Sashe 24
Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
8 A kwana a tashi A haka rayuwarmu tai ta garawa, yau fari gobe tsumma, babu laifi Alhamdulillah yanzu kam munfi Æ™arfin abinda zamu saka a bakin salati. Koda yaushe Gwadabe a cikin tafiye_tafiye yake, duk garin da ya je yakan siyo mana tsarabar garin, su bushasshen kifi, manja, doya, wake, gawayi duk yana siyowa ya kawo. Babala ta jima sosai a gidan sai data warke tsab, ana gobe zanyi arba'in ita kuma ta tattara ta koma Æ™auye. Irin Æ™oÆ™arin da taga Gwadabe nayi a kanmu sai ya sake dagula komai. A tsakar gida Babala bata da aikin daya wuce faÉ—in an ma É—anta asiri sai wahala nake bashi, ya shiga tarkon yarbawa jikokin oduduwa. In hakan baiyi mata ba sai ta sameni har É—aki ta Æ™aremun tanadi tsab, ni dai zaman gidan gabaki É—aya ya gundureni, haka naita haÆ™uri har Allah yasa ta koma Takai. Gwadabe ma haka yasha haÆ™uri da Babala, damuwa duk ta haÉ—u tayi mishi yawa, ga matsala da yake samu a wajen Æ´an lodi akwai wani bawan Allah da yasa Gwadabe sosai a gaba, domin yawan tashi da motar Gwadabe take yi wajen sufurin kaya, ada yafi kowa Æ™wazo a matukan tirelolin har ana mishi kirari da giya dubu, akwaishi da sharara gudu a hanya dandanan sai ya isa ikko, yana isa zai sauke lodi ya sake nauso hanya. To samuwar mota a hannu Gwadabe sai ya doke giya dubu wajen Æ™wazo da kazar_kazar bil haƙƙi Gwadabe yake komai. Wata rana ana ma Gwadabe lodi giya dubu shi kuma shigowarshi Æ´an lodin kenan, da ya kalli Gwadabe sai yace. "Wata rana ma ba zaka samu Æ™afafun da zaka taka mota ba, balle hannayen murza sitoyari in dai muna tasharnan gasa da ni ba daÉ—i." To daga ni har Gwadabe sai muka shiga damuwa daya dawo yake sanar dani, mu kaita adda'ar neman tsari harda sadaka, ga wannan damuwar ga damuwar Babala abubbuwa suka cakuÉ—e goma da ashirin. Washe garin ranar da Babala ta tafi muka cika kwanaki arba'in. Ƴan biyu sun yi kuÉ“ul kuÉ“ul dasu gwanin sha'awa. Tun sassafe naketa kaye_kaye dan yau kam a gidanmu zanje in wuni yawon arba'in. Kafin sha biyu na gama duk abinda ya dace, Toye na dawowa daga makaranta, na kwaÉ“e mishi inifom na watsa mishi ruwa, na shiryashi tsab, naima matan gida sallama. Atampa mai haske nasaka da sabon takalmi da mayafi, ina fita tun kafin in sauka daga kan tudun gidan na soma jiyo hayaniyar muryoyinsu suna gulmar da suka saba. Muna zuwa titi na tari Bus sai Æ™ofar Nasarawa inda anan gidanmu yake. Cikin layinmu na shiga tun daga titi nake gaggaisawa da mutane, wasu dole ma in tsaya su ga Æ´an biyu a haka harna isa Æ™ofar gidanmu. Gidane mai É—auke da karamar Æ™ofa gefe da gefen Æ™ofar shagunane biyu. ÆŠaya na Iyaa Debisi daya na Iyaa Kokodeen. Iyaa Debisi soson danga dasu lagwani, ashana, sitati, gyalu, bula, kayan robibi. Su take siyarwa tana da injin niÆ™a har biyu dana wuta dana ruwa. A shagonnan mu kai rayuwarmu, akwai Æ™ofa a cikin shagunan wanda zaka É“ulla babban tsakar gidan namu. Iyaa Kokodeen kuma albo, garin Amala, daddawar kalwa, da bushasshen rogo, garin rogo su take siyarwa harda ma kamun jar dawa. Wannan sana'ar tasu da ita muma mu ka yi wayo muka gansu akai, gashi har yanzu ana takusawa. A