Sashe 87
Kisan Mummuke Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tausashe ta ɗora da fadin" So nake yi ka yi mata aure, ina so a daura mata aure da shi din idan ya so sai a kaita gidanta, ina so in ga Farhana a ɗakinta, hakan ne kawai zai iya kwantar min da hankali Andadi...., plz ka amshe shi yau, ka zauna da shi, ka bashi damar turo da magabatansa, ka yi bincike a kansa......, ka san me yake yi a lokacin da ba mai ganinsa sai abokansa, ka yi bincike a kan addininsa, ba ruwana da samunsa, in dai ya fito daga gidan mutane masu mutunci ko me yake ci ta je ta ci, ta je ta yi biyayar aure ta yi bautar aure......, Andadi idan Inna tace da Farhana an fito daga yawon bana rintsawa, idan na je barci baya iya daukana, zuciyata sai ta yi ta bugawa , bana so in mutu bata shiga ɗakinta ba, bana so in mutu in bar maka ita a irin wannan halin, sam ba zasu zaunu da MAZNA a haka ba, ba zasu taba zama Inuwa daya da MAZNA ba, Andadi na gaji, na gaji sosai da damuwar FARHANA "
A hankali ya koma saman kujerar ya dora goshin Anna a kirjinsa a hankali habarsa a saman kanta, ya lumshe idannuwansa yana rike da hannunta a tausashe ya furta" In sha Allah zan amshe shi, sai dai kafin ya zo zan je in same shi, domin na san gidan iyayen sa......., ki kwontar da hankalinki in dai wannan ne an gama,"
Ya sauke ajiyar zuciya a sanyaye ya ce" Bana son in ganki a irin wannan halin.........."
Ya sake zuba mata ido a hankali ya ce" Da ace ina da dama, zan raba ki da Inna ne....., sai dai kin kiya, hasali ma kin saka min dokar kiyayar shiga lamarinki da ita............., Ama ina tsoron in gaza.........."
A hankali Anna ta ce" A'a, babu ruwanku da tsakanina da Inna, Inna uwa ce a gare ni, du abinda ta min wanda na sani da wanda ban sani Ba ma, Andadi kullum cikin yafe mata nake yi,kuma ina rokon Allah ta gama da duniya lafiya........., ka san me? Ita da kanta na tabbata irin yadda abin ke mata ciwo a zuciya ne take fadin ire Iren haka, ta haka ta iya fitar da Tata damuwar, ta haka ne kawai take iya amayar da damuwarta a rayuwa........plz Ni dai ka yi yadda ya dace, ka min abin nan yadda ya dace, ta haka hankalina zai fi kwonciya.........., a bata wanda take so din, kuma a kwana kusa"
Idannuwansa ya lumshe, tausayin Anna da Mutalab na ratsa zuciyarsa .......
Shin yaya zai yi kenan? Da farko shi da kansa ya zata kawai Mutalab yana son zaunawa ne dai, Ama a hankali ya gane da gaske yana son auren FARHANA ne....., kuma gashi yayi nauyin baki bai sanarwa Anna abin nan ba har ita ta kawo maganar nan, yanzu yaya zai yi kenan?
A hankali ya sake furta" in sha Allah, idan na yi sallar la'asar zan je da kaina , kuma ba zan je da niyar yin abinda hankali zai tashi ba........., zan sanar masa ya fito ne kawai"
Anna ta sauke ajiyar zuciya a tausashe ta furta" Allah ya maka albarka, yadda kake min biyayya ina yi maka addu'ar Allah ya baka ya'yan da zasu yi maka masu albarka"
Idannuwansa ya lumshe, yana jin addu'ar nan har cikin zuciyarsa......
Kwarai idan ya ji addu'ar nan daga bakin Anna yakan ji wani irin farin ciki na shiga zuciyarsa har ma ya ji a ransa cewar kwarai zai samu shi ma haihuwar nan, kwarai Allah zai bashi, Allah zai basu shi da MAZNA, zasu samu karuwar haihuwar nan a kwana kusa, shi ma zai rike d'ansa a hannunsa har yayi farin ciki da hakan........, shi ma zai yiwa d'ansa tarbiyya har a kai wajen da yaronsa zai masa biyayya, yana ji a ransa cewar wata rana shi ma zai samu wannan farin cikin.........
