Sashe 4
Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
Iyabo:.
Ƙafafuna har rawa suke yi wallahi dana ɗora ƙafata a cikin gidan. Da Yaya Halima na soma cin karo ta tawo ita da ƙawayenta, taci kwalliya, da halamun rakiya zata yi musu. Dariyar dole na ƙaƙaro nace.
Yaya Halima rakiya zaki yi ne. Ina wuni? Na furta da hausar bakina irinta yarbawan da suka ƙware a yaren Hausa. Dan babu kalmar da take bani wahalar furtawa sai dai nakan furtatane da irin Hausar bakina. Harara Yaya Halima ta doka mun, ta ƙura ma titsetsen cikina idanu ƙur. Tsaki ta ja mai ƙarfi suka wuce ni ita da ƙawayenta fuu. Jikina ya sake macewa mus, da jan ƙafa na ƙarasa shiga babban gidan nasu mai ƙofofi huɗu, ko wanne shiyya da ƙofarshi, amman gidan gabaki ɗaya a haɗe yake, ƴan uwane dangin juna da yaransu da jikokinsu a cikin gidan. Babban wan mahaifin su Gwadabe shi ya tara kan wannan dangi a waje ɗaya, kasancewar mahaifinsu Allah ya albarkaceshi da yawan yara (kakan su Gwadabe kenan). Su rai Talatin da uku mahaifinsu ya haifa, matanshi biyu rak. Sai wan mahaifinsu Gwadabe yaji bari ya haɗe kan ƙannenshi su zauna waje guda domin ƙarfafar zumunci. Irin abinda Babala tayi kenan akan Yaya Hambali daya haɗe kan ƙannenshi waje guda suke rayuwa gida ɗaya. Su Baban Nazifi da su Sukairaju kowanne cikinsu yana da ɗakinshi da yake sauka in sabgar biki ta kawomu, akwai katifu da labuleye a ɗakin. Gwadabe ne kawai bashi da ɗakin sauka in mun zo. Hakan ya farune sakamakon ni ya aura ƴar ƙabilar Yoruba bai auri ƴar ƙalibarsu ta Hausa fulani ba. Ina shiga shiyyar Babala naci karo da su Yaya Haula, da Sawaiba matar Harisu, dasu Gude sune ƴan gaba gaban murhu anata tuƙa tuwon jama'ar biki. Duk suka kalleni suka watsar, nasu kam ai na daɗe da sabawa. Ko da nayi sallama ɗaiɗaikun mutanene suka amsani, suma baƙine da suka shigo daga wasu ƙauyukan dan taya iyalan wannan gida murnar biki. A sanyaye na gaishesu har zan wuce Yaya Haula tace.
"Ai kamata yayi ki ci ɗamara da mayafinki ki zo ki tuƙa mana tuwonnan yayi sumul kamar Amala, kinsan dai a gidan surukai kike. Cijewa nayi nace mata.
To bari in gaisa da su Babala sai in zo Yaya Haula" Shikenan iyakar abunda nace, Sai kawai Gude ta daka tsalle tace.
"Lallai Iyabo wuyanki ya isa yanka sosai. Gwadabe ya ɗaure miki kugu sosai. Ke har kina da ta cewa a cikin zuriyarnan, ɗorin dosono dake? Ai da gidanku kika je bikinku na kwalo_kwalo dole ki zage kici aiki dama yarbawa ba'a sanku da hutu ba sai wahala" Hawayen da suke shirin zubo mun nayi saurin mayarwa dan hango Babala tana nufomu. Tana ganina ta zabga mun harara mai muni. Babu shiri na zube a ƙasa ko nauyin cikina banji ba.
Barka da fitowa Babala" Tsaki taja.
" In Kinga dama kin tashi daga wannan tsugunnon naku na gado. Kin shigo garin amman baki iya zuwa inda nake kin gaisheni ba, balle matan yayyena da ƙannena su ci albarkacina a matsayina na mahaifiyar Gwadabe. Sai da kika ganni zaki wani zube a ƙar, ai ni na ɗauka ba zaki barshi yazo bikin ba ma." Hawaye take ya tsinke a idanuna ya soma zuba shar_shar_shar, in furta kalma na kasa, in ɗago in bata hakuri na kasa bakina yayi mun nauyi ainun.
