Sashe 108
Zaytoonah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwana biyu kenan Zaytoonah ba ta sake yiwa Justice girki ba, duk abinda za ta yi dai dai cikinta ta ke yi ba ta ma zama a wajen dining É—in.
Rashin ganin ta da bai yi ba kwana biyu ya dame shi hakan ya sa ya nufi É—akin ta yau da Asuba tun ma kafin ya wuce masallaci.
Raka'atanil fajri ya samu tana yi lokacin da ya shigo wanda hakan ya burge shi.
Da ta idar sai da ta yi addu'o'in ta kafin ta juyo ta kalle shi, yana zaune bakin gado jikinsa sanye da farar jallabiya.
"Barka da Asuba" ta faÉ—a bayan ta kauda kan ta gefe.
"Princess na yi laifi ne ki ke gudu na?"
"Ranka shi daÉ—e gudun ka kuma, ai ban isa ba"
"To minene matsalar?"
Ta yi shiru tana kallon zanen masallacin ka'aba da ke jikin darduman ta.
"Ni ne na miki laifi ko kuma 'ya'yan ki?"
Still ba ta bashi amsa ba dan ba ta san mi za ta faÉ—a ba.
Ganin ta yi shiru ya sa shi cewa "ba zan takura mi ki ba amma ina so ki sani zan fi jin daÉ—i idan za ki sake jiki da ni. Mu ci abinci tare as a family, a zauna a yi hira ayi raya. Infact ina so Yaran nan su É—auke ki a matsayin uwa ba Anty ba"
"Daga baya kenan" Zaytoonah ta faÉ—a a ran ta.
"Idan kina zaman ɗaki haka ba za su saba da ke ba. Na yadda yaran suna da sakalci saboda hannun da na riƙe su da shi tun bayan rasuwan mahaifiyar su amma duk da haka idan kin ga sun yi ba daidai ba ki kwaɓe su sannan ki ja su a jiki saboda yanzu sun zama na ki. Ina neman alfarma ɗaya a wajen ki"
Ta É—an kalleshi sannan ta sauke idon ta
"Ko da once in a while ne a dinga sammani girki, saboda matar tawa gwana ce wajen sarrafa abinci Masha Allah"
Ko ya aka yi maganar yai tasiri a ranta har ta yi murmushi oho.
Ya miƙe tsaye ya ce " barin wuce masallaci kar na rasa jam'i"
Daga lokacin kuma Zaytoonah ta koma riƙe gidan ta. Tuni ta dakatar da Atika wajen yiwa Justice girki ta ce za ta dinga yi ma sa ita ta dinga yin na sauran ma su aikin gidan.
Kusan kullum sai Raziya ta yi ƙorafi a kan girkin Zaytoonah. Ba ta wani tanka ma ta dan ɓata lokaci kawai za ta yi. Sauran yaran na ci babu complain amma ita kullum bakin ta ba ya shiru, idan ta yi magana Justice ba zai ma ta faɗa ba sai dai kawai ya ce ta je ta karɓi abinci a wajen Atika. Daga baya ma sai ya koma Raziya abincin Atika ta ke ci dan dole, ta so Justice ya dakatar da Zaytoonah ta dena girki amma bai yi hakan ba.
A sati na biyu da zuwan ta gidan ne Maman Tope ta karɓi aiki. Matar tana da sauƙin kai sosai. Professional Chef ce da ta yi aiki a manyan manyan hotels na Abuja, lokacin da mijin ta ya rasu ya barta da yara biyar komai ya zo ya dagule ma ta. Abubuwa su ka ma ta yawa har ta kai ma ta rasa aikin ta. Aikin da ta zo ta samu daga baya albashin bai ma ta ba ga kuma aikin yana cinye ma ta lokaci.
A lokacin da Justice ya dawo Abuja da aiki yana neman mai abinci saboda cook ɗin da aka bashi daga office namiji ne shi kuma baya son namiji saboda yaran sa, shine Hajiya Ghazala ta nemo ma sa Maman Tope. Da farko ita ta nemo ma sa Atika amma ya complain ɗin gaskiya bai gane da aikin ta ba, ya so ma ya sallameta ne sai Hajia Ghazalan ta ce ma sa ai Atikan na buƙatan aikin saboda kula da 'ya'yan ta. Da tana aiki ne a gidan wani Alhaji to sai ya zo ya rasu aka sallami ma su aikin gidan gaba ɗaya. Jin wannan bayani ya sa ya haƙura ya barta.
