Sashe 95
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu musu Ajidde ta duk’a tana kuka.
Inne ta tsaresa da idanu tana jiran ba’asi.
Mu’azzam ya dubi Inne yace “Da alama baku San wa kuka kawo gidan nan kuka ajiye ba Inne.. Wannan yarinyar b’arauniya ce ba mai magani ba.. Dama ni tun farko ban yarda da ita ba..” Ya dubi Ajidde dake duk’e wajen tana hawaye ya daka mata tsawa da fad’in “Ke.! bud’e bakinki ki fad’i cewa ke b’arauniya ce.!”
Inne ta dakatar dashi da fad’in “Haba Modibbo.. Wane irin abu ne zaka saka ‘yar talikan nan gaba kana tuhumarta da sata.. Awho dan Ta maka ihun b’arawo jiya shine yau kaima bari ka kirata b’arauniya.. Ko dan kaga tufafin matarka jikinta.?”
Mu’azzam dake faman aikawa Ajidde mugun kallo daga nan yana take duk’a tana hawaye yace “Inne yarinyar nan b’arauniya ce.. Itace yarinyar da ta tasamma min sata kwanakin baya Ran da nazo gidan nan..” Ya kaikaito ya dubi Ajidde yace “Ke.. Ki fad’a mata cewa ke b’arauniya ce.” Ya daka ma Ajidde tsawa da fad’in haka.
Kafin Ajidde takai ga basa amsa suka sinkayo muryar Musaddiq ya doso wajen yana fad’in “Ita ba b’arauniya bace..!”
Gaba d’aya suka juyo suna duban Musaddiq dake nufosu cikin tsananin dakewa.
Mu’azzam ya d’an tsaresa da idanu kafin yace “You don’t know anything Musaddiq.. Just stay out of this..”
Musaddiq dake sakin huci dab kusan Mu’azzam d’in ya tsaya suna fuskantar juna lokaci guda yake furta “I told you she’s not a thief.!”
Yanda yake maganar da zafin rai yasa Mu’azzam tsaresa da idanu yana dubansa, ya d’an girgiza kai kad’an kafin yace “Are you alright..?”
“Garau nake..! Na fad’a maka ita ba b’arauniya bace.. Or did she steal from you..?!” Yai maganar yana duban cikin idanun Mu’azzam.
Mu’azzam ya girgiza kai yace “She didn’t amma tayi kusa.. And for that zata bar gidan nan dan bamu San wace irin criminal bace ita.. Bamu buk’atar maganinta..”
Musaddiq ya katsesa da fad’in “Babu yana zataje.. Sabida ita mutumiyar kirki ce.. Kuma Aunty Nuratu tana buk’atar maganinta..!”
Aunty Shemau ta zaro idanu waje tana kame k’irji, mai Musaddiq yake nufi da cewa Nuratu tana buk’atar maganin yarinyar.. Kodai Musaddiq yasan shirinsu ne itada mahaifiyarsa..? Muryar Mu’azzam ne ya kaste mata tunanin nata.
Ganin yanda yake amsa masa magana yasa ya kuma karkatowa yana duban Musaddiq d’in “Are you high..?” Mu’azzam ya tambaya yana tsare Musaddiq d’in da idanu.
Tambayar da Mu’azzam yai masa na k’arshe ya mugun tunzirasa, lokaci guda ya soma fad’in “Kana tunanin kai kad’ai ne mutumin Kirki a nan.. Well let me remind you.. You are not a saint Mu’azzam Gamji.. And you need to learn that you can’t control the lives of the people around you.. And yes like it or not Babu yanda Ajidde zataje.. Tana nan a gidan nan..!”
Wann karon cikin tsananin mamaki Mu’azzam ya girgiza kai kad’an yana duban Musaddiq d’in “Have you lost your mind.?” Ya furta a hankali yana duban Musaddiq d’in.
Inne tai saurin rik’o Musaddiq tana k’ok’arin janyosa baya yayinda Mama Hindu ta janye Ajidde suka fice daga wajen. Shemau kuwa gyara tsayuwarta tai tana kallon show d’in dake wakana.
Inne tana janye Musaddiq take fad’in “Ya isa haka abi komai a sannu..”
Musaddiq cikin d’aga murya yace “No Inne.. who does he think he is da dole kowa Sai ya bi abinda yake so.. Ajidde bazata bar gidan nan ba.. Kuma zata dawo zama cikin gidan nan na har abada..!”