"Haula menene yake faruwa nake jiyo hayaniyarku ne?" Babala ta faɗa cikin ɓacin rai. Abinda Yaya Haula take jira dama kenan ai kuwa sai cewa tayi da Babala.
"Ce mata fa nayi tazo ta tuƙe mana tuwonnan yayi laushi irin nasu yarbawa. Shine ta nemi faɗa mun magana Babala, so take ta fake da ciki ta ƙi yin aiki. Lokacin bikin Rahina ma haka ta kwanta jinya ko tsinke taƙi ɗagawa. Ko a can Kano Gwadabe shi ke mata har shara da wanke_wanke, balle kuma wanki da wankan Toye" Baki Babala ta riƙe tana jijjiga kai kawai.
"Ba shakka ashe har yanzu Yarbawa suna da baƙar zuchiyar yin agumu. Abunda na dinga jiye ma Gwadabe kenan yaƙi ganewa sabida tun ana neman aka gusar mishi da hankali. Ai sunan Gwadabe ya daɗe a hannun Baba lawo ( Bokan yarbawa)" Hawaye kawai nake zubarwa rana zafi inuwa ƙuna. Ana cikin wannan ruguntsumin Gwadabe ya shigo yana rungume da Toye ga jakar kayanmu yana ja, Bara'u na riƙe da jakar kayan Toye. A tsaye suke suna gaisawa da dangin Babala, amman hankalin Gwadabe na kaina yanda yaga ina tsiyayar hawaye gani a gurfane. Ba shiri ya iso inda muke.
"Babala lafiya meke faruwa haka? Iyabo ke ba likita ya hanaki tsugunno ba, tashi tsaye" Ya faÉ—a a sanyaye. Babala ta sauke gwauron numfashi ta dubi Gwadabe tace.
"Babu shakka Gwadabe, sannu me mata. Wato likita ya hanata tsugunno a tsaye kake so ta gaisheni kenan ko marar albarka? Yayi kyau ai ku sha kuruminku komai ma ya kusan zuwa ƙarshe da izinin Allah" Tana faɗar haka ta wuce fu tana share hawaye. Bansan me akayi mata har da zai sata zub da hawaye ba. A kullum naga Babala na kuka akanmu tsorone yake sake shigata dan kukanta a wajen Gwadabe babbar musibace wacce ko arziki bazai bari yayi ba. Gabana ya yanke ya faɗi, take na ji jiri na shirin kayar dani. Me take nufi da komai ya kusan zuwa ƙarshe to? Ko so take Gwadabe ya rabu dani kenan ya auri Bahaushiya ƴar uwarshi?. A baya haka Babala ta tursasa Gwadabe sai da yai mun saki ɗaya. Sakin daya sake rura wutar rikici tsakanin dangina da dangin Gwadabe kenan, wannan saki ba ƙaramin ta da zaune tsaye yayi ba. Dan Iya Debisi da Babala sai da suka kusan raba abun faɗe a layi. Har an kwashe mun jerena har ga Allah ko ni a wancan lokacin na haƙura da Gwadabe. Allah ne yayi shan ruwan aurenmu bai ƙareba ina dawowa na samu wannan ciki."
"Tashi daga tsugunnon Iyabo ki shiga ciki ke da Toye ki huta. Zan je in nemo miki abunda zaki iya ci, ko in sa Sakina ta yo miki"
Da ƙyar na miƙe tsaye ƙafafuna sun yi tsami ainun. Haula da sauran matan dake wajen duk sai suka riƙe bakinsu akan furucin da Gwadabe yayi. Shi kuwa kamar ya faɗa ne dan ma ya sake cusa musu baƙin ciki.