Zuwan Maman Tope gidan ne ta koyawa Atika wasu girke- girken zamani da na gargajiya musamman abincin mutanen Kudu. Da ke ita ta koyi girki ne professionally har da certificate kuma aikin abincin hotel da ta yi na kusan shekaru shabakwai ya sa tanada experience É—in girki sosai.
Maman Tope a Gwagwalada ta ke zaune da yaran ta. Idan ta zo ta yi 15 days a gidan Justice sai ta koma chan ta huta na 15days inda ta ke ɗan taɓa ƙananun sana'a dan tana ƙoƙarin buɗe ƙaramin restaurant ɗin ta ne nan da shekara mai zuwa, idan kuɗin sun taru.
Atika kuwa a Mararraba ta ke...
***
"Ahmad idon ka kenan?"
Zaytoonah ta faɗa tana karɓan jakar Justice da ke hannun Ahmad ɗin.
"Anty Zaytoonah ai na zo hidimar biki ba mu haÉ—u ba ne saboda jama'a sun yi yawa"
Hararan sa ta yi tana faÉ—in "Anty kuma?" ta bi bayan Justice da tuni ya haura stairs É—in. Shi kuwa Ahmad sai ya kama dariya.
"Sannu da dawowa" ta faɗa yayinda ta ke ajiye ma sa jakar a saman kujerar da ya ke zama yayi aiki. Ɗakin ba baƙon ta bane dan kullum tana shiga ta gyara ma sa.
"Mun same ku lafiya"
Lafiya ta amsa a taƙaice yayinda ta sunkuyar da kan ta ƙasa ganin yana ɓalle button ɗin shirt ɗin sa.
"Za ku ci abinci yanzu ne ko sai kun yi sallah?"
"Ki tambayi Ahmad ko zai ci yanzu amma ni kam sai na yi sallah"
Ta amsa da toh ta fita daga É—akin.
Komawa wajen Ahmad ta yi ta zauna yana zuba ma ta taɗi yana ba ta labarin wani case mai sarƙaƙiya da Justice ya haɗa shi da shi.
"Anty Zaytoonah wai yaushe za ki dawo office ne?, mun yi kewar ki fa"
"Rufa min asiri Ahmad ko zan yi aiki ba yanzu ba. Ka san tashin hankalin da na shiga a case É—in Chief Udodiri"
"Habawa! Ke da ki ke da Justice a kusa wani tsoro za ki ji"
Dai dai nan su ka ji saukowar Justice ɗin dan haka kowa yai gum da bakin sa. Lokacin da ya sauko ya ce za su wuce masallaci Ahmad ya miƙe yana faɗin sai mun dawo Anty.
Al'adar Justice ne idan ya fita sallar magariba a masallacin ya ke zama yai ta azkar har sai anyi Isha kafin ya dawo gida. Indai ya dawo kafin nan to akwai dalili mai girma.
Bayan sun dawo daga sallar ne aka haɗu a dinning ana cin abinci. Ahmad sai santin girkin ya ke yi. Raziya haushi har wuya, ba abin da ta tsana irin ta buɗe ido ta ga Zaytoonah a gidan su. Ga uwa uba ƙannenta da duk faɗan da ta ke yi mu su akan Zaytoonan sun ƙi sauraranta. Ita dai Falaq ba ta wani shiga harkan Zaytoonah saboda dama haka halittar ta ya ke ba ta cika sake jiki da mutane ba amma Suhailah kam cikin ƙanƙanin lokaci ta sake da Zaytoonah, har ɗakin ta tana shiga ta ce za ta yi kallo ko kuma ta ce Zaytoonan ta ma ta wanka.
"Uncle na ce za ka bar Anty ta dawo office ko?" Ahmad ya faÉ—i maganar hankali kwance.
"Insha Allah" ya faÉ—a tareda cigaba da cin abinci.
Zaytoonah ta kalli Ahmad tana jijjiga kai alamar za ka gamu da ni.
Ahmad bai bar gidan na su ba sai kusan ƙarfe goma saura. Da ake akwai surutu kafin ka ce me lokaci ya ja, sai da Justice ya ce zai je ya kwanta ne ma ya iya yin shiru yana faɗin shima bari ya wuce gida kar dare yai sosai...
