← Book details Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 237

Sashe 28

Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kinga can wajen tudun?" Gwadabe ya nuna mun da hannunshi. Wani dan tudune karami akayishi a falon kamar wajen cin abici. ( Daining )Amman bashi da girma, a wajen na saka kayan kallona. "To ki fito da kayan kallon gobe zan siyo miki teburi da dirowar da zaki dinga zuba kayan abinci a ciki. Zaki dinga amfani da risho, ke ko gawayinne in kika kunna a ƙofar ɗaki daya ruru ki shigo dashi, ki sa labule wajen ya zama miki kicin. Iyabo bana so ki sake fita na kuma na jajjada miki. Kiyi haƙuri wata rana sai labari. Ki daure wallahi ba'a sona haka ke faruwa ba, naso mu bar gidannan muyi nesa da ƴan uwa Kuka babu irin wanda banyi ba, washe gari kuwa sai ga Gwadabe da tebur, da durowarshi gajera ta kicin ɗin ƴan gayu. Tare muka jera kayan tukwanena da ɗan kayan abinci da nake dasu, har randunana a cikin wajen na jera, Gwadabe ya hau ya kafa mun labele, Laila sai zirga_zirga take yi tsakanin tsakar gida da ciki. Bai fita ba sai da ya ciccika mun randunanan da ruwa tab, kana ya fice kasuwa. Ni kuma na shiga aikace, aikacen gidan. Bani na fita tsakar gida ba sai da na gama komai nawa na fito da ruwa bokiti uku na sheƙar a rariya, bokitin dana shake shi da wanki na fita dashi na je maƙota na shanya. Ina dawowa na yi komawata ɗakina. Haka al'amuran rayuwar su kaci gaba da gudana yau fari gobe tsumma. A kwana a tashi, gashi yau mun wayi gari jama'ar Takai suna hanyar shigowa Kano. Gidan namu shaƙe da matan anguwa suna ta faman taya mu aikace_aikacen biki. Dan Yaya Haula hantsice leƙa gidan Kowa, babu gidan da bata shiga, kowa a layinnan ya santa. Gida ya ɗau fenti, ga girma da gidan ya ƙara, sakamakon gidaje biyu na jere damu da Yaya Hambali ya siya, aka rushe katangun gidan ya ƙara girman gaske, kuma yasha gyara sosai. Ɓangaren Amarya Laraba da Ango Nazifi ya sha gyara na musamman. Wajajen la'asar sai ga ƴan Takai sun iso Bus biyu su da gayyar yara raɓe_raɓe, gida ya kacame da hayaniya, amman nifa babu wanda yazo daidai da ƙofar ɗakina . Washe gari aka shiga biki ka'in da na'in. Ranar ɗaurin aure tun duku_ duku muka game jallof ɗin shinkafa, da tuwon shinkafa, harda masa. Su Gwadabe kuma suka kama hanyar Takai dan acan za'a ɗaura auren kasancewar duk haɗin gidane. Ko akwatin Amaryar Nazifi baa'a kaiba, ance in aka kawota sai kawai a miƙa. Akwatuna masu taya suna nan a ɗakin Yaya Haula, ina dai gani matan waje sunata shigowa kallon kaya. Ni ko da nake gidan babu wanda ya neme ni da in zo in ga kaya, nima ban ɗaɗa kaina ba. Bayan azahar maza ƴan ɗaurin aure suka dawo tare da bataliyar maza ƴan Takai. Da yamma lis kuma sai ga jerin gwanon tsofaffi da Amarya an tawo da'iya. Harda Sakina aka tawo, suma sun sha ankonsu na Takai. Muma duk mun ci namu ankon na cikin gida, shaddace mai ruwan toka na iyaye, sai wani yaɗi haka na ƙawayen Amarya dai. A haka taro ya watse, duk da ina kaffa _kaffa sai da Yaya Halima ta ci mun mutunci a cikin mutane, daurewa nayi na shanye dan a ranar ma