A'a Gwadabe kar ka nemo mini wani abuncin. Duk abunda na samu zanci, ai jikin nawa da sauƙi." Hannu nasa na sauke Toye daga kafaɗarshi. Ya miƙo mun jakar hannun Bara'u na rataya. Jakar kayanmu kuma nace ya tafi mana da'ita gidan Bara'u tunda acan yake sauka mafiya yawan lokuta. Ina tafe ina jan ƙafata. Sai kallon banza aketa watsomun, harda masu tsaki, da tofar da miyau. Duk inda naga taron mata sai na gaishesu zan wuce, kuma fa saina rusuna mu a al'adarmu akwai wannan tarbiyyar. Wasu su amsa ciki_ciki, wasu ba sa amsaba a haka har na isa ɗakin Babala. Cike dam ɗakin yake da ƙannenta da yayyenta. Yaya Halima ma ta dawo daga Rakiya tana zaune tana cin tuwon shinkafa miyar kabewa sai ƙamshin man shanu take yi. Laila na zaune a kusa da'ita ta ci ado sosai, sai wani hararata take yi. Ina shiga na zube a ƙasa ɗaya bayan ɗaya na dinga binsu da gaisuwa, har Laila dana girma ban bari ba sai da na gaisheta.
"Sai ki tashi maza ki shiga cikin surukan gidannan ki kama aiki, baki ci ta zama ba" Cewar Baba Iyatu ƙanwar Babala. Miƙewa nayi ina shirin fita na jiyo Yaya Halima na cewa.
"Ki tafi da ɗanki babu wanda zai kular miki dashi" Yaron na kalla yayi tsuru_tsuru kamar ba dangin mahaifinshi ya shigo ba. Duk ƙin Gwadabe da dangina suke yi bai shafi abunda muka haifaba sam, amman banda dangin Gwadabe. Hannun Toye na kama muka fito tare. Da Gwadabe naci karo zai shigo ni kuma zan fita.
"Ina kuma zaki je ke da ba ishasshiyar lafiya gareki ba?" Ban ce mishi komai ba gudun kar in faÉ—i wata kalma da zata zama lefi.
"Aiki zata je ta kama ma su Haula. Ko su zasu girka mata abinda zata ci ne rasa kunya?" Cewar Baba Iyatu. Da sauri na wuce shi ina murmushi wanda yafi kuka ciwo. Shi kuma ina jiyoshi yana musu bayanin hawan jini ne dani, kuma likita ya hanani yawan aiki da zurga_zurga. Ni dai gaba na ƙara dani akaita hada hadar girki har sai da muka gama na zauna a kan turmi ina ba Toye abinci a baki. Sakina ce ta iso inda nake da fara'arta. Nima cikin fara'a na tarbeta. Kwanon hannunta ta ajjiye a gabana.
"Maman biyu ga farfesun kifi Gwadabe yasa nayi miki. Yace shi kaɗai kike iya ci ya zauna" Ɗan murmushi na ƙaƙaro na dubi Yaya Haula bata kallonmu amman kunnuwanta yana wajenmu.
Kai Sakina sai da ya saki wahala? Kinga ga tuwo nan ma ina jira Toye ya ƙoshi ne sai in cinye ragowar, jikin yanzu da sauƙi" Da sauri Yaya Haula ta yi ɓangaren Babala na yi imani wata fitinar zata je ta kunno mun. Ɗakin Goggo Innawo mu ka shiga, ita Goggo Innawo ƙanwar mahaifiyar Sakina ce a gidan take aure. Anan naci kifina muna hirar yaushe gamo.
"Oh Iyabo ashe rabon Æ´an biyu ne ya dawo dake É—akin ki. Irin rikicin da akaita tayi babu wanda ya zaci aurenku zai dawo, sai gashi har da cikin Æ´an biyu" Dariya nayi nace.
Sakina kinsan duk abinda ya samu bawa da sanin Allah. Shan ruwan aurenmu ne bai ƙare ba. Duk rikici in Allah ya riga ya ƙadarto a dakin Gwadabe zan ƙare rayuwata, babu tsumi babu dabara ga duk waɗanda basa son tarayyyarmu. Ni aurena da Gwadabe ya ƙara mun tsoron Allah, anan na sake gane ƙudurar Allah. Irin badaƙalar da ta biyo neman auren ai me girma ce, amman da yake Allah ya yarda da haɗin ba gamu ba". Sakina tace.
