← Book details Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 113 OF 237

Sashe 113

Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana fitowa daga ɗakin Hadiza ya sauke ajjiyar zuchiya sassanya. Tsaki yaji an doka daga gabanshi, ɗagowar da zaiyi yaga ashe Baba Asshi ce a tsaye da yaranta da matansu a tsakar gidan suna ƙus_ƙus. "Ina wuni Baba Asshi?" In kun tanka Baba Asshi ta tanka. Saida ya wuce ta sake jan wani dogon tsakin, kanshi kawai ya gyaɗa yana fata da burin kar a samu irin wannan rarrabuwar kan a nashi gidan. Da sallama ya shiga ɗakin Amarya Shafa. Tana zaune akan kujera tasha adon atamfarta baƙar macce ƴar leda. Bakinnan nata yasha janbaki raɗau sai sheƙi yakeyi. Komai zaune yake daram a muhallinshi. Da sauri Shafa ta miƙe ta tawo da sassarfa izuwa wajen mijinta. Isowarta ke da wuya ya haɗe jikinshi da nata ya riƙeta gam. Ajjiyar zuchiya ya sauke mai ƙarfi a zuchiyarshi yace.."Lallai aure ni'imace akwai hikima a auren mata biyu, shi yasa ubangijinmu ya umarcemu da somawa da biyu madamar zamuyi adalci. Ko wacce mace da irin ƙamshinta, taushin fatarta, kalaminta, Sannan da irin baiwar da Allah subuhanahu wata ala yai mata. A wannan daren Amarci Gwadabe ya gwangwaji Amarcinshi lami lafiya kuma Alhamdulillah Shafa ta kawo cikakken budurci marar kokonto a cikinshi. Tana kwance a ƙirjin mijinta tana baccin daɗi da wahala zuchiyoyinsu fes. Ta ɓangaren Hadiza kuwa tana kwance tana lissafe lissafe gami da hasaso abinda bazai taɓa bata kwanciyar hankali da nutsuwa ba. Dan a wannan daren sai da ta dinga tambayar kanta to waima me yasa ta amince da Auren Gwadabe ne ma?" Nasihu da surruka, da dabarun zama da kishiya, da zama tauraruwa a idanun miji da Baba Fhatsima ta karanto mata, shi ya sake faɗi mata. Wasu zafafan hawaye suka gangaro suka wanke mata kumatunta. Zurub ta miƙe ta faɗa banɗaki ta ɗauro alwala ta koma ɗakinta. Ta maye gurbin tunane_tunanen da basu da amfani da yin sallolin nafila tana miƙa kukanta ga Ubangiji kan ya sassauta mata kishin dake zuchiyarta. Yaa kuma kareta da cutar da abokiyar zamanta koda da furucine. Ya ɗaga daraja da kimarta a idanun mijinta. Haka ta dinga sallah tana adda'a, ai kuwa saida taga bacci yana shirin kayar da'ita sannan ta kwanta. Ta kuwa samu bacci mai nutsuwa kuma nannauya. Asubar fari ta miƙe ta nufi kitchen. Dai_dai Shafa itama ta buɗe ƙofar ɗakinta ta fito kitchen. Idanu suka haɗa duk da dai akwai duhu amman sunsan juna suke kallo. "Yaya barka da asuba" Shafa ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe kitchen ɗinta. "Yauwa barka dai Amarya mai maganar suger. Ya kwanan angon naki?" Shafa tayi murmushi ta ɗan sauke kanta ƙasa bata ce komai ba dai. Kitchen Hadiza ta faɗa tana murmushi, amman a baɗini zuchiyarta ma bugawa yake yi, hatta hannayenta sai taji suna rawa kakakar_kakakar. Cikin zuchiyarta tace. "Kishi bala'ine. Gaskiya mana a gidanmu aka kasa samun dedeto. Ashe haka kishi yake da tasiri mai girma?" Hawayen dake shirin zubowa a idanunta ta mayar da hanzari. A gurguje ta kunna risho ta faɗa banɗaki bayan ta ɗora ruwan wanka. Jikinta a mugun mace ta fito daga banɗakin, daidai Gwadabe ya fito daga ɗakin Shafa zaije wankan tsarki. Shafar tana biye dashi da dukkan halamu tare zasu je suyi wankan. Lallai soyayya ta kai soyayya. Murmushi