake neman abu a rasa ko kuma kana kiwon dabba sai ka nemeshi ka rasa. Over this few months ba abin da ba ta riyawa ran ta ba gameda ɓatan Daddyn su. Ta yi tunanin ko 'yan yankan kai ne su ka ɗauke shi ko kuma dai accident yai gawarsa ta ƙone aka rasa waye aka bisine shi. Akwai lokutan da ta ke tunanin ko dai ya gaji da su ne ya gudu dan ya gina sabuwar rayuwa ba tareda su ba, sai kuma ta tuna da cewa Daddyn su na son su sosai, ba zai taɓa guduwa ya bar su.
"Come here" Auwal ya faÉ—a yana jawota jikinsa, ya dinga bubbuga bayanta yana cigaba da rarrashinta...
Da yamma lis Zaytoonah ta shiga kitchen.
"Mommy whats cooking?"
"Your eyes" Mommy ta amsa a hasale
Ta je ta rungume Mommyn ta baya tana faÉ—in "Mommy i'm sorry"
"Sorry for yourself"
"Ah Ah Mommy na tuba fa, no more bad result daga yanzu"
"Har da kukan banza?"
"Yes Mommy, babu kukan banza"
"Sakeni na yi aiki to"
Maimakon ta saketa sai ta ƙara ƙanƙameta tana faɗin "i love you Mommy"
"Na ji sakeni"
"Ai ba ki amsa ba"
Maryam ta yi murmushi ta ce "I love you too"
Sai a sannan Zaytoonah ta saketa, ta kama ma ta aiki har su ka haÉ—a girkin.
***
Ƙarfe biyun dare Auwal ya kira Maryam akan ta zo gidan Hajjo Sadiq ba lafiya. Maryam ta zura dogon hijabi na sallah ta ɗau key ta fita. Addu'a ta ke yi a ranta saboda yanayi na sanyi da aka shiga lokacin ne ciwon Sadiq ya fi tashi. Bai fi sati biyu da ya wuce ba aka sallamoshi daga Asibiti. Shekaranjiya da kan sa ya zo gidan ta ya wuni, dan har sai dare da Auwal zai koma gidan Hajjo ya tafi da shi. Ɗan zaman da yayi da ita ba ƙaramin tausayi ya ba ta ba dan da crutches ya ke tafiya saboda ciwon ƙafa, ciwon ya hanashi girma sai ƙaton kai. Makaranta kam kusan watan sa uku ma bai zuwa.
Ko ta kan Sadiq da ya zo dubawa bai yi ba sai ya tsaya kula da Maryam. Ya tambayi likita miya ke damunta ya ce jininta ne ya hau amma sauran bayani sai an kawo result É—in gwajin da aka je yi ma ta bayan an É—eba jinin ta.
Bayan awa É—aya aka kirashi wajen Likita inda ya bayyana ma sa Maryam na É—auke da juna biyu kuma ta rage damuwa dan zai iya jawowa ta rasa cikin.
Muntari ya hangame baki yana jin bayanin Likita.
"Ciki fa ka ce? Har yanzu ba ta dena haihuwa ba ne? Kai a dai sake dubawa ko an jirkita result É—in, rabonta da samun ciki shekaru shida no shekaru bakwai kenan"
Likita da ya É—auka Muntari mijin Maryam ne ya ce "ai ba ta wuce shekarun haihuwa ba ma su shekaru hamsin ma suna haihuwa balle ita da na ke tunanin ba ta fi arba'in ba"
"Talatin da tara ne ma" ya gyara ma sa, kar ya ƙarawa Maryam ɗin sa tsufa.
"To ka gani, she's still very active ta samu ciki. Tana buƙatar hutu sosai, za mu riƙeta na kwana biyu kafin mu sallameta, kuma idan ta koma gida ma ta rage yawan ayyuka ta kuma cire damuwa a ranta"
Muntari ya gyaɗa kai kafin ya miƙe ya bar office ɗin bayan sun yi musabaha da Likita.
Yana shiga ɗaki ya ƙurawa Maryam ido wani kishi da haushi na turnuƙe shi. A fili ya furta "shege Tijjani sai da yai yadda ya ƙunsa ma ta ciki kafin ya tafi"
Daga baya ne ya kira Hajjo ya je ya duba Sadiq ya kuma gaya ma ta Maryam ma an ba ta gado saboda ta faÉ—i lokacin suna shigowa.
"Miya sameta?" Hajjo ta tambaya tana mamakin abun
"Likita ya ce damuwa ce ta ma ta yawa"
"Ai dole, ta fi kowa damuwa da rashin Hamma amma kuma ta ke daurewa tana nuna ba komai".
