Sashe 1
Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
NAMA YA DAHU....
ROMO ÆŠANYE"
GAWURTATTU UKU
DAGA ALƘALAMIN BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI
MARUBUCIYAR LITTAFIN NA FAÆŠO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA (LABARIN SHANONO DA OGA KAILA.
NA SAKE DAWOWA DA WANI LABARIN MAI ƊAUKE DA DARASI, DA BAN TAUSAYI, SADAUKARWA, TSAGWARON ZUNZURUTUN SOYAYYA DA ƘAUNA, FARIN CIKI, BAƘIN CIKI DUK A CIKIN WANNAN LITTAFI MAI SUNA A SAMA. KU BIYONI KU SHA KARATU.
ALƘALAMINA BAYA RUBUTA ABINDA BAZAI AMFANAR DA AL'UMMAR ANNABI BA.
KAMAR YADDA NA SABA WANNAN LABARIN SHIMA YA FARU A GASKEN GASKE, KU BIYO NI DA HANKICI DOMIN SHARE HAWAYEN DA ZASU ZOBO A GURABEN IDANUWANKU. KU GYARA ZAMA DA KYAU KU BI LABARIN SANNU_SANNU ZAKU FAHIMCI INDA YASA GABA.
Lamba ta 1
JIHAR KANO:
Kano na ɗaya daga cikin manyan birane a ƙasar Hausa. Kano itace cibiyar kasuwanci ta Najeriya gaba ɗaya. Jihar ta Kano tana da ƙananan hukumomi guda arba'in da hudu. Kana gari ne da yake da masarauta mai ɗunbun tarihi, mai kwarjini a cikin kasashen Hausa da kewayenta. Haka zalika Kano gari ne babba wanda mazauna cikinta ke magana da harshen Hausa. Itace gari mafi yawan jama'a a Najeriya baki ɗaya.
Kanon ta yi suna wajen kasuwancin da ta bunkasa a kai, har ya zamana ana cewa da ita Cibiyar Kasuwanci. Haka kuma tarihin Kano ya nuna daman can tana da suna wurin cinikayya tsakaninta da mutanen gabas ta tsakiya.
Yawan mutanen da suke garin na Kano sun haura kimanin mutane miliyan goma (10.000,000) a ƙidayar da aka yi a shekara ta alif dubu biyu da shida. Jihar Kano tana da matuƙar tasiri a yawan mutane Najeriya, saboda ita ce ta fi kowacce jiha yawan mutane daga ko'ina a faɗin duniya, tun daga na kudancin Najeriya, har zuwa ƙasashen dake maƙwabtaka da Najeriya,hakq kuma za ka tarar da mutanen sin ( wato china) da kuma na ƙasashen larabawa har da turawan yammacin duniya mutanen Kano sun shahara wajen addini sosai.
ƘOFAR MATA.
Cikin wani layin masu rangwamen arziki na shiga. Duk da kasancewa safiya ce sosai. Hakan bai hana ganin yara suna kai kawo a cikin unguwa ba. Wasu suna kan layin siyan ƙosai, wasu suna kan layin siyan fanke. Wasu yaran da gasarar kokko na gansu a hannunsu. Kasancewar baifi ƙarfe bakwai da rabin safiya ba. Anata hada_hadar shirin karya kumallo. A bakin wani madaidaicin gida na tsaya marar fenti, mai ɗauke da ƙatuwar bishiyar durumi a ƙofar gidan ƙosasshiyar gaske. A ƙarƙashin wannan bishiyar na hango motoci biyu a fake, ɗayar golf 3 ce, ɗayar kuma Vectra ce. Da dukkan halama motocin ta masu gidance. Wani matashine ya fito daga gidan hannunshi riƙe da bokitin ƙarfe cike dumbul da ruwa, ga soson buhu a ɗayan hannun nashi. A gaban motocinnan ya ajjiye bokitin, nan take ya soma watsa ma Vectra ɗinnan ruwa. Daga cikin gidan dai na jiyo hayaniya na tashi kuma muryar namiji nake jiyowa, har da kukan mace daga bisani na jiyo. Ba shiri na faɗa cikin gidan dan ganin meke faruwa haka.