Yaci gaba da sakin huci yana nufo Mu’azzam d’in, saida ya tsaya kaman k’irjinsa zai bangaji na Mu’azzam kafin yaci gaba da fad’in “And do you know Why is that Mu’azzam Gamji..? Because I love her..! Yes I love her.. And I’m going to marry her.. Kai baka isa ka koreta ba Mu’azzam Gamji..!”
K’iris ya rage Shemau bata kifa k’asa ba.. Daga Inne har Mu’azzam Cak suka tsaya suna duban Musaddiq dake ci gaba da sakin huci kaman zai kaiwa Mu’azzam d’in naushi.
Mu’azzam yai k’ok’arin calming kansa dan ya lura kaman Musaddiq d’in a sama yake.. K’ila yasha wani kayan mayen nasa.
Inne zatai magana Mu’azzam ya dakatar da ita yana fad’in “Kar ki damu Inne I’ll take care of this..”
Lokaci guda ya mik’a hannunsa yana k’ok’arin kamo Musaddiq d’in yake fad’in “Brother calm down.”
Fuzga Musaddiq yai yana ci gaba da sakin huci yake nuna Mu’azzam d’un da yatsa “Don’t you dare.. Don’t you dare come near me.!” Yana ida fad’in haka yasa kai zai shige cikin huci.
Inne tai saurin taresa cikin tsananin b’acin rai take fad’in “Baka da hankali ne kake d’agawa D’anuwanka murya haka.. Kodai ka koma shan kayan mayen Naka ne..?!”
Bai daina sakin huci ba yake duban Inne “Go ahead and take his side.. Dama abinda kuka iya kenan.. Baya laifi a idonku.. Bani ya kamata ki tambaya ko na koma shan kayan maye ba.. Shi ya kamata ki tambaya tinda har zai tare k’aramar yarinyar nan yace ta masa sata bayan bata sata masa komai ba.. Idan bai gode wa d’awainiyar da takeda mahaifiyarsa wanda bazai iya biyanta kwatankwacin abinda tai ba bazai k’ala mata sharrin sata har yace zai koreta a gidan nan ba.. Kuma kunji abinda na fad’a I love that girl.. Ina sonta.. Ina sonta sosai kuma zan aureta.. Idan zaku koreta a gidan nan sabida shalele Mu’azzam yace a koreta Toh definitely zaku had’a dani dan nima zan tafi kuma bazaku sake ganina ba..!” Daga haka ya fice fuu yana sakin huci.
Inne tai mutuwar tsaye tana duban Musaddiq har ya fice. Aunty Shemau dake lab’e bayan parlorn itama kallo tabi Musaddiq d’in dashi tana jinjina lamarin cikin zuciyarta har yazo ya shigeta ya fice a parlorn.
Mu’azzam ya k’araso ya rik’e Inne ya zaunarta a hankali saman kujera.
Duban Mu’azzam tai tace “Kaga yanda yake d’aga mana murya..? Anya yana cikin hankalinsa..?”
Mu’azzam ya fuzar da fuci kad’an yace “Zan same shi Inne.. Zan mishi magana.. Zanji meke damunsa.. Tabbas akwai abinda ke damun D’anuwana.. Koda ya sha abubuwansa ba haka yake ba.. Something is off with him..”
Inne dai shiru tai tana jinjina abubuwan dake faruwa da ahalinsu. Safeenah tayi harbi da bindiga. Auren Mu’azzam da Safeenar ya k’are yanzu ga Musaddiq ya bijiro da wani irin hali da basu saba ganinsa ciki ba dukda ya kasance mai gagara. A hankali Ta maida kanta cikin kujera tana ambaton Allah tareda rok’onsa ya tsare mata ahalinta.
Basu kuma ganin Musaddiq a gidan ba har dare. Sannan a daren Inne da tsiraru cikin dangi sukaima Sadiya rakiya zuwa b’angaren da tin kwanaki Innen Tasa aka gyarawa Mu’azzam da Safeenah.
**
Bugu biyu Mommy ta d’aga wayan Shemau, ko gaisawa basuyi ba tace “Ina sauraronki Shemau, fad’a mun meke faruwa.. Kun raka Karuwar Mu’azzam d’akinta ko k’ak’a..?”
Aunty Shemau ta nusa tace “Idan nice ke Aunty Hajara ba wann zan tambaya ba..”
