← Book details Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 237

Sashe 37

Nama Ya Dahu Romo Danye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

a kumbure. Matar da muka zauna waje guda na tambaya. Baiwar Allah a ina zan samu motar Jere Banyo?" Cikin kwaɓaɓɓiyar hausa tace. "Nima can zani, mu je daga can gaba zamu samu mota sai mu tafi" Ajjiyar zuchiya na sauke, na bi bayanta tiryan_tiryan har zuwa wajen akori kurar dana ga ta cika ta batse da mata da mazan funani. Duk masu tallar nononnan da sukaita wucewa ashe duk can zasu je. Iko sai Allah tafiya mabuɗin ilimi kenan. Haka na haye akori kura na biya nera ɗari, a cakuɗe muke da maza, motar an cika mutane har bana iya shaƙar numfashin kirki, baka jin komai sai warin hammata da ƙarnin nono. Ga hanyar babu kyau, haka mu kaita cuccurewa waje guda da mazan da matan. Na sha ɗan karen wuya ainun kafin mu isa Jere Banyo. A mugun galabaice na fito, ina mayar da numfashina. Masu acaɓa ne naji suna ta ihun faɗin. "Jaɓɓi lamba zaki je, kuzo mu je" A galabaice na isa gaban acaɓar nace. Jaɓɓi lamba zani, nawa ne?" "Nera hamsin ne, hau mu je" Hawa nayi ya ja muka nitsa. Ya Allah birni ma rahamane, kwazazzabo muka dinga shiga, acaɓarnan tana sama tana ƙasa damu tamkar zamu kifa. Ƙarafan acaɓar na riƙe dam, na runtse idandunana inata karanto adda'a,. Ga ƙurar jar bushasshiyar rairayi data cika mun idona da hancina dam. Wallahi na ɗauka kafin in sauka daga acaɓarnan zamu rikito mu afka wani ƙaton ramin, babu kwalta ko guntu. Bani na buɗe idona ba har sai da mai acaɓa yace. "Mun iso madakata fa" kana na buɗe idanuna a hankali na ganni a tashar ƴan acaba. A mugun gajiye na sakko daga acaɓar tare da sallamarshi. Jarabawar dana samu duk yaro ko yarinyar da na tambayeta inane gidan Modibbo Yuguda mai nagge. Sai dai su bini dana mujiya basu iya yaren hausa ba, ni kuma ban iya fullanci ba. Ga duhu ya soma doso kai. Wata baiwar Allah ce ta ja hannuna zuwa gidan wani dattijo. Bayan sun yara yaren fullanci mai daɗi da garɗin saurare sai ya fuskanceni cikin gurɓatacciyar hausa yace. "Gidan Modibbo Yuguda mai nagge kike nema ko yarinya? Dan Ɓingel tace iyakar abunda ta gane a bayaninku kenan" E gidanshi na zo Baba. Ni ƴar wajen matarshi Daso ce, yayar su Ɓodɗo ce daga birnin Kano " Baki ya rike tare da girgiza kanshi, ya dubeni da mamaki maɗaukaki yace. "Kika ce ke ƴar Daso ce kuma daga birnin Kano, to Daso dama tana da wata ƴa?" Take naga ya sauya kala daga fara'a zuwa kicin_kicin. Wata dattijuwar fara sol ɗin bafulatana mai yala yalan gashi ya kirawo ta shiga dani cikin asalin gidan. Bayan yace mun zai tura yanzu a tawo da Dadan. Cikin wata bukka aka shiga dani, sai da na sunkuya sosai kafin na iya shiga cikin bukkar, irin gidajen da suke dashi kenan a rugar . Ban taɓa ganin ɗakin gargajiya a zahirance ba sai yau, ɗakin ya burgeni ya ƙayatar dani. Jeren ƙorene kyawawa masu zanen tsuntsaye da masu zanen ƙadangare gasu nan iri iri an mammanna su a jikin bangon bukkar. Daga kusurwa biyu kuma wasu ƙwaryane hawan hawa a jejjere ko wanne anyi mishi murfo da faifal mai kala_kala. Ɗayar kusurwar kuma jeren kwallane masu hoton tsuntsaye da korayen ciyayi, ga wasu tukwanen ƙasa a kikkife a gefe. Abun al'ajabi baya ƙarewa sai gani ga gadon ƙasa da katifar yayi. Ƙasan cikin bukkar kuma buhune aka ɗinka aka shinfiɗa a matsayin ledar tsakar ɗaki. A gefe na zauna ƙuri ga duhu_ duhu a cikin ɗakin. Wannan dattijuwar ce ta shigo hannunta rike da fitilar aci bal_bal, akwai wani ɗan gini da akayi a saman ɗakin kamar anyi gininne musamman domin ajjiye wannan aci bal_bal ɗin. Bayan ta ajiye sai tace dani. "Use ɓilgel ( sannu yarinya)" Sai naga ta fita. Inaso