Washegari kuma Muhsina ta kira ta akan za ta kawo ma ta ziyara. Zaytoonah ta ji daɗin hakan dan tun a gidan rasuwa rabon ta da Muhsinar. Ƙarfe shabiyu saura na rana su ka iso gidan ita da Azma. Tuni dama Zaytoonah ta mu su girki. Sai da aka ɗan taɓa hira kafin ta kawo mu su abinci, su ka haɗu dukkan su a tsakiyar falo suna ci. Muhsinar ce ta ce ta kawo mu su abincin nan dan yanzu ba ta iya cin abinci a dinning. Zaytoonah ta fara tsokanar ta akan ko dai ciki gareta.
"Za ki sani ai. Kema na ki na nan tafe ƙila naki abinci sai idan Galadima ya ba ki a baki za ki iya ci"
Zaytoonah ta kai ma ta dundu yayinda Azma ke ta dariyan su.
"Yo ƙarya na yi ne? Waya sani ko yanzu ma junior yarima na jina"
"Za ki yi ki bari ai, kin gannin nan ni kaɗai na ke wasu fa?. Ashe dai zuwan Abban su Habib saƙo mai mahimmanci ya zo turawa" Zaytoonah ta yi maganar tana dariya ita da Azma ita kuma Muhsinar na faɗin " oho dai tunda saƙon ya je inda ya kamata"...
Haka dai su ka sha hiran su, a ƙalla sun kai awa uku a gidan kafin su ka fara shirin tafiya, da za su tafi Zaytoonah ta mu su jagora zuwa ɗakin ta. Sun yaba ɗakin na ta saboda komai na zamani ne aka saka a wajen.
"Ya 'yan matan na ki?, fatan ba wata matsala?"
Muhsinah ta faÉ—a lokacin da su ke saukowa.
"Babbar na bani ciwon kai wallahi, ina ga randa ta kai ni maƙura duka zan ma ta"
"Haba Zaytoonah, ai gara ki haɗata da uban ta, idan ki ka fara dukan yaran nan yanzu kowa kallon muguwa zai dinga yi miki. Yaran yanzu ai sai a hankali, na ka ma ya ka ƙare da su balle na wani"
"Abin na ta ne ya fara isa na Allah"
"Ki bita a hankali sai kiga nan gaba kaÉ—an kun zo kun saba"
"Allah ya sa haka"...
***
Yau Asabat yaran na gida sun dawo daga Islamiyyar safe kenan sun baje a falo suna kallo ko uniform ba su cire ba.
Rashin ganin ta da bai yi ba kwana biyu ya dame shi hakan ya sa ya nufi É—akin ta yau da Asuba tun ma kafin ya wuce masallaci.
Raka'atanil fajri ya samu tana yi lokacin da ya shigo wanda hakan ya burge shi.
Da ta idar sai da ta yi addu'o'in ta kafin ta juyo ta kalle shi, yana zaune bakin gado jikinsa sanye da farar jallabiya.
"Barka da Asuba" ta faÉ—a bayan ta kauda kan ta gefe.
"Princess na yi laifi ne ki ke gudu na?"
"Ranka shi daÉ—e gudun ka kuma, ai ban isa ba"
"To minene matsalar?"
Ta yi shiru tana kallon zanen masallacin ka'aba da ke jikin darduman ta.
"Ni ne na miki laifi ko kuma 'ya'yan ki?"
Still ba ta bashi amsa ba dan ba ta san mi za ta faÉ—a ba.
Ganin ta yi shiru ya sa shi cewa "ba zan takura mi ki ba amma ina so ki sani zan fi jin daÉ—i idan za ki sake jiki da ni. Mu ci abinci tare as a family, a zauna a yi hira ayi raya. Infact ina so Yaran nan su É—auke ki a matsayin uwa ba Anty ba"
"Daga baya kenan" Zaytoonah ta faÉ—a a ran ta.
"Idan kina zaman ɗaki haka ba za su saba da ke ba. Na yadda yaran suna da sakalci saboda hannun da na riƙe su da shi tun bayan rasuwan mahaifiyar su amma duk da haka idan kin ga sun yi ba daidai ba ki kwaɓe su sannan ki ja su a jiki saboda yanzu sun zama na ki. Ina neman alfarma ɗaya a wajen ki"
Ta É—an kalleshi sannan ta sauke idon ta
"Ko da once in a while ne a dinga sammani girki, saboda matar tawa gwana ce wajen sarrafa abinci Masha Allah"
Ko ya aka yi maganar yai tasiri a ranta har ta yi murmushi oho.