Shaye da mamaki Mommy tace “Yo mai zan tambaya..? Ko Nuratu ce ta mutu kike shirin bani albishir..?”
Aunty Shemau ta nusa tace “Wann ai ba albishir zan miki ba.. Abin tashin hankali zan sanar dake.”
Wann karon mik’ewa tsaye Mommy tai tana girgiza kai take fad’in “A’a Shemau.. Na gaji da jin labarai marassa dad’i.. Kar dai kice mun nakasashiyar matar Marwan warkewa tayi..?!”
Aunty Shemau tace “Duk ba’a kansu bane..”
Cikeda k’osawa Mommy tace “Shemau ki daina tsinkar min da gaba ki sanar dani meke faruwa.. Marwan ne ya sake yo mun kishiya kokuwa..?”
Shemau tace “Duk ba’a kansu bane. Kan d’anki Musaddiq ne..”
Mommy Ta dafe k’irji tace “Na shiga uku ni Hajara mai ya sami Musaddiq..”
Aunty Shemau Ta murmusa tace “Babu abinda ya sami Musaddiq amma kiyi shirin biki dan Musaddiq ya sami mata a nan..”
Mommy ta girgiza kai tace “Ban fahimceki ba Shemau.”
Aunty Shemau tace fillanci kike so na miki sai kifi fahimta da kyau. Toh d’anki Musaddiq ya fad’a soyayya da mahaukaciyar yarinyar dake kawowa Nuratu magani..”
Mommy ta dafe k’irji tace “Na shiga uku ni Hajara.. Kiyi istigifari Shemau domin kuwa Ina raye Musaddiq bazai auri dangin bokaye da ‘yan bori ba.. Toh banda bak’in jaraba mai ya gani tattare da ita ya tsallake duk matan dake sonsa a nan Abuja.”
Shemau ta tab’e baki tace “Yo ina na sani.. Shawarin da zan baki Aunty Hajara tun wuri ki d’auke Musaddiq daga garin nan ya daina ganin yarinyar ta haka ne kawai za’a iya rabasu.”
Mommy na safa da marwa cikin d’aki take fad’in “Ta yaya zanyi haka Shemau bayan Kinsan halin wannan jarababbiyar tsohuwa..”
Aunty Shemau tace “Tun wuri ki nemowa kanki hanya, kiyi duk yanda zakiyi ki tabbata kin rabasu.. Dan ni duk bama wann ba muddin Musaddiq zai soyayya da yarinyar nan asirinmu tonuwa zai.. Ni babban tashin hankali na kenan..”
Mommy tace “Yo da na had’a iri da zuri’ar bokaye da bori ai gwara asirinmu ya tonu..”
Shemau tace “Lallai baki San abinda kike fad’i ba Hajara.. Wllhi wllhi bazan bari asirina ya tonu Mu’azzam ya jefani kurkuku ba.. Koda wasa kar d’anki ya mun sanadi.. Ni ba damuwata bace idan ma Jikanyar ifiritu zai aura.. Ni damuwata shine kar asirina ya tonu ehe.. Tun wuri kisan yanda zakiyi ki d’auke d’anki daga garin nan Ni zanji da yarinyar..!” Daga haka Shemau ta katse wayar a fusace.
Mommy tana kiran sunan Shemau ko tsayawa sauraronta batai ba ta datse kiran.
Hannu biyu Mommy Ta d’aura aka tana fad’in “Na shiga uku ni Hajara Musaddiq zai karni a tsaye.!” Cikin sauri ta shiga neman layin Musaddiq saidai bata shiga.
**
A b’angaren Sadiya kaw tinda akai mata rakiya zuwa b’angaren bata sanya angon nata a idanunta ba, har dare ya soma ja, Ta mik’e ta gabatar da sallar isha da batayi ba.
Tana nan zaune saman darduma taji alamun shigowarsa dan taji kaman tab’a k’ofar parlorn. Gabanta ya fad’i, bugun zuciyarta na k’aruwa.
Bata tashi saman darduman ba saima tsintar kanta da tai tana kuma gyara zaman tahiyar nata kaman dai bata sallame sallar ba.
Tanajin alamun bud’e d’aya k’ofar d’akin da yayi dan dama d’akuna biyu ne sai parlor da kitchen a section d’in.
Ya b’ata lokaci a d’aya d’akin tana nan zaune tamkar wacce aka dasata.