Murmushi yayi ya amsa da amen kafin Anna ta sake zuba masa ido.....a tausashe sosai ta ce" Andadi, dayar maganar da nake son yi maka kuwa a kan maganar gidan nan ne"
Yanzun ma ido ya zuba mata da kula sosai
Anna ta ce" Andadinine, ina so ka cenza min gida, Ni da Inna da Farhana, ina so mu koma wani gidan ka ji?"
Falon ya daga kai ya bi da kallo, a tausashe ya ce" wata anguwar kike so mu koma Anna ?, kin ga yanzu in ina kike so mu koma sai mu koma tunda an ga Y'ar Mama ko?"
A hankali Anna ta girgiza kai tana dubansa ta ce" anguwar nan ta min Ni ai, sosai nake son anguwar nan, bale da na ga wajen gidan su Nur sai na ji zan fara yin zumunci sosai da yan anguwar nan, idan so samu na yi ka sama min wani wajen a nan wajen din, ......."
Yanzun ma murmushi yayi ya ce" To mu koma cen Plateau mana, sai a rushe nan din ki zabi sabon ginin da kike so a yi Anna ?, Ni ma tunda na zo nake ta tunanin ya dace a sabunta gine ginen nan"
Anna ta rike hannayensa, a tausashe ta ce" Baka fahimci abinda nake nufi ba, kai kuwa Andadi gida dai gida a duniyar nan idan ya wuce wannan ai abin ya wuce ka'ida, haba sai kace wace zan dawama wannan ma dan Inna tace wallahi sai mun shiga ne na yarda muka zo ama da farko har tsoro ya bani fa........, kawai ina so ne kai ku zauna da matarka a nan, Ni kuma da ina da Farhana da Mama da Malan sai mu koma wani wajen"
Yanzu kam fuskarta ya tsare da kallon da ya sa a tausashe ta ce" Ka fahimce Ni kuwa?, takurar ta isa hakanan, ka ji?"
A hankali ya ce" Anna, me yake faruwa ne? Wace irin takura? Wani ke takura ki ne??"
Anna ta girgiza kai, tana dubansa da kula ta ce" Ko daya, ba wanda ke takura min, tun farko ya dace ace na sanar maka bai dace ka haɗa Ni zama da matarka ba, saboda sirikata ce, sam bai dace ace an hada zama sirikai ba, saboda ina iya zamowa takura a gare ta, ba dan ta nuna min ba ko ta min rashin kunya, a'a, ko daya, kawai lokaci yayi da ya dace ace ba gidanmu guda da matarka ba Andadi......, ku yi zamanku a nan, mu sai mu koma wani wajen, ko ku komawar ku plateau mu sia mu zauna a nan, ka ga sai mu ringa ziyartar juna"
Kasa ya kala, kafin ya sake duban Anna
A tausashe sosai ya ce" Anna, wace irin takurata, mu da ba falon mu daya ba, tsakanin nan da cen tafiya ce ba karama ba, .....?, Anna wace irin takura ce da yarinyar da sai ta yi kwana biyu baku haɗu ba ma?, yanzu hakan ai ziyartar taku ne take kawowa ba yar gidan bace saboda ina gani sai ta dau lokaci bata zo nan ba ko.....?, kuma Anna takura ? Anna yaya zaki ce da takura bayan ke , ke ce kike kula da Inna tun muna yara har zuwa yanzu? Ke bata takura ki ba????"
Anna ta zuba masa, sai kuma ta dauke kai ta ce" Ka ga, Ni ba wannan na tambayeka ba, haba yaya za'a yi ace ana jan magana da kai da girmanka? Inna ai Ni mamana ce, ba zata taba takurani ba!"
Yanzu ma wani mamakin ne ya kama shi........, ita Inna mahaifiyarta ce?, to ita MAZNA ba y'arta bace????