Abun mamaki ashe gidan babbane sosai daga ciki, gashi da yalwar tsakar gida. Ɗakuna kuwa gasunan a jejjere kamar a zangon baƙi ( Hotel). Maza da matan gidan, harma da yaran gidan na tarar a tsakar gidan. Wani babban mutum na gani yana ta faɗa, muryarshi ce take fita har ƙofar gida. Babbane a shekaru, dan har da furfura a gemunshi da sumar kanshi. A gefenshi na hango wata doguwar fara kyakkyawar mace a tsaye jikinta sharkab da ruwa har ɗiga take yi tsabaragen jiƙewa, kuka take yi ƙaƙas tamkar wacce akayi ma mutuwa, gata ita dai ba yarinya bace. Wannan Dattijon cikin murya mai amon ɓacin rai yace.
"Haula ki dena kukan ya'isa ki bari su fito inji in shi Gwadabenne yasa matar tashi ta watsa miki ruwan kashi sai in ji. Ke da gidan mijinki babu wanda ya'isa ya takura miki wallahi, zan ture zumunta in kori Gwadabe da iyalinshi a gidana, wannan ƙazanta ta buskuta samodarar matarshi ni ya isheni. Ina mai takaici da baƙin cikin haɗa zuriya da matar Gwadabe da mu ka yi" Ya ƙarashe maganar yana huci kamar zaki."
Gwadabe:.
Da sauri ya fito daga É—akin nashi rigarshi a hannu, shimi ce a jikinshi da koÉ—aÉ—É—en wandon jeans wanda akayi ma wanki sama da sau saba'in, duk yayi yaushi, ya sake kala daga turarren bulu, izuwa kalar sararin samaniya.
"Yaya Hambali kayi haƙuri dan Allah. Kema Yaya Haula ki yi haquri. Iyabo ba da saninta ta watsa miki ruwan kashi a jiki ba. Bata san kina banɗakin bane, amman kiyi haƙuri dan Allah, kuma zata kiyaye " Gwadabe ya faɗa cikin sigar kare iyalinshi, duk da abinda ya faɗan gaskiya ne. Amman dake a hasale suke da Iyabo shi yasa maganar take ƙoƙarin zama babba. Dama ƙiris suke jira ta kuskure su dirar mata a wuya, sabida tsantsar ƙiyayyar da suke nuna ma Iyabo wacce har idanuwansu suka rufe wannan ƙiyayyar tashafi ɗan uwansu gudan jininsu Gwadabe. Harisu wanda ya kasance wa ga Gwadabe, ƙani ga Hambali, ɗa na uku a wajen mahaifiyarsu yace.
"To ita shafaffiyar da mai bamu da matsayin da zata iya fitowa ta ba Yaya Hambali da Yaya Haula haƙuri kenan ko yaya akayi ne Gwadabe?. Nifa na kasa gane wannan baƙin sha'ani naka da iyalinka kanka kalau yake kuwa" Yaya Hambali wanda maganar Harisu ta kasance tamkar zuga a gareshi yace.
"Ta fito ta ba da haƙuri kuwa Harisu? alhalin ba ganinmu da gashi take yi ba. Gwadabe ya gama watsar mana da darajarmu a idanunta. Allah wadaranka Gwadabe ka cucemu daka cakuɗa mana iri da Iyabo, ba zamu taɓa yafe maka cutarwar da kayi mana ba."
"Ya'isa haka Yaya Hambali dan Allah mana. Wannan maganganun tamkar cin fuskane a wajen Iyabo. Sannan ni banga aibu ko laifin Iyabo dan ta kasance Beyerabiya ba. Ni da ku, da iyabo duk musulmaine,kuma duk mutanene Allah ɗaya muke bauta ma, kuma kamar yadda muke sallah, da azumi haka take yi itama" Azabure Hambali yayi kanshi a zafafe yana shirin dukan ƙirjinshi. Harisu ne yai musu iyaka ta hanyar shiga tsakiyarsu dukan ya sauka tabb a tsakiyan gadon bayan Harisun tsabar zafin dukan saida ya gantsare. Jikin Yaya Hambali har rawa yake yi yana ganin Gwadabe kamar yayi mishi rashin kunyane. Barinma yana ganin Gwadabe tamkar shi ya tsugunna ya haifeshi tsabar girme mishi da yayi. Mutum huɗu ne a tsakaninsu kafin Gwadabe. Akwai Yaya Halima wacce ta kasance itace Babba a cikin ummansu, sannan shi Yaya Hambalin, ga Harisu, sannan ga ɗan Fodiyo, ga Sukairaju. Shi Gwadabe daga shi sai Da'u, daga Da'u sai Zakari, sai ƴar Auta Sauwama." Shi kanshi Gwadaben har cikin ƙoƙon ranshi baiji daɗin yanda yayi ma Yaya Hambalin ba, ko babu komai ya girme mishi, kuma shine makwafin uba a garesu baki ɗaya, gashi cikin ummanshi. Yaya Hambali ya bauta musu sosai, kasancewar tun suna ƙananu Allah yai ma mahaifinsu rasuwa. Shi ya maye musu gurbin uba, shine noma, shine kiwo, Fataucin dabino kuwa shi ya gaji mahaifinsu, yayi musu dukkannin wani gata har Allah ya cicciɓesu suka kai matakin mallakar hankali da girman jiki, dana haihuwa.