"Wannan gaskiya ne. Mu kammu ba mui zaton aurenku zai yiwu ba. Duk da dai Gwadabe yana tsantsar sonki da burin son aurenki. Amman bai samu goyon baya a wajen kowa ba sai Bara'u. Bara'u kuma bashi da ikon zartar da hukunci a kan Gwadabe. Ba da ban Baba Magaji ba da yanzu wani labarin akeyi. Ke dai Iyabo ki ta yin haƙuri wata rana sai labari. Ko wacce mace da irin ƙalubalen da take fuskanta a gidan aurenta, muna barma cikinmu sirrinne kawai. Murmushi kawai nayi ina hango lokacin da Gwadabe yake zuwa taɗi ƙofar gidanmu a idanuna. Tun yana zuwa ana barinshi da dai Iyaa Debisi ta ga abun da gaske ne na riga na kamu da son Gwadabe sai aka hana shi zuwa gida wajena. Ni da Gwadabe sai dai mu haɗu a wajen da nake sana'ar tuyan ƙosai da kafa da daddare a bakin titin unguwarmu. Gwauron numfashi na ja kawai mu ka ci gaba da hirarmu da Sakina. Sai da na huta na yi sallar azahar. Muna yin la'asar kuwa aka aiko yaran gidan wai in zo bakin murhu za'a ɗaura sanwar dare. Faɗan irin wuyar da nasha ɓata lokacine kawai, aikin kusan nice ƙarfin yinshi, sukaita zamewa suna barina. Ga tuwon gidan bikin ƙauye ba tuwo bane na wasa, ni na talga tuwonnan na dinga ɗiba da ƙoƙo ina zubawa a tukunya lamba talatin sai juyawa ruwan zafin yake yi. Bayan na gama talge sai na koma wajen su Zuwaira mu ka ci gaba da wanke kwanukan da aka ɓata da rana. Wanke_wanke ne bana wasa ba. Muna tsaka da wanke_wanken Su Yaya Hambali suka zo wucewa ta wajen. Dukkansu suke tafe harda Gwadabe wanda na ga idandunanshi sun kaɗa sun yi jawur. Duk da magriba ta kawo kai akwai ƙarancin haske. Kallona kawai yayi ya girgiza kai suka wuce zuwa shiyyar Babala. Haka kawai sai na tsinci kaina a cikin damuwa gami da faɗuwan gaba, take sai jikina ya mace murus. Cikin dauriya na iya tsaiwa muka kammala duk aikin daya kamata
Ƙafafuna har rawa suke yi wallahi dana ɗora ƙafata a cikin gidan. Da Yaya Halima na soma cin karo ta tawo ita da ƙawayenta, taci kwalliya, da halamun rakiya zata yi musu. Dariyar dole na ƙaƙaro nace.
Yaya Halima rakiya zaki yi ne. Ina wuni? Na furta da hausar bakina irinta yarbawan da suka ƙware a yaren Hausa. Dan babu kalmar da take bani wahalar furtawa sai dai nakan furtatane da irin Hausar bakina. Harara Yaya Halima ta doka mun, ta ƙura ma titsetsen cikina idanu ƙur. Tsaki ta ja mai ƙarfi suka wuce ni ita da ƙawayenta fuu. Jikina ya sake macewa mus, da jan ƙafa na ƙarasa shiga babban gidan nasu mai ƙofofi huɗu, ko wanne shiyya da ƙofarshi, amman gidan gabaki ɗaya a haɗe yake, ƴan uwane dangin juna da yaransu da jikokinsu a cikin gidan. Babban wan mahaifin su Gwadabe shi ya tara kan wannan dangi a waje ɗaya, kasancewar mahaifinsu Allah ya albarkaceshi da yawan yara (kakan su Gwadabe kenan). Su rai Talatin da uku mahaifinsu ya haifa, matanshi biyu rak. Sai wan mahaifinsu Gwadabe yaji bari ya haɗe kan ƙannenshi su zauna waje guda domin ƙarfafar zumunci. Irin abinda Babala tayi kenan akan Yaya Hambali daya haɗe kan ƙannenshi waje guda suke rayuwa gida ɗaya. Su Baban Nazifi da su Sukairaju kowanne cikinsu yana da ɗakinshi da yake sauka in sabgar biki ta kawomu, akwai katifu da labuleye a ɗakin. Gwadabe ne kawai bashi da ɗakin sauka in mun zo. Hakan ya farune sakamakon ni ya aura ƴar ƙabilar Yoruba bai auri ƴar ƙalibarsu ta Hausa fulani ba. Ina shiga shiyyar Babala naci karo da su Yaya Haula, da Sawaiba matar Harisu, dasu Gude sune ƴan gaba gaban murhu anata tuƙa tuwon jama'ar biki. Duk suka kalleni suka watsar, nasu kam ai na daɗe da sabawa. Ko da nayi sallama ɗaiɗaikun mutanene suka amsani, suma baƙine da suka shigo daga wasu ƙauyukan dan taya iyalan wannan gida murnar biki. A sanyaye na gaishesu har zan wuce Yaya Haula tace.