ta sakarma Gwadabe, murmushin daya kasance tamkar garwashi wajen ƙuna. Shigewa tayi ɗaki tana haki. A daddafe tayi ra'atanil fajir, ta ɗaura da sallar asuba. Ta jima sosai akan sallaya tana roƙon Allah ya sa mata salama a zuchiyarta game da wannan kishi mai kai mata mahallaka ya baro. Saida ta karanta Qur'ani suratul naba'i ta shafa adda'a sai taji zuchiyarta tayi wasai. Cikin sauƙin zuchiya ta shalla wanka, ta shiga gyaran ɗakinta cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala, a madadin kunna turaren wuta tunda bata da gawayi kuma yayi wuri ta aika gida a ɗebo mata saita kunna ɗan tsinke ta bishi da Room freshener na MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI mai ƙamshin oud Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya ɗauki saiti. Zama tayi a barandar data haɗa ƙofofin uku, tana iya hango masu gilmawa, suma suna iya hangota. Doya ta gutsura ta fereye kaɗan, ta ɗaura abun suyanta ta zuba mai ta soma suyan doya. Matar Sabitu ce ta fito tsakar gidan taci uban ƙananun kaya kanta babu ko ɗankwali kasancewarta mai gashi daidaiya, sai karairaye takeyi da ledar shara a hannunta ta gangara ƙasan gidan dan jefar da ledar shara a babban durom ɗin shara dake gefen bayan gidan tsakar gidan. Kai Hadiza ta jirjiza kawai. Doyarta ta soyu ta kwashe ta juye man a samira ta adanashi. Sai ta mayar da kaskon kan wuta ta fasa ƙwai biyu ta yanka albassa ta ɗan barbaɗa dunƙule ta soye ƙwanta gidan ya kaure da ƙamshi. Da ɗaya da ɗaya amaren gidan suketa fitowa domin ɗora abinda za'a durama ƴan hanji, dama dai kunsan Amare a gigice suke tashi da yinwa. Ruwan tea Hadiza ta haɗa dama tana da ruwan zafi a flaks ɗinta. Ta gama haɗa kayan karyawanta tsab ta kai ciki. Ta yafa mayafinta da ƙaton kaskonta me murfi ta fito tsakar gidan. Ta haɗu da matar Abdullahi da matar Jazuli, babu wanda ya kalleta itace dai ta gaishesu a wani wulaƙance suka amsata har suna shewa, ko ta mecece ohon musu dai. Ɓarayin su Yaya Tasi'u ta nufa. Da matar Yaya Jamilu ta soma cin karo Innar Khadija. Tana soya dankalin turawa a ƙofar kitchen ɗinta a gawayi. Tayi kaca_kaca da wajen, ɓawon dankalinma da ɓaron ƙwai duk ta zubar a ƙasa yara sun tattaka. "Me zan gani Amarya sassafe haka. Af na mance ashe zawara kwana uku akeyi mata ango ya koma ɗakin Amarya ko?" Ɗan murmusawa Hadiza tayi, inda sabo ta riga da tasan dama irin zaman da akeyi. Magana ta arziki bata haɗa kowa da kowa, face habaici da son gumama juna. "Hakane ango yana ɗakin Amarya. Nima gaushi nazo ku bani" Sai ta tuntsure da dariya tace. "Ga gaushi zo ki ɗiba kafin ku soma hura naku. Tunda me gidan maganin ƙarfin maza yake siyarwa" Ajjiye kaskon tayi, domin furucin Innar Khadija yayi mata zafi. Sun daɗe suna kushe sana'ar Gwadabe a cikin gida. Dan Amaryar Malam har yara take turawa da nera ɗari tace wai a bata maganin basir malam zata ba. "Bari in gaisa da Anty Badi'a tukunna sai inzo in ɗiba." Nan ta wuceta ta barta da zunɗenta ta baya. Tun daga kofar da zata sadaka da ɓarayin Anti Badi'a kake jiyo ƙamshi na tashi. Falonta tsab yasha gyara, ta shiga ta samu Sailuba na fesa Room freshener a labulayen ɗakin. Anty Badi'a data ci kwalliya da riga da sikert ɗan kanti wani mai tattara na zamanin tana gaban durowar da tv yake kai tana juna abun ƙona turaren wuta