Sai dai yayi shiru, hasalima bayan yayi shirun ma sada kai yayi bai dago ba
A tausashe Anna ta ce" ka fahimce Ni, ina da bukatar ka kai matarka wani wajen , inda zata fi sakewa, kuma ba na fada maka haka bane dan ina nufin wani abu , ko ina nufin ta min wani abu, haka na tsara, plz ka kai ta plateau, idan kuwa cen ya mata kadan Ni sai in koma cen, zan iya hakura da nan din sai mu ringa zuwa wajen aiki muna komawa....."
Idannuwansa ya lumshe yana hadiye duk wata damuwar da yake ji a cikin ransa
A hankali ya kalli Anna , a tausashe ya ce" Anna, akoy wani abu da MAZNA ke yi na rashin da'a a gare ki?"
Anna ta yi gaggawar girgiza masa kai ta ce" Ba nace maka ba dan komai na fadi haka ba? Ra'ayi ne fa kawai"
Kai ya gyada a tausashe ya furta" shiKenan, in sha Allah zan duba........., "
Anna ta yi murmushi ta ce" Na gode sosai....., Allah ya maka albarka"
Murmushin yayi shi ma, wanda bai kai zuciyarsa ba ko kadan, sannan suka ci gaba da yin dan shirun har dai ya mike yana fadin" Anna bari in samu Aba da maganar, dan in sanar masa , kafin mu je mu samu shi saurayin nata"
Anna ta gyada kai ta furta" Hakan yayi, ni ma bari in je in dan huta, sai ka shigo"
Daga haka Anna ta nufi elevator, hakan ya sa ya zuba mata ido har ta shige ya rufe kafin ya koma ya zauna a nutse yana dafe gaban goshinsa da ya dau zafi
Abubuwa ne sun zo masa a tare suna neman daga masa hankali
Ya rasa me zai ce da maganar nan........
Maganar da ta zama ta burin zamansu tare a daf da shi ita da Inna?
Inna kan cewa ina so har in mutu ina ganin ka gefen mahaifiyarka ina so ka samawa mahaifiyarka sanyin idanniyar da zata kula da ita kamar yadda ta kula da Ni
Idan Inna ta zauna daga ita sai shi, takan ce ina da burin ganin macen da zata so mahaifiyarka kamar yadda take so na, ta hidimta mata kamar yadda take hidimta min....., idan yace to ba ga MAZNA ba? Sai tace hum, MAZNA ? Ai a kullum bakuwa take a gidan nan, MAZNA? Matar da ka zaba ce kai, Ama ina maka fatan zabin Allah......
Yaman ajiye haka a matsayin abinda Inna ta tsana fa kullum cikin hamaya take da shi......sai dai a yau hankalinsa na neman yi masa wani irin tashin da hankali ba zai dauka ba
A hankali ya koma saman kujerar ya dora goshin Anna a kirjinsa a hankali habarsa a saman kanta, ya lumshe idannuwansa yana rike da hannunta a tausashe ya furta" In sha Allah zan amshe shi, sai dai kafin ya zo zan je in same shi, domin na san gidan iyayen sa......., ki kwontar da hankalinki in dai wannan ne an gama,"
Ya sauke ajiyar zuciya a sanyaye ya ce" Bana son in ganki a irin wannan halin.........."
Ya sake zuba mata ido a hankali ya ce" Da ace ina da dama, zan raba ki da Inna ne....., sai dai kin kiya, hasali ma kin saka min dokar kiyayar shiga lamarinki da ita............., Ama ina tsoron in gaza.........."
A hankali Anna ta ce" A'a, babu ruwanku da tsakanina da Inna, Inna uwa ce a gare ni, du abinda ta min wanda na sani da wanda ban sani Ba ma, Andadi kullum cikin yafe mata nake yi,kuma ina rokon Allah ta gama da duniya lafiya........., ka san me? Ita da kanta na tabbata irin yadda abin ke mata ciwo a zuciya ne take fadin ire Iren haka, ta haka ta iya fitar da Tata damuwar, ta haka ne kawai take iya amayar da damuwarta a rayuwa........plz Ni dai ka yi yadda ya dace, ka min abin nan yadda ya dace, ta haka hankalina zai fi kwonciya.........., a bata wanda take so din, kuma a kwana kusa"
Idannuwansa ya lumshe, tausayin Anna da Mutalab na ratsa zuciyarsa .......