Inne ta tsaresa da idanu tana jiran ba’asi.
Mu’azzam ya dubi Inne yace “Da alama baku San wa kuka kawo gidan nan kuka ajiye ba Inne.. Wannan yarinyar b’arauniya ce ba mai magani ba.. Dama ni tun farko ban yarda da ita ba..” Ya dubi Ajidde dake duk’e wajen tana hawaye ya daka mata tsawa da fad’in “Ke.! bud’e bakinki ki fad’i cewa ke b’arauniya ce.!”
Inne ta dakatar dashi da fad’in “Haba Modibbo.. Wane irin abu ne zaka saka ‘yar talikan nan gaba kana tuhumarta da sata.. Awho dan Ta maka ihun b’arawo jiya shine yau kaima bari ka kirata b’arauniya.. Ko dan kaga tufafin matarka jikinta.?”
Mu’azzam dake faman aikawa Ajidde mugun kallo daga nan yana take duk’a tana hawaye yace “Inne yarinyar nan b’arauniya ce.. Itace yarinyar da ta tasamma min sata kwanakin baya Ran da nazo gidan nan..” Ya kaikaito ya dubi Ajidde yace “Ke.. Ki fad’a mata cewa ke b’arauniya ce.” Ya daka ma Ajidde tsawa da fad’in haka.
Kafin Ajidde takai ga basa amsa suka sinkayo muryar Musaddiq ya doso wajen yana fad’in “Ita ba b’arauniya bace..!”
Gaba d’aya suka juyo suna duban Musaddiq dake nufosu cikin tsananin dakewa.
Mu’azzam ya d’an tsaresa da idanu kafin yace “You don’t know anything Musaddiq.. Just stay out of this..”
Musaddiq dake sakin huci dab kusan Mu’azzam d’in ya tsaya suna fuskantar juna lokaci guda yake furta “I told you she’s not a thief.!”
Yanda yake maganar da zafin rai yasa Mu’azzam tsaresa da idanu yana dubansa, ya d’an girgiza kai kad’an kafin yace “Are you alright..?”
“Garau nake..! Na fad’a maka ita ba b’arauniya bace.. Or did she steal from you..?!” Yai maganar yana duban cikin idanun Mu’azzam.
Mu’azzam ya girgiza kai yace “She didn’t amma tayi kusa.. And for that zata bar gidan nan dan bamu San wace irin criminal bace ita.. Bamu buk’atar maganinta..”
Musaddiq ya katsesa da fad’in “Babu yana zataje.. Sabida ita mutumiyar kirki ce.. Kuma Aunty Nuratu tana buk’atar maganinta..!”
Aunty Shemau ta zaro idanu waje tana kame k’irji, mai Musaddiq yake nufi da cewa Nuratu tana buk’atar maganin yarinyar.. Kodai Musaddiq yasan shirinsu ne itada mahaifiyarsa..? Muryar Mu’azzam ne ya kaste mata tunanin nata.
Ganin yanda yake amsa masa magana yasa ya kuma karkatowa yana duban Musaddiq d’in “Are you high..?” Mu’azzam ya tambaya yana tsare Musaddiq d’in da idanu.
Tambayar da Mu’azzam yai masa na k’arshe ya mugun tunzirasa, lokaci guda ya soma fad’in “Kana tunanin kai kad’ai ne mutumin Kirki a nan.. Well let me remind you.. You are not a saint Mu’azzam Gamji.. And you need to learn that you can’t control the lives of the people around you.. And yes like it or not Babu yanda Ajidde zataje.. Tana nan a gidan nan..!”
Wann karon cikin tsananin mamaki Mu’azzam ya girgiza kai kad’an yana duban Musaddiq d’in “Have you lost your mind.?” Ya furta a hankali yana duban Musaddiq d’in.
Inne tai saurin rik’o Musaddiq tana k’ok’arin janyosa baya yayinda Mama Hindu ta janye Ajidde suka fice daga wajen. Shemau kuwa gyara tsayuwarta tai tana kallon show d’in dake wakana.
Inne tana janye Musaddiq take fad’in “Ya isa haka abi komai a sannu..”
Musaddiq cikin d’aga murya yace “No Inne.. who does he think he is da dole kowa Sai ya bi abinda yake so.. Ajidde bazata bar gidan nan ba.. Kuma zata dawo zama cikin gidan nan na har abada..!”