mai amfani da wuta ( electric burner wanda a lokacin batai yawa ba, sai gidan ƴan gayu ake iya ganinta) "Anty Hadiza, Mama ga Anty Hadiza " Cewar Sailuba kenan. Maman ta ɗago da dariya tace. "Uwargida sarautar mata ke ko me kike yi a nan sassafe kamar wacce tayi ɓatan kai?" Hadiza dake ta kallon falon kamar ta wanke makanta tace. "Ke dai Anty Bari. Kinga rushi nazo ɗiba inaso kafin in karya in kunna turaren wuta" Sai Anty Badi'a tayi Dariya tace. "Ina zuwa. Sailuba ki zuba mata farfesun kan ragonnan a ƙaramar kula maza" Ta shige ɗaki sai gata da sabuwar ( electric burner) a kwalinta ta miƙa mata dama guda biyu ta siyo tafiyarsu Umara ita da mijinta. "Ga wannan aita ƙona turare lafiya." Hadiza ta amsa da murnarta taima Anty Badi'a godiya mai yawa. "Na ganki da leshi kina wayayya. Ai leshi kwalliyar dare ce, ko rana. Da safe ai ƙananan kaya ya kamata ki mayar su zama ababen sawarki. Karfa ki ba damu yarinya ƙarama ta ciri kambu" Hadiza ta zaro idanunta waje tace. "Nifa Anty ƙananan kaya guda ɗaya jol gareni. Wata rigace doguwa mai hannu ɗaya. Itama ƙawatace ta kawo mun. Ina dai da rigunan bacci" Miƙewa Anty Badi'a tayi tace. "Jira" Bata jima ba sai gata da leda ta miƙo ma Hadiza. "Kije maza ki sake kayan jikinki ki sa wannan. Zuwa anjima Sailuba zata zo ta kira mun ke. Akwai Hajiyar da nake siyayyar ƙananun kaya a hannunta kayanta suna da kyau Dubai take siyosu. To anjima dama zata kawo mun kaya, da ƴan sabulan gyaran fata." Cikin murna Hadiza ta fito tana shima Anty Badi'a da albarka. Koda ta fito bata ga Innar Khadija ba, ta ɗebi gaushinta ta wuce. Tana kunna turaren wuta ta shige ɗaki ta buɗe ledar da Anty Badi'a ta bata. Riga da sikert ne irin na jikinta sak kalace ta bambanta. Na jikin Anty Badi'a siket ɗin mai ruwan gorrone, sai rigar mai ruwan madara da kwala a wuyan rigar. Ita kuma Hadiza nata siket ɗin kalan jinin karene maron sai rigar mai ruwan madara. Ta saka kayannan yayi ɗas a jikinta rigar ta ɗan matseta dan tafi Anty Badi'a cikar ƙirji. Tana gyara gashi ta jiyo sallamar Shafa a falo. Shi kuma gogan naka masu abu da abunsu sai ya kutso kai ya shigo cikin uwar ɗakin. Ƙur yayi mata da idanunshi yana mata wani mahaukacin kallo mai ɗauke da guguwar sha'awa da burgewa a ciki. Manna ƙirjinshi yayi a nata ƙirjin, yayi lub a jikinta yana shaƙar ƙamshin dake saurin tayar mishi da jarabarshi. Ajjiyar zuchiya Hadiza ta sauke. Gwadabe ya ɗago idanunshi da suka sauya kala yace. "Wallahi kinyi kyau sosai. Kayannan ya amshi jikinki da fatarki ƴar duma_dumata" Murmusawa tayi wani farin ciki ya baibaye zuchiyarta. "Nagode ango mijin Amarya. Naga sai sheƙin angwanci kake yi." Murmushi yayi mata dan yaji sautin kishi a muryar tata. "Shafa tana falo kizo muci abinci." Da sauri ta kalleshi tace. "Abinci kuma, a ina za'aci abincin ba'a ɗakin Shafa kake ba?" Dariya yayi mata. "Abincinne nace ta ɗakko muzo muci a nan ɗin. Hakan nake so mu dinga yi, sabida zai samar mana nutsuwa da fahimtar juna. Wacce bata da kwana ma zata samu damar zantawa da mijinta. Muje ko?" "Amman Yaya Gwadabe" "Shishshsh... Bana son kice komai, kizo muje" Ba dan ran Hadiza yaso ba dai. Tayo jigum har Gwadabe ya fice tana tsaya tana tunanin ta ina wannan lamarin zai soma. Yama za'ace wannan tsarine me kyau.
Chapter 113 · 0% Book details