"Ai kamata yayi ki ci ɗamara da mayafinki ki zo ki tuƙa mana tuwonnan yayi sumul kamar Amala, kinsan dai a gidan surukai kike. Cijewa nayi nace mata.
To bari in gaisa da su Babala sai in zo Yaya Haula" Shikenan iyakar abunda nace, Sai kawai Gude ta daka tsalle tace.
"Lallai Iyabo wuyanki ya isa yanka sosai. Gwadabe ya ɗaure miki kugu sosai. Ke har kina da ta cewa a cikin zuriyarnan, ɗorin dosono dake? Ai da gidanku kika je bikinku na kwalo_kwalo dole ki zage kici aiki dama yarbawa ba'a sanku da hutu ba sai wahala" Hawayen da suke shirin zubo mun nayi saurin mayarwa dan hango Babala tana nufomu. Tana ganina ta zabga mun harara mai muni. Babu shiri na zube a ƙasa ko nauyin cikina banji ba.
Barka da fitowa Babala" Tsaki taja.
" In Kinga dama kin tashi daga wannan tsugunnon naku na gado. Kin shigo garin amman baki iya zuwa inda nake kin gaisheni ba, balle matan yayyena da ƙannena su ci albarkacina a matsayina na mahaifiyar Gwadabe. Sai da kika ganni zaki wani zube a ƙar, ai ni na ɗauka ba zaki barshi yazo bikin ba ma." Hawaye take ya tsinke a idanuna ya soma zuba shar_shar_shar, in furta kalma na kasa, in ɗago in bata hakuri na kasa bakina yayi mun nauyi ainun.
"Haula menene yake faruwa nake jiyo hayaniyarku ne?" Babala ta faɗa cikin ɓacin rai. Abinda Yaya Haula take jira dama kenan ai kuwa sai cewa tayi da Babala.
"Ce mata fa nayi tazo ta tuƙe mana tuwonnan yayi laushi irin nasu yarbawa. Shine ta nemi faɗa mun magana Babala, so take ta fake da ciki ta ƙi yin aiki. Lokacin bikin Rahina ma haka ta kwanta jinya ko tsinke taƙi ɗagawa. Ko a can Kano Gwadabe shi ke mata har shara da wanke_wanke, balle kuma wanki da wankan Toye" Baki Babala ta riƙe tana jijjiga kai kawai.
"Ba shakka ashe har yanzu Yarbawa suna da baƙar zuchiyar yin agumu. Abunda na dinga jiye ma Gwadabe kenan yaƙi ganewa sabida tun ana neman aka gusar mishi da hankali. Ai sunan Gwadabe ya daɗe a hannun Baba lawo ( Bokan yarbawa)" Hawaye kawai nake zubarwa rana zafi inuwa ƙuna. Ana cikin wannan ruguntsumin Gwadabe ya shigo yana rungume da Toye ga jakar kayanmu yana ja, Bara'u na riƙe da jakar kayan Toye. A tsaye suke suna gaisawa da dangin Babala, amman hankalin Gwadabe na kaina yanda yaga ina tsiyayar hawaye gani a gurfane. Ba shiri ya iso inda muke.
"Babala lafiya meke faruwa haka? Iyabo ke ba likita ya hanaki tsugunno ba, tashi tsaye" Ya faÉ—a a sanyaye. Babala ta sauke gwauron numfashi ta dubi Gwadabe tace.