"Lallai Gwadabe baka da hankali ba'acikin hayyacinka kake ba, matarka da danginta sun gama mallakeka, imma ka yarda, imma ka ƙaryatani, tunda ka soma sa'insa damu shingin duka ya rage.Yaya Hambalin kake mayarma da magana?" Cewar Ɗan Fudiyo wanda ya cike da mamakin ɗan uwan nasu Gwadabe" Yaya Hambali kuwa tsai yayi yana kallon Gwadabe, tare da ƴan uwanshi da suka dira mishi a ka, kowa na tofa albarkacin bakinshi a kan abunda matarshi Iyabo ta yi, da abunda ya aikata yanzu. Gabaki ɗaya Gwadabe sai ya dibibice, kasancewar ba halinshi bane raina na gaba an yi mishi wannan kyakkyawar shaidar sosai. Ya fusata ainun ne da yanda suke cin zarafin iyalinshi ba dare ba rana, ba tare da ta yi musu laifin zaune ba, balle laifin tsaye. ana cikin haka Sai ga Iyabo ta ƙaraso wajen a kidime, jikinta har rawa yake yi dan tasan Gwadabe ba karamin ruwa ya kirawo mata ba"
ROMO ÆŠANYE"
GAWURTATTU UKU
DAGA ALƘALAMIN BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI
MARUBUCIYAR LITTAFIN NA FAÆŠO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA (LABARIN SHANONO DA OGA KAILA.
NA SAKE DAWOWA DA WANI LABARIN MAI ƊAUKE DA DARASI, DA BAN TAUSAYI, SADAUKARWA, TSAGWARON ZUNZURUTUN SOYAYYA DA ƘAUNA, FARIN CIKI, BAƘIN CIKI DUK A CIKIN WANNAN LITTAFI MAI SUNA A SAMA. KU BIYONI KU SHA KARATU.
ALƘALAMINA BAYA RUBUTA ABINDA BAZAI AMFANAR DA AL'UMMAR ANNABI BA.
KAMAR YADDA NA SABA WANNAN LABARIN SHIMA YA FARU A GASKEN GASKE, KU BIYO NI DA HANKICI DOMIN SHARE HAWAYEN DA ZASU ZOBO A GURABEN IDANUWANKU. KU GYARA ZAMA DA KYAU KU BI LABARIN SANNU_SANNU ZAKU FAHIMCI INDA YASA GABA.
Lamba ta 1
JIHAR KANO:
Kano na ɗaya daga cikin manyan birane a ƙasar Hausa. Kano itace cibiyar kasuwanci ta Najeriya gaba ɗaya. Jihar ta Kano tana da ƙananan hukumomi guda arba'in da hudu. Kana gari ne da yake da masarauta mai ɗunbun tarihi, mai kwarjini a cikin kasashen Hausa da kewayenta. Haka zalika Kano gari ne babba wanda mazauna cikinta ke magana da harshen Hausa. Itace gari mafi yawan jama'a a Najeriya baki ɗaya.
Kanon ta yi suna wajen kasuwancin da ta bunkasa a kai, har ya zamana ana cewa da ita Cibiyar Kasuwanci. Haka kuma tarihin Kano ya nuna daman can tana da suna wurin cinikayya tsakaninta da mutanen gabas ta tsakiya.