Shin yaya zai yi kenan? Da farko shi da kansa ya zata kawai Mutalab yana son zaunawa ne dai, Ama a hankali ya gane da gaske yana son auren FARHANA ne....., kuma gashi yayi nauyin baki bai sanarwa Anna abin nan ba har ita ta kawo maganar nan, yanzu yaya zai yi kenan?
A hankali ya sake furta" in sha Allah, idan na yi sallar la'asar zan je da kaina , kuma ba zan je da niyar yin abinda hankali zai tashi ba........., zan sanar masa ya fito ne kawai"
Anna ta sauke ajiyar zuciya a tausashe ta furta" Allah ya maka albarka, yadda kake min biyayya ina yi maka addu'ar Allah ya baka ya'yan da zasu yi maka masu albarka"
Idannuwansa ya lumshe, yana jin addu'ar nan har cikin zuciyarsa......
Kwarai idan ya ji addu'ar nan daga bakin Anna yakan ji wani irin farin ciki na shiga zuciyarsa har ma ya ji a ransa cewar kwarai zai samu shi ma haihuwar nan, kwarai Allah zai bashi, Allah zai basu shi da MAZNA, zasu samu karuwar haihuwar nan a kwana kusa, shi ma zai rike d'ansa a hannunsa har yayi farin ciki da hakan........, shi ma zai yiwa d'ansa tarbiyya har a kai wajen da yaronsa zai masa biyayya, yana ji a ransa cewar wata rana shi ma zai samu wannan farin cikin.........
Murmushi yayi ya amsa da amen kafin Anna ta sake zuba masa ido.....a tausashe sosai ta ce" Andadi, dayar maganar da nake son yi maka kuwa a kan maganar gidan nan ne"
Yanzun ma ido ya zuba mata da kula sosai
Anna ta ce" Andadinine, ina so ka cenza min gida, Ni da Inna da Farhana, ina so mu koma wani gidan ka ji?"
Falon ya daga kai ya bi da kallo, a tausashe ya ce" wata anguwar kike so mu koma Anna ?, kin ga yanzu in ina kike so mu koma sai mu koma tunda an ga Y'ar Mama ko?"
A hankali Anna ta girgiza kai tana dubansa ta ce" anguwar nan ta min Ni ai, sosai nake son anguwar nan, bale da na ga wajen gidan su Nur sai na ji zan fara yin zumunci sosai da yan anguwar nan, idan so samu na yi ka sama min wani wajen a nan wajen din, ......."
Yanzun ma murmushi yayi ya ce" To mu koma cen Plateau mana, sai a rushe nan din ki zabi sabon ginin da kike so a yi Anna ?, Ni ma tunda na zo nake ta tunanin ya dace a sabunta gine ginen nan"
Anna ta rike hannayensa, a tausashe ta ce" Baka fahimci abinda nake nufi ba, kai kuwa Andadi gida dai gida a duniyar nan idan ya wuce wannan ai abin ya wuce ka'ida, haba sai kace wace zan dawama wannan ma dan Inna tace wallahi sai mun shiga ne na yarda muka zo ama da farko har tsoro ya bani fa........, kawai ina so ne kai ku zauna da matarka a nan, Ni kuma da ina da Farhana da Mama da Malan sai mu koma wani wajen"
Yanzu kam fuskarta ya tsare da kallon da ya sa a tausashe ta ce" Ka fahimce Ni kuwa?, takurar ta isa hakanan, ka ji?"
A hankali ya ce" Anna, me yake faruwa ne? Wace irin takura? Wani ke takura ki ne??"