"Babu shakka Gwadabe, sannu me mata. Wato likita ya hanata tsugunno a tsaye kake so ta gaisheni kenan ko marar albarka? Yayi kyau ai ku sha kuruminku komai ma ya kusan zuwa ƙarshe da izinin Allah" Tana faɗar haka ta wuce fu tana share hawaye. Bansan me akayi mata har da zai sata zub da hawaye ba. A kullum naga Babala na kuka akanmu tsorone yake sake shigata dan kukanta a wajen Gwadabe babbar musibace wacce ko arziki bazai bari yayi ba. Gabana ya yanke ya faɗi, take na ji jiri na shirin kayar dani. Me take nufi da komai ya kusan zuwa ƙarshe to? Ko so take Gwadabe ya rabu dani kenan ya auri Bahaushiya ƴar uwarshi?. A baya haka Babala ta tursasa Gwadabe sai da yai mun saki ɗaya. Sakin daya sake rura wutar rikici tsakanin dangina da dangin Gwadabe kenan, wannan saki ba ƙaramin ta da zaune tsaye yayi ba. Dan Iya Debisi da Babala sai da suka kusan raba abun faɗe a layi. Har an kwashe mun jerena har ga Allah ko ni a wancan lokacin na haƙura da Gwadabe. Allah ne yayi shan ruwan aurenmu bai ƙareba ina dawowa na samu wannan ciki."
"Tashi daga tsugunnon Iyabo ki shiga ciki ke da Toye ki huta. Zan je in nemo miki abunda zaki iya ci, ko in sa Sakina ta yo miki"
Da ƙyar na miƙe tsaye ƙafafuna sun yi tsami ainun. Haula da sauran matan dake wajen duk sai suka riƙe bakinsu akan furucin da Gwadabe yayi. Shi kuwa kamar ya faɗa ne dan ma ya sake cusa musu baƙin ciki.
A'a Gwadabe kar ka nemo mini wani abuncin. Duk abunda na samu zanci, ai jikin nawa da sauƙi." Hannu nasa na sauke Toye daga kafaɗarshi. Ya miƙo mun jakar hannun Bara'u na rataya. Jakar kayanmu kuma nace ya tafi mana da'ita gidan Bara'u tunda acan yake sauka mafiya yawan lokuta. Ina tafe ina jan ƙafata. Sai kallon banza aketa watsomun, harda masu tsaki, da tofar da miyau. Duk inda naga taron mata sai na gaishesu zan wuce, kuma fa saina rusuna mu a al'adarmu akwai wannan tarbiyyar. Wasu su amsa ciki_ciki, wasu ba sa amsaba a haka har na isa ɗakin Babala. Cike dam ɗakin yake da ƙannenta da yayyenta. Yaya Halima ma ta dawo daga Rakiya tana zaune tana cin tuwon shinkafa miyar kabewa sai ƙamshin man shanu take yi. Laila na zaune a kusa da'ita ta ci ado sosai, sai wani hararata take yi. Ina shiga na zube a ƙasa ɗaya bayan ɗaya na dinga binsu da gaisuwa, har Laila dana girma ban bari ba sai da na gaisheta.
"Sai ki tashi maza ki shiga cikin surukan gidannan ki kama aiki, baki ci ta zama ba" Cewar Baba Iyatu ƙanwar Babala. Miƙewa nayi ina shirin fita na jiyo Yaya Halima na cewa.
"Ki tafi da ɗanki babu wanda zai kular miki dashi" Yaron na kalla yayi tsuru_tsuru kamar ba dangin mahaifinshi ya shigo ba. Duk ƙin Gwadabe da dangina suke yi bai shafi abunda muka haifaba sam, amman banda dangin Gwadabe. Hannun Toye na kama muka fito tare. Da Gwadabe naci karo zai shigo ni kuma zan fita.
"Ina kuma zaki je ke da ba ishasshiyar lafiya gareki ba?" Ban ce mishi komai ba gudun kar in faÉ—i wata kalma da zata zama lefi.
"Aiki zata je ta kama ma su Haula. Ko su zasu girka mata abinda zata ci ne rasa kunya?" Cewar Baba Iyatu. Da sauri na wuce shi ina murmushi wanda yafi kuka ciwo. Shi kuma ina jiyoshi yana musu bayanin hawan jini ne dani, kuma likita ya hanani yawan aiki da zurga_zurga. Ni dai gaba na ƙara dani akaita hada hadar girki har sai da muka gama na zauna a kan turmi ina ba Toye abinci a baki. Sakina ce ta iso inda nake da fara'arta. Nima cikin fara'a na tarbeta. Kwanon hannunta ta ajjiye a gabana.