bencin dake Æ™ofar shagon Iyaa Debisi na zauna dan na gaji sosai. Toye kuma yayi cikin gida da gudu. Iyaa Debisi tana zaune a cikin shago taci leshi É—inkin buba É—aurin É—ankwalinnan a cukurkuÉ—e sai gyangyaÉ—i take ta yi abunta, dama kullum aikinta kenan wannan gyangyaÉ—i ba'a rabata dashi, kuma a zaune ake yinshi. Iyaa Iyaa!! Na kirayi sunanta tare da É—an buga benci kaÉ—an sai ta buÉ—e idanunta muka haÉ—a idanu. "Ahhh Iyabo kece da tsakar ranar nan da yara, ku yaran zamani baku da hankali ai mace mai goyo ko ciki bata fitowa sa'ilin da rana ta take. Maza shiga ciki gani nan zuwa. Mahaifiyarki ma yanzu isowarta ko awa É—aya ba'ayi ba tana ciki" MiÆ™ewa nayi ina fara'a dan na jima banga Mamana ba. Shagon Iyaa Kokodeen na shiga na durÆ™usa a gabanta na gaisheta , itama tace maza in shiga ciki rana ta take. Ko da na shiga samarin gidan basa nan kowa na wajen aiki, babu Æ´an mata a gidan tuni sun jima da aure, Bose ce da aka bari itama gashi tana gidan mijinta. Sai matan Æ™annen su Iyaa su su uku Iyaa Beji, da Iyaa Lekan, sai Iyaa Amope. A É—akinmu na ya da zango mahaifiyata tana tsaye tana sallah goduwa farar bafulata siririya, gata da alkunya da sanyin hali bata iya sakewa tayi hira dani, iyakarta dani gaisuwa da tambayar ya nake ni da mai gidan nawa. Iyakar hirata da'ita kenan saita tsuke bakinta tayi shiru kanta a sunkuye." Tana idarwa ta juyo tace. "Jabu kune a tafe? ( Jabu sunan da dangin mahaifiyata suke kirana dashi kenan, dangin mahaifina kuma iyabo)" Data juyo sai naga ta rame sosai idanunta sun zurma da yawa" Dada kinzo lafiya ina wuni?" Bata amsaba sai miÆ™o mun hannu da tayi na tashi na sunto yaran na saka mata a cinyarta. Tayi Æ™uri tana kallonsu tana musu adda'a. Take Naji hawaye na kwarara a idanuna, Allah ya É—aura mun tausayinta sosai a zuchiyata. Inna dubeta sai inga kamar tana cikin Æ™unci da matsi a gidan aurenta. Dada baki da lafiya ne naga kin rame?" Cikin gurÉ“atacciyar hausarta ta fulanin daji tace " E jinya nayi kusan wata shida sai dai a kwantar sai dai a tayar, shine dalilin da yasa ban É“ulloku ba." Sai kuma taci gaba da magana dani da yarbanci, dan Hausa mugun wahala take bata, dama da yarbancin muke magana." "Ashe kin samu Æ™aruwa Allah ya raya. Ina É—ayan jikan nawa?" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Yana É—akin Iyaa Beji can na baro shi, ya wajen BaÉ—É—o da mai gidanta? ( BoÉ—É—o Æ™anwatace a gidan da Dada take aure yanzu, sau É—aya na taÉ“a ganinta tal a rayuwata) "ÆoÉ—É—o ta haihu tana goyon Daso an yi mun takwara" Sai naji ina kewar Æ™annena da dangin mahaifiyata ma, sai naji inason kasancewa dasu. Dada inaso in zaki koma zan tambayi izinin mai gidana zan biki in gano rugarku, inaso lokaci zuwa lokaci in dinga zuwa ziyartarki ke da danginki nima ya kamata yarana su san dangina na wajen uwa su saba" Da sauri ta É—ago ta dubeni tace. "Kar ki soma, kiyi zamanki na yafe miki. Ni zan dinga zuwa ina dubaki kamar yadda na shafe sama da shekaru ashirin ina zuwa ganinki." Ƙur nayi mata da idanu ina karantar yanayinta, duk sai naga ta ruÉ—e, tashi tayi ta bani su Taiwo ta haye Æ™aramin gadon Iyaa ta kwanta ta juya mun baya. Na rasa me ake