Yaci gaba da sakin huci yana nufo Mu’azzam d’in, saida ya tsaya kaman k’irjinsa zai bangaji na Mu’azzam kafin yaci gaba da fad’in “And do you know Why is that Mu’azzam Gamji..? Because I love her..! Yes I love her.. And I’m going to marry her.. Kai baka isa ka koreta ba Mu’azzam Gamji..!”
K’iris ya rage Shemau bata kifa k’asa ba.. Daga Inne har Mu’azzam Cak suka tsaya suna duban Musaddiq dake ci gaba da sakin huci kaman zai kaiwa Mu’azzam d’in naushi.
Mu’azzam yai k’ok’arin calming kansa dan ya lura kaman Musaddiq d’in a sama yake.. K’ila yasha wani kayan mayen nasa.
Inne zatai magana Mu’azzam ya dakatar da ita yana fad’in “Kar ki damu Inne I’ll take care of this..”
Lokaci guda ya mik’a hannunsa yana k’ok’arin kamo Musaddiq d’in yake fad’in “Brother calm down.”
Fuzga Musaddiq yai yana ci gaba da sakin huci yake nuna Mu’azzam d’un da yatsa “Don’t you dare.. Don’t you dare come near me.!” Yana ida fad’in haka yasa kai zai shige cikin huci.
Inne tai saurin taresa cikin tsananin b’acin rai take fad’in “Baka da hankali ne kake d’agawa D’anuwanka murya haka.. Kodai ka koma shan kayan mayen Naka ne..?!”
Bai daina sakin huci ba yake duban Inne “Go ahead and take his side.. Dama abinda kuka iya kenan.. Baya laifi a idonku.. Bani ya kamata ki tambaya ko na koma shan kayan maye ba.. Shi ya kamata ki tambaya tinda har zai tare k’aramar yarinyar nan yace ta masa sata bayan bata sata masa komai ba.. Idan bai gode wa d’awainiyar da takeda mahaifiyarsa wanda bazai iya biyanta kwatankwacin abinda tai ba bazai k’ala mata sharrin sata har yace zai koreta a gidan nan ba.. Kuma kunji abinda na fad’a I love that girl.. Ina sonta.. Ina sonta sosai kuma zan aureta.. Idan zaku koreta a gidan nan sabida shalele Mu’azzam yace a koreta Toh definitely zaku had’a dani dan nima zan tafi kuma bazaku sake ganina ba..!” Daga haka ya fice fuu yana sakin huci.
Inne tai mutuwar tsaye tana duban Musaddiq har ya fice. Aunty Shemau dake lab’e bayan parlorn itama kallo tabi Musaddiq d’in dashi tana jinjina lamarin cikin zuciyarta har yazo ya shigeta ya fice a parlorn.
Mu’azzam ya k’araso ya rik’e Inne ya zaunarta a hankali saman kujera.
Duban Mu’azzam tai tace “Kaga yanda yake d’aga mana murya..? Anya yana cikin hankalinsa..?”
Mu’azzam ya fuzar da fuci kad’an yace “Zan same shi Inne.. Zan mishi magana.. Zanji meke damunsa.. Tabbas akwai abinda ke damun D’anuwana.. Koda ya sha abubuwansa ba haka yake ba.. Something is off with him..”
Inne dai shiru tai tana jinjina abubuwan dake faruwa da ahalinsu. Safeenah tayi harbi da bindiga. Auren Mu’azzam da Safeenar ya k’are yanzu ga Musaddiq ya bijiro da wani irin hali da basu saba ganinsa ciki ba dukda ya kasance mai gagara. A hankali Ta maida kanta cikin kujera tana ambaton Allah tareda rok’onsa ya tsare mata ahalinta.
Basu kuma ganin Musaddiq a gidan ba har dare. Sannan a daren Inne da tsiraru cikin dangi sukaima Sadiya rakiya zuwa b’angaren da tin kwanaki Innen Tasa aka gyarawa Mu’azzam da Safeenah.
**
Bugu biyu Mommy ta d’aga wayan Shemau, ko gaisawa basuyi ba tace “Ina sauraronki Shemau, fad’a mun meke faruwa.. Kun raka Karuwar Mu’azzam d’akinta ko k’ak’a..?”
Aunty Shemau ta nusa tace “Idan nice ke Aunty Hajara ba wann zan tambaya ba..”