Yawan mutanen da suke garin na Kano sun haura kimanin mutane miliyan goma (10.000,000) a ƙidayar da aka yi a shekara ta alif dubu biyu da shida. Jihar Kano tana da matuƙar tasiri a yawan mutane Najeriya, saboda ita ce ta fi kowacce jiha yawan mutane daga ko'ina a faɗin duniya, tun daga na kudancin Najeriya, har zuwa ƙasashen dake maƙwabtaka da Najeriya,hakq kuma za ka tarar da mutanen sin ( wato china) da kuma na ƙasashen larabawa har da turawan yammacin duniya mutanen Kano sun shahara wajen addini sosai.
ƘOFAR MATA.
Cikin wani layin masu rangwamen arziki na shiga. Duk da kasancewa safiya ce sosai. Hakan bai hana ganin yara suna kai kawo a cikin unguwa ba. Wasu suna kan layin siyan ƙosai, wasu suna kan layin siyan fanke. Wasu yaran da gasarar kokko na gansu a hannunsu. Kasancewar baifi ƙarfe bakwai da rabin safiya ba. Anata hada_hadar shirin karya kumallo. A bakin wani madaidaicin gida na tsaya marar fenti, mai ɗauke da ƙatuwar bishiyar durumi a ƙofar gidan ƙosasshiyar gaske. A ƙarƙashin wannan bishiyar na hango motoci biyu a fake, ɗayar golf 3 ce, ɗayar kuma Vectra ce. Da dukkan halama motocin ta masu gidance. Wani matashine ya fito daga gidan hannunshi riƙe da bokitin ƙarfe cike dumbul da ruwa, ga soson buhu a ɗayan hannun nashi. A gaban motocinnan ya ajjiye bokitin, nan take ya soma watsa ma Vectra ɗinnan ruwa. Daga cikin gidan dai na jiyo hayaniya na tashi kuma muryar namiji nake jiyowa, har da kukan mace daga bisani na jiyo. Ba shiri na faɗa cikin gidan dan ganin meke faruwa haka.
Abun mamaki ashe gidan babbane sosai daga ciki, gashi da yalwar tsakar gida. Ɗakuna kuwa gasunan a jejjere kamar a zangon baƙi ( Hotel). Maza da matan gidan, harma da yaran gidan na tarar a tsakar gidan. Wani babban mutum na gani yana ta faɗa, muryarshi ce take fita har ƙofar gida. Babbane a shekaru, dan har da furfura a gemunshi da sumar kanshi. A gefenshi na hango wata doguwar fara kyakkyawar mace a tsaye jikinta sharkab da ruwa har ɗiga take yi tsabaragen jiƙewa, kuka take yi ƙaƙas tamkar wacce akayi ma mutuwa, gata ita dai ba yarinya bace. Wannan Dattijon cikin murya mai amon ɓacin rai yace.
"Haula ki dena kukan ya'isa ki bari su fito inji in shi Gwadabenne yasa matar tashi ta watsa miki ruwan kashi sai in ji. Ke da gidan mijinki babu wanda ya'isa ya takura miki wallahi, zan ture zumunta in kori Gwadabe da iyalinshi a gidana, wannan ƙazanta ta buskuta samodarar matarshi ni ya isheni. Ina mai takaici da baƙin cikin haɗa zuriya da matar Gwadabe da mu ka yi" Ya ƙarashe maganar yana huci kamar zaki."
Gwadabe:.
Da sauri ya fito daga É—akin nashi rigarshi a hannu, shimi ce a jikinshi da koÉ—aÉ—É—en wandon jeans wanda akayi ma wanki sama da sau saba'in, duk yayi yaushi, ya sake kala daga turarren bulu, izuwa kalar sararin samaniya.
"Yaya Hambali kayi haƙuri dan Allah. Kema Yaya Haula ki yi haquri. Iyabo ba da saninta ta watsa miki ruwan kashi a jiki ba. Bata san kina banɗakin bane, amman kiyi haƙuri dan Allah, kuma zata kiyaye " Gwadabe ya faɗa cikin sigar kare iyalinshi, duk da abinda ya faɗan gaskiya ne. Amman dake a hasale suke da Iyabo shi yasa maganar take ƙoƙarin zama babba. Dama ƙiris suke jira ta kuskure su dirar mata a wuya, sabida tsantsar ƙiyayyar da suke nuna ma Iyabo wacce har idanuwansu suka rufe wannan ƙiyayyar tashafi ɗan uwansu gudan jininsu Gwadabe. Harisu wanda ya kasance wa ga Gwadabe, ƙani ga Hambali, ɗa na uku a wajen mahaifiyarsu yace.