É“oye mun ne da Dada bata Æ™aunar in ziyarceta, bata son danginta su sanni, to meke faruwa ne tabbas tana Æ™asa tana dabo. Iyaa ce ta shigo tana faÉ—a sosai kamar zata ari baki, tana yi tana dukan cinyarta tanata faman yare. Ashe da Debisi take yi shigowarshi cikin gidan kenan. Da yare yace da'ita. "Kiyi haÆ™uri Iyaa nifa ba cewa nayi yemisi ta ajjiye aikinta ba, gani nayi ta fifita aikinta fiye da zaman auren da muke yine. Kuma tama ga damar zuwa ta haÉ—a mun jarfa ne" Ya Æ™arashe a sanyaye. Iyaa Kokodeen ce ta shigo É—akinnan tace. "Haba Iyaa Debisi wannan yaron fa yana da gaskiya kuma ma ai yayi Æ™oÆ™ari sosai Ya kamata itama yemisi ta dena zuwa tana yawon kawo Æ™ararshi wajenki ko wajen mahaifiyarta. Ai ga irinta nan abunda ake hango muku daban abinda kuke hango ma kawunanku daban, ku kun É—auke mu ba wayayyuba. Dama duk namijin da zai auri soja ai dole sai dai ayi zaman haÆ™uri." Wannan maganar tamkar ingiza iyaa Debisi Iyaa Kokodeen tayi dama har gobe da mikin Æ™in aurena da Burodami Debisi yayi a zuchiyarta. Dan da Æ™yar ma aka shawo kanta bayan aurena ta zubar da makaman yaÆ™inta, macace mai kafiya da binbinni, gata da mita. "Basshi ai duk abinda na guje mishi kenan, shi yasa naso ya auri Æ´ar uwarshi Iyabo. Musamman dana fahimci ita iyabon tana sonshi. A gida ma ita ke kula da komanshi ina ga ya aurata. Yaronnan ya buÉ—a mana Æ™asa a idanu, dana matsa ya je ya haÉ—oni da dangin ubanshi akazo aka danneni. To yanzu me yake so ayi mishi? Ai haka zaka je kaita kwashe takaici da baÆ™in cikin zama da Soja, kuma ban yarda ka sake takurama Yemisi akan batun aikinta ba." Daga ni har Burodami Debisi muka yi tsamo_ tsamo tamkar kazar data faÉ—a ruwa, ya É—ago mu haÉ—a idanu ya kasa sabida kunya tare da nadamar abinda ya aikata. Lokacin na shiga tunanowa a zuchiyata, a lokacin da Burodami Debisi ya murtsuke idanunshi yace shi Allah ya kashe shi bazai aureni ba. Ji nayi tamkar alÆ™iyamatace ta tsaya. Abun bai zo mun da daÉ—i ba, domin jaririyar zuchiyata da so da tsantsan kaunarshi ta ginu, ban taÉ“a tunanin zuchiyata zata iya son wani mahaluki bayan Burodami Debisi ba. Ni ban iya sa abu a zuchiyaba, ban iya son abuba. Da wasa da wasa Gwadabe ya maye gurbin dana adana Burodami Debisi a ciki, harya samu matsayin da shi kanshi Burodami Debisi bashi da irinshi. Yanzu kuwa da Gwadabe ya riga ya lasamun giyar sonshi na shiga mayen Æ™aunarshi jinshi nake tamkar numfashina, ko kuma bugun zuchiyata, ina ma mijina irin son da har abada bazai iya samun macen da zata so shi kwatan son da nake yi mishi ba. Muryar mahaifiyata ne ya katsemun tunani, cikin Æ™warewa a yaren yarbanci ta soma magana kamar ba bafulatana ba. "Ai aikin gama tuni ya gama. Abinda zai faru ya faru. Jabu tayi aure harda albakar aure. Shima Debisi yayi aure harda Æ™aruwar haihuwa. Ni ina ganin Toyosi ki yi haquri ki kawar da wannan batun. Kai kuma Debisi aure ai cike yake da Æ™aÉ—darori iri daban _daban. Ita kanta Jabu kana ji da ganin irin matsalolin da take fuskanta da dangin mijinta, auren ba daÉ—inshi take ji ba ana dai zaune zaman yara ko ba haka ba Alima?" Ta kai dubanta kan Iyaa Kokodeen wacce ainihin sunanta Halima, to a