Sa'ilin da Maryam ta tashi ta so a barta ta tashi ta tafi saboda ta ɗan ji ƙarfin jikinta amma Likita ya ƙi Muntari ma na gefe yana ba ta baki.
Tana son yiwa Likitan bayanin jinyar Sadiq sai maganar likitan ya katse ta.
"Hajiya kina buƙatan hutu fa, dan rashin samun nutsuwa ka iya sa ki rasa abinda ke cikin ki"
"Ciki?" Ta furta da mamaki
"Yes, inaga Maigidan bai riga ya faÉ—a miki ba kenan?"
Muntari yai saurin cewa "tana tashi na zo na kira ka" nan kuwa sai da ta yi kusan 15mins da tashi kafin ya je ya gayawa Likitan bayan da ta ce mi shi ya je ya ce a cire ma ta Canula da ke hannunta za ta tafi É—akin Sadiq.
Shafa ƙasan cikinta ta yi sai ga hawaye. Ciki a lokacin da ta cire rai da sake haihuwa, ciki a lokacin da ake tsaka da neman T J. Ba za ta yi abinda zai sa ta rasa cikin nan ba, not after 'yan biyun ta da ta rasa.
Washegari Maryam ta sa aka Sallameta bayan ta bawa Likita tabbacin za ta kiyaye dokokin sa saboda lafiyar ta. Muntari dai haushin cikin ya cika shi amma kuma soyayyar Maryam ya shafe haushin.
Sadiq kam sai da yai kwana tara a Asibitin aka sallameshi su ka dawo gida, yawan jinya da ya ke yi ma ya sa makarantar sa ma lilo ta ke yi, ya kasa wani yin nisa a karatun.
Addu'a da sadaƙa kam ba wanda aka fasa yiwa T J dan a gano inda ya ke. Tun suna sa ran za'a ji labarin sa har kuma su ka fara fidda rai amma ga Maryam kam kowacce rana da ta fito da hope ɗin ganin T J ta ke musamman yanzu da ta gano tana ɗauke da cikin sa.
Sai da cikin ma ya kai wata biyar ma yawancin mutane su ka gane tana ɗauke da cikin, ciki kuwa har da Iya. Hanne ce ba lafiya ta je gaisheta shine ta haɗu da Iya ashe Hannen laulayi ta ke yi, duk da damuwar ɓatar T J da Iyan ke ciki samun cikin Hanne ya sa ta kwantar da hankalin ta.
Ba laifi da Maryam ta gaisheta ta amsa, haka ta bita da kallo lokacin da za ta tafi tana ƙara tabbatarwa kanta cewa ciki ne a jikin Maryam ɗin...
***
"Zaytoonah miye wannan?"
Ta faÉ—i tana nuna takardan da Zaytoonan ta ba ta.
"Mommy report card ma na" ta amsa tana tura baki
"Sai yaushe za ki maida hankali a karatu ne. Second term 21st a cikin ku 35 yanzu third term kuma 28th. I'm not happy, from 3rd position a first term sai ki koma ƙarshe-ƙarshe"
"Mommy first term Daddy yana nan, yanzu kuma bayanan, ni daga yanzu ma ba zan je school ɗin ba" ta ƙarisa maganar tana tashi za ta bar ɗakin.
"Come back here Zaytoonah. Kar ki sake tashi a gabana ba tareda mun gama maganan ba"
Ta zo ta zauna tana zumɓura baki. Maryam na fara ma ta maganan maida hankali a karatu ta fashe da kuka.
"Mommy ba zan yi karatun ba, ba zan yi ba. Just leave me alone"
"Zan mugun saɓa miki kuwa, ke kaɗai ce kika rasa Uba? Su Salman, Sadiq da Humairah su mutu kenan saboda kin fi su son Daddyn ku?. Haba Zaytoonah sai kin kasheni hankalin ki zai kwanta? Ke ce Babba amma kin fi kowa wauta. Da wanne zan ji Dan Allah"
"Mommy dan Allah ki yi haƙuri" Auwal da shigowar sa ɗakin kenan ya faɗa.
"Ita za ka bawa haƙuri kar ta kashe ni. Na gaji da matsalarta a gidan nan"
Zaytoonah ta fice daga É—akin da gudu.
Ya sani ba halin Mommy ba ne ƙorafi amma duba da abubuwan da su ka faru da kuma cikinta da ya girma gaba ɗaya ta chanja. Abu kaɗan yanzu faɗa ta ke yi. Akwai ranan da tana yiwa Zaytoonah magana sai da ta haɗa da mari, ba dan ya shiga tsakani ba ma da ba ƙaramin duka za ta yiwa Zaytoonan ba. Ya sani Mommy na fama da depression ne.