Takai zasu komai. A dangina babu wanda yai mun kara yazo, Uwani ce dai na matsama bata da yadda zata yi shi yasa tazo. A kwana a tashi asarar mai rai. Wasa wasa ƴan biyu shekararsu guda, har suna dabo, Toye kuma yanata zuwa makaranta. Fitinar gidanmu kuma babu abinda ya ragu sai ƙaruwa, dan sau huɗu Gwadabe na biyan kayan da aka sata. Na huɗun ma har ƙarƙashin kujerata akazo aka saka mun, da suka shigo bincike suka zaro. Nayi imanin Laila ce ta aikata mun hakan ba kowa ba, dan tuggu da munafurci iri iri take haɗawa, tsaraicinta da aljanun ƙarya fa babu abinda laila ta dena, a wannan shekara guda ɗin abubbuwa masu dama sun faru. In baku mance ba nace ina yaye ƴan biyu zan bar gidan, to maganar tana ɗamfare a zuchiyata. Ga zawarawa kullum a cikin sallama da' Laila suke, tare da kawo mata ƙwalam da maƙulashe, amman mayyar tana kan bakarta ita sai Gwadabe. Gwadabe ne yaita bani haƙuri nima ganin na kusan yaye in barshi ma baki ɗaya shi yasa ma ban yi tafiyata ba na haƙura na zauna, na cire damuwar kowa da komai a raina. Kamar wasa wata ranar juma'a sai ga Oga Lurwanu shi da karen motar Gwadabe sun riƙo gwadabe ko iya taka ƙafarshi bayayi, suka shinfiɗe mun shi a doguwar kujera. "Gashi nan kin ganshi, mota ya shiga, amman wallahi sai zaro shi akayi ƙafa taƙi takuwa. Muna kyautata zaton sammu akayi mishi. Dama in dai a raba mutum da kafa ko hannune a harkar tuƙi ba kanshi farau ba. Sai ku dage mishi da maganin gargajiya" Hannu na ɗaura aka ina kuka, shima Gwadabe kukan yake yi yana girgiza mun kai halamar in yi shiru. "Ki gode ma Allah ma, da ba haɗarin mota akasa yayi ba ya ragargaje ba. Dan shima anayi kana tsaka da tuƙi sai kaga zaki ko kura, kana ɗauke hannunka magana ta ƙare. Wasu kuma teku suke gani a gabansu duk sai su dibibice" Ni dai sai mamaki da tsoron sha'anin mutan Duniya duk ya kamani. Nera dubu biyar ya ajjiye mun. "Mu kam zamu koma Gwadabe Allah ya ƙara sauƙi" Su kai mana sallama suka tafi. Kifewa a jikinshi nayi ina kuka kamar fitar rai. "Iyabo ki yi ta mun adda'a Allah zai bani lafiya, ta Allah ba dai ta mutum ba. Ni na ɗauka wannan jarabawace ubangijina ya jarabceni dashi. Bazan ɗaura hakkin akan kowa ba Allah yana madakata yana ji da ganin kowa. Ki yi ta mun adda'a. Kafin in amsa shi Yayyen nashi su kayo sallama suka shigo. Baban Nazifi yace. "Gwadabe haka abun ya faru? Ni ina kasuwa ma shigowata kenan mata suke sanar dani wai an shige da kai a hannu baka tafiya, haɗari ne ya afku kome? Koma dai menene Allah ya kyauta gaba. Ke bamu waje ko?" Ya juyo yana mun kallon tsana, ƴan biyu na kwashe dan kar su damu Babansu. Ina daga uwar ɗaki na kira Iyaa nake sanar mata halin da Gwadabe yake ciki. Halin ko in kula ta nuna, tsaki ma tayi ta kashe wayarta, sai Burodami kokodeen da Burodami Debisi na kira na sanar musu, sai ƙawar arziki Uwani. Su Baban Nazifi sun daɗe sosai a falon kafin daga bisani suka tafi, ni da yaran muka fito. "Iyabo inaso zan ɗaura alwala, gashi ina jin fitsari ma. Zaki iya kuwa?" Murmushi nayi ina hawaye lokaci guda nace. "Ai ko ɗaukarkane kacokam zan iya