Ya miƙe tsaye ya ce " barin wuce masallaci kar na rasa jam'i"
Daga lokacin kuma Zaytoonah ta koma riƙe gidan ta. Tuni ta dakatar da Atika wajen yiwa Justice girki ta ce za ta dinga yi ma sa ita ta dinga yin na sauran ma su aikin gidan.
Kusan kullum sai Raziya ta yi ƙorafi a kan girkin Zaytoonah. Ba ta wani tanka ma ta dan ɓata lokaci kawai za ta yi. Sauran yaran na ci babu complain amma ita kullum bakin ta ba ya shiru, idan ta yi magana Justice ba zai ma ta faɗa ba sai dai kawai ya ce ta je ta karɓi abinci a wajen Atika. Daga baya ma sai ya koma Raziya abincin Atika ta ke ci dan dole, ta so Justice ya dakatar da Zaytoonah ta dena girki amma bai yi hakan ba.
A sati na biyu da zuwan ta gidan ne Maman Tope ta karɓi aiki. Matar tana da sauƙin kai sosai. Professional Chef ce da ta yi aiki a manyan manyan hotels na Abuja, lokacin da mijin ta ya rasu ya barta da yara biyar komai ya zo ya dagule ma ta. Abubuwa su ka ma ta yawa har ta kai ma ta rasa aikin ta. Aikin da ta zo ta samu daga baya albashin bai ma ta ba ga kuma aikin yana cinye ma ta lokaci.
A lokacin da Justice ya dawo Abuja da aiki yana neman mai abinci saboda cook ɗin da aka bashi daga office namiji ne shi kuma baya son namiji saboda yaran sa, shine Hajiya Ghazala ta nemo ma sa Maman Tope. Da farko ita ta nemo ma sa Atika amma ya complain ɗin gaskiya bai gane da aikin ta ba, ya so ma ya sallameta ne sai Hajia Ghazalan ta ce ma sa ai Atikan na buƙatan aikin saboda kula da 'ya'yan ta. Da tana aiki ne a gidan wani Alhaji to sai ya zo ya rasu aka sallami ma su aikin gidan gaba ɗaya. Jin wannan bayani ya sa ya haƙura ya barta.
Zuwan Maman Tope gidan ne ta koyawa Atika wasu girke- girken zamani da na gargajiya musamman abincin mutanen Kudu. Da ke ita ta koyi girki ne professionally har da certificate kuma aikin abincin hotel da ta yi na kusan shekaru shabakwai ya sa tanada experience É—in girki sosai.
Maman Tope a Gwagwalada ta ke zaune da yaran ta. Idan ta zo ta yi 15 days a gidan Justice sai ta koma chan ta huta na 15days inda ta ke ɗan taɓa ƙananun sana'a dan tana ƙoƙarin buɗe ƙaramin restaurant ɗin ta ne nan da shekara mai zuwa, idan kuɗin sun taru.
Atika kuwa a Mararraba ta ke...
***
"Ahmad idon ka kenan?"
Zaytoonah ta faɗa tana karɓan jakar Justice da ke hannun Ahmad ɗin.
"Anty Zaytoonah ai na zo hidimar biki ba mu haÉ—u ba ne saboda jama'a sun yi yawa"
Hararan sa ta yi tana faÉ—in "Anty kuma?" ta bi bayan Justice da tuni ya haura stairs É—in. Shi kuwa Ahmad sai ya kama dariya.
"Sannu da dawowa" ta faɗa yayinda ta ke ajiye ma sa jakar a saman kujerar da ya ke zama yayi aiki. Ɗakin ba baƙon ta bane dan kullum tana shiga ta gyara ma sa.
"Mun same ku lafiya"
Lafiya ta amsa a taƙaice yayinda ta sunkuyar da kan ta ƙasa ganin yana ɓalle button ɗin shirt ɗin sa.
"Za ku ci abinci yanzu ne ko sai kun yi sallah?"
"Ki tambayi Ahmad ko zai ci yanzu amma ni kam sai na yi sallah"
Ta amsa da toh ta fita daga É—akin.
Komawa wajen Ahmad ta yi ta zauna yana zuba ma ta taɗi yana ba ta labarin wani case mai sarƙaƙiya da Justice ya haɗa shi da shi.