"Maman biyu ga farfesun kifi Gwadabe yasa nayi miki. Yace shi kaɗai kike iya ci ya zauna" Ɗan murmushi na ƙaƙaro na dubi Yaya Haula bata kallonmu amman kunnuwanta yana wajenmu.
Kai Sakina sai da ya saki wahala? Kinga ga tuwo nan ma ina jira Toye ya ƙoshi ne sai in cinye ragowar, jikin yanzu da sauƙi" Da sauri Yaya Haula ta yi ɓangaren Babala na yi imani wata fitinar zata je ta kunno mun. Ɗakin Goggo Innawo mu ka shiga, ita Goggo Innawo ƙanwar mahaifiyar Sakina ce a gidan take aure. Anan naci kifina muna hirar yaushe gamo.
"Oh Iyabo ashe rabon Æ´an biyu ne ya dawo dake É—akin ki. Irin rikicin da akaita tayi babu wanda ya zaci aurenku zai dawo, sai gashi har da cikin Æ´an biyu" Dariya nayi nace.
Sakina kinsan duk abinda ya samu bawa da sanin Allah. Shan ruwan aurenmu ne bai ƙare ba. Duk rikici in Allah ya riga ya ƙadarto a dakin Gwadabe zan ƙare rayuwata, babu tsumi babu dabara ga duk waɗanda basa son tarayyyarmu. Ni aurena da Gwadabe ya ƙara mun tsoron Allah, anan na sake gane ƙudurar Allah. Irin badaƙalar da ta biyo neman auren ai me girma ce, amman da yake Allah ya yarda da haɗin ba gamu ba". Sakina tace.
"Wannan gaskiya ne. Mu kammu ba mui zaton aurenku zai yiwu ba. Duk da dai Gwadabe yana tsantsar sonki da burin son aurenki. Amman bai samu goyon baya a wajen kowa ba sai Bara'u. Bara'u kuma bashi da ikon zartar da hukunci a kan Gwadabe. Ba da ban Baba Magaji ba da yanzu wani labarin akeyi. Ke dai Iyabo ki ta yin haƙuri wata rana sai labari. Ko wacce mace da irin ƙalubalen da take fuskanta a gidan aurenta, muna barma cikinmu sirrinne kawai. Murmushi kawai nayi ina hango lokacin da Gwadabe yake zuwa taɗi ƙofar gidanmu a idanuna. Tun yana zuwa ana barinshi da dai Iyaa Debisi ta ga abun da gaske ne na riga na kamu da son Gwadabe sai aka hana shi zuwa gida wajena. Ni da Gwadabe sai dai mu haɗu a wajen da nake sana'ar tuyan ƙosai da kafa da daddare a bakin titin unguwarmu. Gwauron numfashi na ja kawai mu ka ci gaba da hirarmu da Sakina. Sai da na huta na yi sallar azahar. Muna yin la'asar kuwa aka aiko yaran gidan wai in zo bakin murhu za'a ɗaura sanwar dare. Faɗan irin wuyar da nasha ɓata lokacine kawai, aikin kusan nice ƙarfin yinshi, sukaita zamewa suna barina. Ga tuwon gidan bikin ƙauye ba tuwo bane na wasa, ni na talga tuwonnan na dinga ɗiba da ƙoƙo ina zubawa a tukunya lamba talatin sai juyawa ruwan zafin yake yi. Bayan na gama talge sai na koma wajen su Zuwaira mu ka ci gaba da wanke kwanukan da aka ɓata da rana. Wanke_wanke ne bana wasa ba. Muna tsaka da wanke_wanken Su Yaya Hambali suka zo wucewa ta wajen. Dukkansu suke tafe harda Gwadabe wanda na ga idandunanshi sun kaɗa sun yi jawur. Duk da magriba ta kawo kai akwai ƙarancin haske. Kallona kawai yayi ya girgiza kai suka wuce zuwa shiyyar Babala. Haka kawai sai na tsinci kaina a cikin damuwa gami da faɗuwan gaba, take sai jikina ya mace murus. Cikin dauriya na iya tsaiwa muka kammala duk aikin daya kamata