mijina. Nice a haƙƙu in yi maka duk abinda kake da buƙata" Miƙewa nayi na kai yara uwar ɗaki na kulle, falonma na kulle na tawo da ƙaton po mai murfi, cikin dabara na zamo Gwadabe izuwa kan po ɗinnan. Yayi fitsari na mai tsarki, na sake mayar dashi kan kujera. Daga ni har shi sai muka fashe da kuka na faɗa jikinshi. Allah kenan mai yin yadda yake so da bayinshi. Mutum ya fita da ƙafafuwanshi amman yanzu jibeshi a kwance, abunda yafi ƙarfi yanzu ya fi ƙarfinshi. Su Baban Nazifi daya kamata ace su zasu mai duk wannan amman kowa ya tafi ya barmu. Gwadabe kayi haƙuri kuka ba namu bane fa. Akwai Allah shi zai yi mana sakayya. Ka rungumi ƙaddararks sai Allah ya kawo maka ɗauki. Zaka warke bi izinillahi rabbi" "Iyabo ki duba dangina jinina yanda suka nuna halin ko in kula da abunda ya sameni, babu wanda ya tambayeni ko ina jin wata lalura. Yanzu ko Da'u da ba sai ya zauna ya kula dani ba?"... A'a Gwadabe kar ka ɗaura musu nauyin da ba nasu ba. Ni ya kamaci da in jinyata maka. Karma ka sake tada wannan zancan. Ga bawo kayi alwala." Shi da kanshi yayi alwala ni kuma na wanke mishi ƙafafuwanshi. Gwadabe ka daure in kai ka kan gado kaji, sai kayi zamanka acan. Yanzu nan anjima kaɗan Laila zata tashi kwanciya." "Ba zaki iya kaini ba Iyabo, ki je ki kira Da'u ko Nazifi ɗayansu yazo ya kaini, ko du su biyun." Bana so in mishi musu da To" Na amsa mishi, na fita da po ɗin da yayi fitsari na zubar, sai da na mayar ƙarƙashin gado sannan na je kiran Nazifi da Da'u tare da sanar dasu saƙon dake tafe dani. Abun mamaki ko da suka kinkimeshi su biyun dukkansu sai mitar yayi nauyi suka dinga yi, ƙafarshi ɗaya ma basu kama ba sai janta su kai kii. Ni ko ina durƙushe ina hawaye har suka fice ina kuka. A wajen su Yaya Haula suka shigo suka sameni idanuna sun ƴi luɓu_luɓu dasu. "Ohh ni ƴarnan mutum ba a bakin komai yake ba, yau_ yau ɗinnan Gwadabe ya zama musaki sai an kwantar sai an tayar. Sannu Iyabo kinji sannu" Kalmar musaki data faɗa ya dafani sosai. "Kaimu muje mu yi mishi sannu ko. Laila sai ki kwashe kayanki ki ko ɗakin su Halima da Ƙauwama sai ki koma kinga ƴan zuwa dubiya zasuita sunturi kuma dole falo za'a dinga fito dashi" Ni dai gaba nayi suka biyoni. Suka gama gaisheshi suka fita. Ni kuma ina gefenshi ina tofa mishi adda'a a ƙafar tashi, shi kuma yana kallon silin yayi wani irin sanyi" "Iyabo kinga irin riƙon wulaƙancin da Da'u su kai mun? Kinga yatsan ƙafata ya fashe. Daga kwanciya lalura yau _yau harna soma fuskantar wulaƙanci, sai kace ba ciki ɗaya muke ba. Wannan ƙiyayyar dame tayi kama, ki duba fa yanda su Yaya Hambali suka zo suka dubani wallahi babu damuwar komai a fuskokinsu, sai cewa su kai nima karambanine yasa na shiga sana'ar da bani da ilimi a kanta. Wai sana'ar hatsari gareta." Hawayene suka gangaro daga idanunshi izuwa fuskarshi. Rarrashinshi na dinga yi, a ƙoƙarina na ganin na faranta mishi rai, wala Allah ya samu sassauci. Ruwan ɗumi na zuba a bawon na tsoma tsumma na ɗan gargasa mishi yatsan nashi da yake jini. Ya samu yayi sallah, na bashi abinci a baki da kaina,
Chapter 28 · 0% Book details