ince zan yi alwala in yi sallah amman bansan me zance ba, dole haka nayi gum. Can bayan duhu ya mamaye sararin samaniya duniya tayi baƙi ƙirin sai na jiyo muryar Dada. Murya mai zaƙi da siranta, muryar dake raunata zuchiyata take kara mun so da tausayin uwata. Cikin bukkar ta shigo da sallama. Tana saye da wata iriyar jemammiyar atampar dana taɓa sai mata a shekarun baya. Sai ɗan wani yalolon tattararren mayafi mai ruwan ƙwai. Ƙafafuwanta kuwa duk ƙura. Idanu ta ƙura mun ƙur, sai naga guraben idanunta tab da ruwan ƙwalla. "Jabu kece a Jaɓɓi lamba a darennan? Kinsan fa kin tambayeni zaki kawo mana ziyara nace miki a'a. To me yasa zaki yi gaban kanki ki zo, ita kuma uwar taki ta barki bacin tasan...." Sai ta ja bakinta ta tsuƙe tare da sauke gwauron numfashi. "Tawo mu tafi to, kawo jakar in riƙe miki" Ta kai hannunta zata ɗauki jakata nayi wuf na ɗauka. A'a Dada zan ɗauka. Kuma kiyi haƙuri dole ce tasa na zo gareki, dole ce tasa Iyaa ta barni nazo, ba a san ranta na tawo ba" Duk fa maganganunnan da yarbanci muke yinshi. Babu dai abinda tace dani sai naga ta sunkuya ta fice. Bayanta nabi muka fita, muna tafe a jere da juna abinda bamu taɓa yi ba kenan. Tiryan_tiryan mu kaiya tafiya, muna wuce samari da ƴan mata. A yadda na lura kab garin gidajensu iri ɗaya ne, gidajen bukka zagaye da jinka, basu da dangar gini ko da na laka ne. Wani gida muka shiga ƙatoton gaske, mata da yaran gidan nono_nono kowa ya ja zugar abokan hirarshi. Ga aci bal_bal kashi kashi, sai fullanci akeyi ana dariya. Mijin Dada yana zaune akan tabarmar keso da rediyo a gabanshi yana ji, ga abinci da kofi a gabanshi. Sallamar Dada yasa wani yaro namiji da ƴar budurwa suka nufota da sauri suna faɗin. "Use Dada" ( Sannu Dada) Mijinta ya juyo ya dube ni, ya dubi Dada dana fuskanci tun shigowarmu jikinta yake rawa. "Je ki gaishe da Babanku gashi can" Ta dubi wannan ƴar berar da tazo ta tareta sai tai mata yare. Shi kuma namijin sai ya amshi jakar hannuna, ita ƴar budurwar kuma tai mun jagora zuwa wajen mijin Dada, gashi ni ban iya Fullanci ba. Haka dai na durƙusa a gabanshi gaisuwar dai ta kurame mu ka yi, sannan muka zo mu ka tarar da Dada tsaye inda muka barta ta nausa a cikin tunani mai nauyi, har sai da ƴar rakiyata ta jijjiga hannayenta. "Dada am" Tace kafin Dada ta dawo cikin nutsuwarta, bayan ta ja fasali sai ta dubeni tace. "Mu je in kai ki ki gaisa da abokan zamana" Binta nayi a baya ta nuna musu ni, nai musu gaisuwar kurame biyu a cikinsu suna ɗan jin Hausa sai muka gaisa da kyau. Daga cikin ƴan mata da yaran gidan ma suna jin Hausa hakan yasa na ɗan ji sanyi. Amman bansan me Dada tace dasu a kaina ba ni dai. Zungul_zungul na bi bayanta har cikin bukkar da nake da tabbacin nata ɗakun kenan. Babu komai a ɗakin sai tarkace kawai, sai gadon ƙasa da katifar yayi taji zanin gado. A bakin gadon tace in zauna. Bayan na zauna Dada sai ta fita. Wannan budurwar kuma tana wajen tulu tana ɗebo mun ruwa a ƙoƙo, bayan ta bani na sha, sai nace. "Inason zan shiga bayan gida, banyi sallar la'asarba ƙila isha tayi ma ko?" "E muma mun yi sallar Isha. Muje in kai ki" Cikin gurɓatacciyar hausar da ba ko wacce nake ganewa ba tayi maganar. Muna fitowa tsakar gidan sai muka tarar da Dada da abokan zamanta a tabarmar da mijinsu yake zaune. Sai faɗa yake zubowa yana ambaton Daso_Daso. Jikina tuni ya bani a kaina ake tattauna maganganu, da jin ƙarfin muryar kuwa ba magana bace ta daɗi. Na sake gasgata hakanne da na ji muryar Dada na rawa, da kuma irin yanda kab yaran gidan su kai ciko_cirko kuma suka ƙura mun idanu kamar maye yaga jariri. MRS BUKHARI NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI
Chapter 37 · 0% Book details