Shaye da mamaki Mommy tace “Yo mai zan tambaya..? Ko Nuratu ce ta mutu kike shirin bani albishir..?”
Aunty Shemau ta nusa tace “Wann ai ba albishir zan miki ba.. Abin tashin hankali zan sanar dake.”
Wann karon mik’ewa tsaye Mommy tai tana girgiza kai take fad’in “A’a Shemau.. Na gaji da jin labarai marassa dad’i.. Kar dai kice mun nakasashiyar matar Marwan warkewa tayi..?!”
Aunty Shemau tace “Duk ba’a kansu bane..”
Cikeda k’osawa Mommy tace “Shemau ki daina tsinkar min da gaba ki sanar dani meke faruwa.. Marwan ne ya sake yo mun kishiya kokuwa..?”
Shemau tace “Duk ba’a kansu bane. Kan d’anki Musaddiq ne..”
Mommy Ta dafe k’irji tace “Na shiga uku ni Hajara mai ya sami Musaddiq..”
Aunty Shemau Ta murmusa tace “Babu abinda ya sami Musaddiq amma kiyi shirin biki dan Musaddiq ya sami mata a nan..”
Mommy ta girgiza kai tace “Ban fahimceki ba Shemau.”
Aunty Shemau tace fillanci kike so na miki sai kifi fahimta da kyau. Toh d’anki Musaddiq ya fad’a soyayya da mahaukaciyar yarinyar dake kawowa Nuratu magani..”
Mommy ta dafe k’irji tace “Na shiga uku ni Hajara.. Kiyi istigifari Shemau domin kuwa Ina raye Musaddiq bazai auri dangin bokaye da ‘yan bori ba.. Toh banda bak’in jaraba mai ya gani tattare da ita ya tsallake duk matan dake sonsa a nan Abuja.”
Shemau ta tab’e baki tace “Yo ina na sani.. Shawarin da zan baki Aunty Hajara tun wuri ki d’auke Musaddiq daga garin nan ya daina ganin yarinyar ta haka ne kawai za’a iya rabasu.”
Mommy na safa da marwa cikin d’aki take fad’in “Ta yaya zanyi haka Shemau bayan Kinsan halin wannan jarababbiyar tsohuwa..”
Aunty Shemau tace “Tun wuri ki nemowa kanki hanya, kiyi duk yanda zakiyi ki tabbata kin rabasu.. Dan ni duk bama wann ba muddin Musaddiq zai soyayya da yarinyar nan asirinmu tonuwa zai.. Ni babban tashin hankali na kenan..”
Mommy tace “Yo da na had’a iri da zuri’ar bokaye da bori ai gwara asirinmu ya tonu..”
Shemau tace “Lallai baki San abinda kike fad’i ba Hajara.. Wllhi wllhi bazan bari asirina ya tonu Mu’azzam ya jefani kurkuku ba.. Koda wasa kar d’anki ya mun sanadi.. Ni ba damuwata bace idan ma Jikanyar ifiritu zai aura.. Ni damuwata shine kar asirina ya tonu ehe.. Tun wuri kisan yanda zakiyi ki d’auke d’anki daga garin nan Ni zanji da yarinyar..!” Daga haka Shemau ta katse wayar a fusace.
Mommy tana kiran sunan Shemau ko tsayawa sauraronta batai ba ta datse kiran.
Hannu biyu Mommy Ta d’aura aka tana fad’in “Na shiga uku ni Hajara Musaddiq zai karni a tsaye.!” Cikin sauri ta shiga neman layin Musaddiq saidai bata shiga.
**
A b’angaren Sadiya kaw tinda akai mata rakiya zuwa b’angaren bata sanya angon nata a idanunta ba, har dare ya soma ja, Ta mik’e ta gabatar da sallar isha da batayi ba.
Tana nan zaune saman darduma taji alamun shigowarsa dan taji kaman tab’a k’ofar parlorn. Gabanta ya fad’i, bugun zuciyarta na k’aruwa.
Bata tashi saman darduman ba saima tsintar kanta da tai tana kuma gyara zaman tahiyar nata kaman dai bata sallame sallar ba.
Tanajin alamun bud’e d’aya k’ofar d’akin da yayi dan dama d’akuna biyu ne sai parlor da kitchen a section d’in.
Ya b’ata lokaci a d’aya d’akin tana nan zaune tamkar wacce aka dasata.