"Anty Zaytoonah wai yaushe za ki dawo office ne?, mun yi kewar ki fa"
"Rufa min asiri Ahmad ko zan yi aiki ba yanzu ba. Ka san tashin hankalin da na shiga a case É—in Chief Udodiri"
"Habawa! Ke da ki ke da Justice a kusa wani tsoro za ki ji"
Dai dai nan su ka ji saukowar Justice ɗin dan haka kowa yai gum da bakin sa. Lokacin da ya sauko ya ce za su wuce masallaci Ahmad ya miƙe yana faɗin sai mun dawo Anty.
Al'adar Justice ne idan ya fita sallar magariba a masallacin ya ke zama yai ta azkar har sai anyi Isha kafin ya dawo gida. Indai ya dawo kafin nan to akwai dalili mai girma.
Bayan sun dawo daga sallar ne aka haɗu a dinning ana cin abinci. Ahmad sai santin girkin ya ke yi. Raziya haushi har wuya, ba abin da ta tsana irin ta buɗe ido ta ga Zaytoonah a gidan su. Ga uwa uba ƙannenta da duk faɗan da ta ke yi mu su akan Zaytoonan sun ƙi sauraranta. Ita dai Falaq ba ta wani shiga harkan Zaytoonah saboda dama haka halittar ta ya ke ba ta cika sake jiki da mutane ba amma Suhailah kam cikin ƙanƙanin lokaci ta sake da Zaytoonah, har ɗakin ta tana shiga ta ce za ta yi kallo ko kuma ta ce Zaytoonan ta ma ta wanka.
"Uncle na ce za ka bar Anty ta dawo office ko?" Ahmad ya faÉ—i maganar hankali kwance.
"Insha Allah" ya faÉ—a tareda cigaba da cin abinci.
Zaytoonah ta kalli Ahmad tana jijjiga kai alamar za ka gamu da ni.
Ahmad bai bar gidan na su ba sai kusan ƙarfe goma saura. Da ake akwai surutu kafin ka ce me lokaci ya ja, sai da Justice ya ce zai je ya kwanta ne ma ya iya yin shiru yana faɗin shima bari ya wuce gida kar dare yai sosai...
Washegari kuma Muhsina ta kira ta akan za ta kawo ma ta ziyara. Zaytoonah ta ji daɗin hakan dan tun a gidan rasuwa rabon ta da Muhsinar. Ƙarfe shabiyu saura na rana su ka iso gidan ita da Azma. Tuni dama Zaytoonah ta mu su girki. Sai da aka ɗan taɓa hira kafin ta kawo mu su abinci, su ka haɗu dukkan su a tsakiyar falo suna ci. Muhsinar ce ta ce ta kawo mu su abincin nan dan yanzu ba ta iya cin abinci a dinning. Zaytoonah ta fara tsokanar ta akan ko dai ciki gareta.
"Za ki sani ai. Kema na ki na nan tafe ƙila naki abinci sai idan Galadima ya ba ki a baki za ki iya ci"
Zaytoonah ta kai ma ta dundu yayinda Azma ke ta dariyan su.
"Yo ƙarya na yi ne? Waya sani ko yanzu ma junior yarima na jina"
"Za ki yi ki bari ai, kin gannin nan ni kaɗai na ke wasu fa?. Ashe dai zuwan Abban su Habib saƙo mai mahimmanci ya zo turawa" Zaytoonah ta yi maganar tana dariya ita da Azma ita kuma Muhsinar na faɗin " oho dai tunda saƙon ya je inda ya kamata"...
Haka dai su ka sha hiran su, a ƙalla sun kai awa uku a gidan kafin su ka fara shirin tafiya, da za su tafi Zaytoonah ta mu su jagora zuwa ɗakin ta. Sun yaba ɗakin na ta saboda komai na zamani ne aka saka a wajen.
"Ya 'yan matan na ki?, fatan ba wata matsala?"
Muhsinah ta faÉ—a lokacin da su ke saukowa.
"Babbar na bani ciwon kai wallahi, ina ga randa ta kai ni maƙura duka zan ma ta"
"Haba Zaytoonah, ai gara ki haɗata da uban ta, idan ki ka fara dukan yaran nan yanzu kowa kallon muguwa zai dinga yi miki. Yaran yanzu ai sai a hankali, na ka ma ya ka ƙare da su balle na wani"
"Abin na ta ne ya fara isa na Allah"
"Ki bita a hankali sai kiga nan gaba kaÉ—an kun zo kun saba"
"Allah ya sa haka"...
***
Yau Asabat yaran na gida sun dawo daga Islamiyyar safe kenan sun baje a falo suna kallo ko uniform ba su cire ba.