Anna ta girgiza kai, tana dubansa da kula ta ce" Ko daya, ba wanda ke takura min, tun farko ya dace ace na sanar maka bai dace ka haɗa Ni zama da matarka ba, saboda sirikata ce, sam bai dace ace an hada zama sirikai ba, saboda ina iya zamowa takura a gare ta, ba dan ta nuna min ba ko ta min rashin kunya, a'a, ko daya, kawai lokaci yayi da ya dace ace ba gidanmu guda da matarka ba Andadi......, ku yi zamanku a nan, mu sai mu koma wani wajen, ko ku komawar ku plateau mu sia mu zauna a nan, ka ga sai mu ringa ziyartar juna"
Kasa ya kala, kafin ya sake duban Anna
A tausashe sosai ya ce" Anna, wace irin takurata, mu da ba falon mu daya ba, tsakanin nan da cen tafiya ce ba karama ba, .....?, Anna wace irin takura ce da yarinyar da sai ta yi kwana biyu baku haɗu ba ma?, yanzu hakan ai ziyartar taku ne take kawowa ba yar gidan bace saboda ina gani sai ta dau lokaci bata zo nan ba ko.....?, kuma Anna takura ? Anna yaya zaki ce da takura bayan ke , ke ce kike kula da Inna tun muna yara har zuwa yanzu? Ke bata takura ki ba????"
Anna ta zuba masa, sai kuma ta dauke kai ta ce" Ka ga, Ni ba wannan na tambayeka ba, haba yaya za'a yi ace ana jan magana da kai da girmanka? Inna ai Ni mamana ce, ba zata taba takurani ba!"
Yanzu ma wani mamakin ne ya kama shi........, ita Inna mahaifiyarta ce?, to ita MAZNA ba y'arta bace????
Sai dai yayi shiru, hasalima bayan yayi shirun ma sada kai yayi bai dago ba
A tausashe Anna ta ce" ka fahimce Ni, ina da bukatar ka kai matarka wani wajen , inda zata fi sakewa, kuma ba na fada maka haka bane dan ina nufin wani abu , ko ina nufin ta min wani abu, haka na tsara, plz ka kai ta plateau, idan kuwa cen ya mata kadan Ni sai in koma cen, zan iya hakura da nan din sai mu ringa zuwa wajen aiki muna komawa....."
Idannuwansa ya lumshe yana hadiye duk wata damuwar da yake ji a cikin ransa
A hankali ya kalli Anna , a tausashe ya ce" Anna, akoy wani abu da MAZNA ke yi na rashin da'a a gare ki?"
Anna ta yi gaggawar girgiza masa kai ta ce" Ba nace maka ba dan komai na fadi haka ba? Ra'ayi ne fa kawai"
Kai ya gyada a tausashe ya furta" shiKenan, in sha Allah zan duba........., "
Anna ta yi murmushi ta ce" Na gode sosai....., Allah ya maka albarka"
Murmushin yayi shi ma, wanda bai kai zuciyarsa ba ko kadan, sannan suka ci gaba da yin dan shirun har dai ya mike yana fadin" Anna bari in samu Aba da maganar, dan in sanar masa , kafin mu je mu samu shi saurayin nata"
Anna ta gyada kai ta furta" Hakan yayi, ni ma bari in je in dan huta, sai ka shigo"
Daga haka Anna ta nufi elevator, hakan ya sa ya zuba mata ido har ta shige ya rufe kafin ya koma ya zauna a nutse yana dafe gaban goshinsa da ya dau zafi
Abubuwa ne sun zo masa a tare suna neman daga masa hankali
Ya rasa me zai ce da maganar nan........
Maganar da ta zama ta burin zamansu tare a daf da shi ita da Inna?
Inna kan cewa ina so har in mutu ina ganin ka gefen mahaifiyarka ina so ka samawa mahaifiyarka sanyin idanniyar da zata kula da ita kamar yadda ta kula da Ni
Idan Inna ta zauna daga ita sai shi, takan ce ina da burin ganin macen da zata so mahaifiyarka kamar yadda take so na, ta hidimta mata kamar yadda take hidimta min....., idan yace to ba ga MAZNA ba? Sai tace hum, MAZNA ? Ai a kullum bakuwa take a gidan nan, MAZNA? Matar da ka zaba ce kai, Ama ina maka fatan zabin Allah......
Yaman ajiye haka a matsayin abinda Inna ta tsana fa kullum cikin hamaya take da shi......sai dai a yau hankalinsa na neman yi masa wani irin tashin da hankali ba zai dauka ba