"To ita shafaffiyar da mai bamu da matsayin da zata iya fitowa ta ba Yaya Hambali da Yaya Haula haƙuri kenan ko yaya akayi ne Gwadabe?. Nifa na kasa gane wannan baƙin sha'ani naka da iyalinka kanka kalau yake kuwa" Yaya Hambali wanda maganar Harisu ta kasance tamkar zuga a gareshi yace.
"Ta fito ta ba da haƙuri kuwa Harisu? alhalin ba ganinmu da gashi take yi ba. Gwadabe ya gama watsar mana da darajarmu a idanunta. Allah wadaranka Gwadabe ka cucemu daka cakuɗa mana iri da Iyabo, ba zamu taɓa yafe maka cutarwar da kayi mana ba."
"Ya'isa haka Yaya Hambali dan Allah mana. Wannan maganganun tamkar cin fuskane a wajen Iyabo. Sannan ni banga aibu ko laifin Iyabo dan ta kasance Beyerabiya ba. Ni da ku, da iyabo duk musulmaine,kuma duk mutanene Allah ɗaya muke bauta ma, kuma kamar yadda muke sallah, da azumi haka take yi itama" Azabure Hambali yayi kanshi a zafafe yana shirin dukan ƙirjinshi. Harisu ne yai musu iyaka ta hanyar shiga tsakiyarsu dukan ya sauka tabb a tsakiyan gadon bayan Harisun tsabar zafin dukan saida ya gantsare. Jikin Yaya Hambali har rawa yake yi yana ganin Gwadabe kamar yayi mishi rashin kunyane. Barinma yana ganin Gwadabe tamkar shi ya tsugunna ya haifeshi tsabar girme mishi da yayi. Mutum huɗu ne a tsakaninsu kafin Gwadabe. Akwai Yaya Halima wacce ta kasance itace Babba a cikin ummansu, sannan shi Yaya Hambalin, ga Harisu, sannan ga ɗan Fodiyo, ga Sukairaju. Shi Gwadabe daga shi sai Da'u, daga Da'u sai Zakari, sai ƴar Auta Sauwama." Shi kanshi Gwadaben har cikin ƙoƙon ranshi baiji daɗin yanda yayi ma Yaya Hambalin ba, ko babu komai ya girme mishi, kuma shine makwafin uba a garesu baki ɗaya, gashi cikin ummanshi. Yaya Hambali ya bauta musu sosai, kasancewar tun suna ƙananu Allah yai ma mahaifinsu rasuwa. Shi ya maye musu gurbin uba, shine noma, shine kiwo, Fataucin dabino kuwa shi ya gaji mahaifinsu, yayi musu dukkannin wani gata har Allah ya cicciɓesu suka kai matakin mallakar hankali da girman jiki, dana haihuwa.
"Lallai Gwadabe baka da hankali ba'acikin hayyacinka kake ba, matarka da danginta sun gama mallakeka, imma ka yarda, imma ka ƙaryatani, tunda ka soma sa'insa damu shingin duka ya rage.Yaya Hambalin kake mayarma da magana?" Cewar Ɗan Fudiyo wanda ya cike da mamakin ɗan uwan nasu Gwadabe" Yaya Hambali kuwa tsai yayi yana kallon Gwadabe, tare da ƴan uwanshi da suka dira mishi a ka, kowa na tofa albarkacin bakinshi a kan abunda matarshi Iyabo ta yi, da abunda ya aikata yanzu. Gabaki ɗaya Gwadabe sai ya dibibice, kasancewar ba halinshi bane raina na gaba an yi mishi wannan kyakkyawar shaidar sosai. Ya fusata ainun ne da yanda suke cin zarafin iyalinshi ba dare ba rana, ba tare da ta yi musu laifin zaune ba, balle laifin tsaye. ana cikin haka Sai ga Iyabo ta ƙaraso wajen a kidime, jikinta har rawa yake yi dan tasan Gwadabe ba karamin ruwa ya kirawo mata ba"