ÆŠakin Zaytoonah ya wuce ya samu ta kifa kai akan gado sai kuka ta ke yi.
Bai ce ma ta komai ba sai ya zauna bakin gado yana sake duba report card ɗin Zaytoonan. Kusan minti biyar da shigowar sa bai ce komai ba hakan ya sa Zaytoonah ta tsaida kukan ta ɗago tana kallon sa, suna haɗa ido ta harareshi ta cigaba da sheshsheƙar kuka.
"Ki cigaba da harara ta, idan idonki ya faÉ—o na Kare za a sa miki"
Ta murguÉ—a ma sa baki ta ce "ina ruwan ka"
"Da ruwa na mana tunda ni za a nuna a gari ace ga Yayan Zaytoonah dog eyes"
Ta É—au pillow ta buga ma sa a ka.
"Ashe dai ba Mommy kawai za ki kashe ba har da ni" ya faÉ—a yana dariya
Zaytoonah ta ja tsaki.
Kusan 5 seconds kafin ya kira sunan ta a hankali "Zaytoonah"
Ba ta amsa ba amma ta zuba ma sa idanun ta.
"Abinda ki ke yi ba shi zai sa a ga Daddy ba. Infact abinda ki ke yi zai sawa Mommy ɓacin rai ne ƙarshe watarana ta samu heart attack ta mutu"
Zaytoonah ta zaro ido
"Ki na so Mommy ta mutu ne?"
Ta yi saurin girgiza kai
"To ki dena sa ma ta ɓacin rai. Na sha gaya miki addu'a za ki dinga yiwa Daddy ba wai kuka ko taurin kai ba. Ki na so Daddy ya dawo ya samu ba kya karatu ran sa ya ɓaci da ke?"
Nan ma ta girgiza ma sa kai.
"To ki dage da karatu, ban da rashin kunya da taurin kai kin ji"
Jikinta ne ya sanyi ta sunkuyar da kai tana zubda ƙwalla. She's trying to accept the fact that Daddy ya ɓata, ɓata kamar yadda ake neman abu a rasa ko kuma kana kiwon dabba sai ka nemeshi ka rasa. Over this few months ba abin da ba ta riyawa ran ta ba gameda ɓatan Daddyn su. Ta yi tunanin ko 'yan yankan kai ne su ka ɗauke shi ko kuma dai accident yai gawarsa ta ƙone aka rasa waye aka bisine shi. Akwai lokutan da ta ke tunanin ko dai ya gaji da su ne ya gudu dan ya gina sabuwar rayuwa ba tareda su ba, sai kuma ta tuna da cewa Daddyn su na son su sosai, ba zai taɓa guduwa ya bar su.
"Come here" Auwal ya faÉ—a yana jawota jikinsa, ya dinga bubbuga bayanta yana cigaba da rarrashinta...
Da yamma lis Zaytoonah ta shiga kitchen.
"Mommy whats cooking?"
"Your eyes" Mommy ta amsa a hasale
Ta je ta rungume Mommyn ta baya tana faÉ—in "Mommy i'm sorry"
"Sorry for yourself"
"Ah Ah Mommy na tuba fa, no more bad result daga yanzu"
"Har da kukan banza?"
"Yes Mommy, babu kukan banza"
"Sakeni na yi aiki to"
Maimakon ta saketa sai ta ƙara ƙanƙameta tana faɗin "i love you Mommy"
"Na ji sakeni"
"Ai ba ki amsa ba"
Maryam ta yi murmushi ta ce "I love you too"
Sai a sannan Zaytoonah ta saketa, ta kama ma ta aiki har su ka haÉ—a girkin.
***
Ƙarfe biyun dare Auwal ya kira Maryam akan ta zo gidan Hajjo Sadiq ba lafiya. Maryam ta zura dogon hijabi na sallah ta ɗau key ta fita. Addu'a ta ke yi a ranta saboda yanayi na sanyi da aka shiga lokacin ne ciwon Sadiq ya fi tashi. Bai fi sati biyu da ya wuce ba aka sallamoshi daga Asibiti. Shekaranjiya da kan sa ya zo gidan ta ya wuni, dan har sai dare da Auwal zai koma gidan Hajjo ya tafi da shi. Ɗan zaman da yayi da ita ba ƙaramin tausayi ya ba ta ba dan da crutches ya ke tafiya saboda ciwon ƙafa, ciwon ya hanashi girma sai ƙaton kai. Makaranta kam kusan watan sa uku ma bai zuwa.